Showing 15001 words to 18000 words out of 112373 words
Chapter 6 - AGE MATE'S Complete Document book by Momy Fareesa .txt
 yaja motar Atsiyace suka bar layin.....saidai sunyi mamakin gadararsa d'aya nuna rashin tsoro" yana dai kallonsu kawai, ya wani tamke fuska shi damuwarsa jam'in daya rasa"yayi Imani basu Isa suyi masa Abinda Allah be masaba"ba suyi cikakken mintina biyar ba da shiga cikin nafef d'in suka watso masa wata powder gefen fuska"yafara tari da dare kansa ,daga nan be koma sanin inda kansa yake ba......��
🫣ğŸ¤ğŸ¤”🤫
Anan k'arshen Free page yazo domin samun naki halal d'in hanzarta biya sbd adama dake Acikin wannan tsabtataccen labari me cike da zazzafar soyayya da ban tausayi had'e da saka zuciya nishad'i,har yanzun bamu shiga cikin gundarin labarin ba Akwai kura,kun dai san Alk'alamina 🤗🤗 siyen nagari maida kud'i gida ne sai mun had'e paid grps guys
wannan book d'in na kudine !
Regular grp 500
Vip grp 1000
Special grp 2k wato 3pages in a day 
zaku biya kud'in ku ta wannan acc number👉2230373842 NABILA ALIYU UBA BANK
Kituro shaidar biyanki what's app number d'ina  08100084251 500 kawai ake turo Kati idan bakida acc amma sauran payment d'in ta acc ne
  banason transfer d'in Kati ko vtu photo d'in katin MTN zaki d'auka saiki turo  dan Allah banda kira� 
Y'an nijar kutuntub'i wannan n👉 +227 88 01 90 50
Regular 300f
Vip 700f
Special grp 1500f
dan girman Allah da darajan iyayenki karki mun mgn idan baki shirya biyaba
#Mommyn fareesa 
#Dr Nura Darma
#Ahyaan 
#mr Mahuta
#AA mashi
#mu'az
#Khairiyyah
#Ammah
#Ummah
#ikkhee
7/21/24, 11:01 - Buhainat: � *AGE MATE'S* ��♀�
*11&12*
*Littafin kud'i ne!*
.......sunyi tafiya me d'an nisa ta kusan mintina 30 "kafn daga isanisu parking Adaidai wani had'ad'd'en get house"mutum biyu suka d'auki Dr darma dabai san inda kansa yake ba da k'yar sbd nauyinsa suka wuce dashi ciki"Mr mahuta dake zaune A haraban gidan kan wasu kujeru suna mgn da wani Amininsa ya bisu da kallo yana sakin murmushi "bayan wucewar su ciki honorable rabiu yace"Abokinah me hakan ke nufi?"Atak'aice ya bashi labarin had'uwarsa da Ahyaan da irin bak'ak'en magan ganunda Dr darma ya cab'a masa, da yadda yasaka Aka masa bincike kansa ya gano waye shi "kafin yaci gaba da cewa" tunda naga yarinyar har yanzun zuciyata tak'i nutsuwa"Ina son kasancewa da ita,kunnu wana nason  jin sautin zazzak'ar muryanta da tsiwarta"bana jin zan iya k'yale yarinyar"rabona da nayi  sex tun kafin na ganta"gaba d'aya bana jin sha'awar ko wace mace sai ita"inaso kota Aure ko bata Aure ba na mallaketa......yo Ai wannan Aganina ba wani Abin damuwa bane"kasan ma koita d'in  y'ar hannu ce?"ah ah gaskiya " ga yadda nayi bincike Akanta ba y'ar bariki bace ba"uhmm Abokinah baka ji"kayi dai k'ok'arin yi mata b'arin kud'i ta Amince ta Aureka"idan ta k'iya kuma sannu sannu kuna soyayya har ta d'an fara sakin jiki dakai "sai ka jata zuwa shan ice cream "kawai saika saka Asanya mata desire table Aciki  daga nan ka biya buk'atar ka ba shikenan ba?? gaskiya ka kawo shawara me kyau Abokinah......wata iriyar dariya suka kece da ita.....Ahankali Dr darma ya bud'e sexy eyes d'insa yana dafe da kansa dake sara masa"Addu'o in neman tsari ya fara jerowa Abayyane cikin taushin muryansa me cike da nutsuwa da haiba"yana k'arema kansa da inga yake kwance kallo"kai tsaye idanunsa kan Agogon dake d'aure A damtsan hannunsa suka sauka"k'arfe 10:11 pm"k'irjinsa ya buga! sbd tunawa da beyi sallar isha'i ba da yayi"ya san kuma daddy zai nemesa idan yaga k'arfe goma na dare  ta wuce, sbd be wuce 9:pm a shagonsa yake dawowa gida.....tashi yayi zaune yana kallon had'ad'd'en parlourn da yake ciki na Alfarma k'anyar da haske kamar da rana"yamutsa fuska yayi yana y'an dube dube yaga shika d'ai ne ciki"yaja tsaki me k'arfi yana hard'e dogayen kyawawan k'afafuwansa waje guda yana wani girgiza su"babu wata damuwa ko Alamar razana atattare dashi.... motsin da yaji yasakashi jin k'irjinsa ya buga! saidai tsabar jin kai irin nasa bema kalli gefen daya kejin Alamar tafiyarba....banyi mamakin izzar kaba Ayanzun "sbd Abinciken da nayi game dakai na samu labarin halayyarka fiye da Abinda na gani Ayanzun"saidai matsalar izzar taka da d'agawar ta banzace tunda kai talaka ne! cewar Mr mahuta dake k'ok'arin zama kan kujera yana sanye da manyan kaya"sai lokacin darma ya d'ago kansa yamasa kallon second 5 yana sakin wani irin shed'anin murmushi "sai kuma ya had'e rai yana janye idanunsa ya mayar kan Agogon dake d'aure Ahannunsa.... Akallah Mr mahuta zaiyi 38yrs da haihuwa"yasan shida shi ba sa'annin juna bane"saidai zai nuna masa iyakarsa"duk yadda Mr mahuta yayi zaton yaron ya wuce tunaninsa sbd yak'i mgn yayi shiru kawai"ganin zasu iya kwana Anan bayan ba haka ya tsaraba ya sakashi cewa"naga Ahyaan Ina kuma *sonta da Aure*! na saka Akamun kai nan sbd Akwai Aikin da nake so na baka game da hakan"da farko na d'auka kaida ita ko masoyane "I mean Ina nufin bata sonka kaine ke haukan ka ,saida nayi bincike nagane ba haka bane"domin da tana sonka kana sonta da tuni kunyi Aure sbd zumuncin iyayenku "inaso ka janyo mun hankalinta, ka nuna mata mahinmancin Amincewa da soyayya ta har zuwa ta Aure ni"ni kuma namaka Alk'awarin ban kwana da talauci"nasan dai duk wanda ya kwana garin nan yasan wanene *Alh Abubakar mahuta* ? babban d'an siyasa,kuma tsohon deputy governor"kuma babban hamshak'in Attajiri"nasan k'ilan kai baka sanniba "sunana *Ibarahm Abubakar mahuta* .nine babban d'ansa! yana fad'in hakan ya danna Landline phone"ba b'ata lokaci yaci gaba da cewa" mukhtar kamun kud'in nan dake cikin jaka"daga haka ya Ajiye land line d'in"har lokacin Dr darma na nan zaune yana saurarensa bece uffan ba"kimanin shud'ewar mintina 5 saiga yaro guda da Acikinsu suka kamosa ya shigo da wata leda viva bak'a Ahannunsa "bayan ya Ajiye ya juya ya fita"kallonsa yayi yace"ga wannan million biyu ne ciki" somun tab'i ne Dr kafin nan gaba saima yadda kake so za'a baka"na sami labarin har yanzun baka fara Aiki ba, shima zaka iya kamun takardun naka mu gani za'a kai inda Atake za'a daukeka Aiki "yanzun kasamun contact naka! ya fad'a yana sakin wani shegen murmushin rainin wayo"sbd Aganinsa dole Dr darma ya Ajiye zafin kai tunda yaga kud'i..... mik'ewa tsaye yayi Anutse yana koma sakin wani k'aramin murmushi "wanda yadaki zuciyar Mr mahuta dake zaune yana kallonsa da son jin ta bakinsa"gab dashi ya iso murmushin dake saman fuskarsa na dishewa"saida ya kallesa sama da k'asa kafin ya girgiza kansa Ido  cikin Ido cikin  iya tsara laffuzzan mgn yace" *wanda Ake d'auka ba komai bane sauda yawa wata ran shine ke zama komai" harma ya Amfani wanda ke ganin yafi k'arfin ya nemi ya masa wani Amfani* naji inada gadarar, kamar yadda kace"saidai Ina godiya ga Allah da yayini A talaka bamai dukiyar da zaiyi fahari ko tunk'aho itaba"iya Abinda na. sani da talaka dame kud'i duk Allah ne  yayisu"fatan dacewa kamai muke nema"zancan Ahyaan dakake mgn ! Kaifa namiji ne? to meye zai Hana kayi Amfani da kanka wajen shayo kanta harta Amince maka?"Ina so kasani kud'i! basu bane komai" ka rik'e kud'inka bana buk'ata "iya Abinda na sani duk me jin kansa da nuna shi wanine tofa Agaban bainar jama'a yake gadararsa bawai ya tsaya yayita Abayan fage ba"idan har ka gama mgn dani Ina buk'atar na k'ara gaba"ban damu da matsayinka ko dukiyarka ba ,ko kuma zaka saka acutar dani"Abinda kawai na sani.....kai! kasan ko shi waye  ne kake k'ok'arin gaya masa mgn?"cewar wani k'ato d'aya shigo ya tsintsi maganar Dr darma"saidai mahuta beso ya dakatar da shiba, yaso ya barsa yakai Aya "ya lura zafin kan yaron da izzarsa me girma ne"Amma daidai yake dashi....Dr darma kuwa murmushin takaici yayi yana nufar k'aton abazata yamasa wata wawar  cakuma yana fad'in waye shi bayan *Ibrahim Abubakar mahuta*? Haihuwar sa Akayi kamar kowa ko kuwa daga sama yafad'o ne??"ya fad'a cikin zafin zuciya yana ingizashi da masifar k'arfi,ya daki bango"Atake wasu katti su ukku suka fito da manyan makamai Ahannunsu zasu nufesa"hannu guda Mr mahuta ya d'aga musu Alamar su bari"kafin ya mik'e tsaye sbd Al'amarin yaron ya fara bashi tsoro" yana ganin ba ta haka yaka mata yabiyo masa ba"Amma saiya basar ya kalli mutum biyu yana fad'in ku maidashi gida"daga haka ya d'auki ledar kud'in yabar parlourn.....kafin Dr darma ya juyo yaji wani k'yalle saman fuskarsa sun rufe masa Ido dashi "beyi mgn ba yana dai tsaye suka jashi suka fita suka shige mota...... k'arfe sha d'aya saura suka yi parking bakin titi basu shigo cikin layin suba"bece komai ba da suka janye k'yallen,kamar yadda suma basu maca komai ba, sai fitowa kawai da yayi daga cikin nafef d'in yana jan tsaki "ko Ajikinsa da Abinda Mr mahuta yayi na sakawa a d'akkosa"saidai zai nuna masa cewa raina kama kaga gayya"da wannan tunanin ya zaro wayarsa yaga 20 miss call"bema tsaya dubawa yaga kona waye,  time kawai ya duba"jikinsa na bashi y'an gidan sune ke kiran sa"yaja tsaki yana nufar layin nasu da yayi tsit duk gidajen Anguwar suna a rufe ,sai d'aid'ai k'un motoci dake wucewa da mashina"tun daga nesa ya hango daddy da Abba da khaleel tsaye bakin get d'in shiga  *gida biyu* suna mgn..... d'an huci ya furzan daga bakinsa"yana fad'in daidai nake dakai wlh mahuta tunda ka had'a wasanka dani"haka kawai sbd wani banza za'a tayarwa da iyayena hankali"ya fad'a Afili cikin yana yin jin b'acin rai yana tattaro nutsuwa da dakiya ya yafama kansa"cikin tausayin iyayen nasu ya iso gabansu....nurah! Ina kaje haka baka dawo gida  da wuri ba, Anata kiranka ta waya  baka d'auka ba??cewar Abba suna binsa da kallo....sunkuyar dakai k'asa yayi yana tunanin Abinda zai fad'a musu sbd su yadda"kasancewar be saba yin k'arya ba"kuma baya jin zai iya sanar musu Ainahin gaskiyar Abinda ya faru...wai bada kai Ake mgn bane?"cewar daddy Ad'an tsawace"kuyi hak'uri Abba Ina gidansu wani Abokinah k'anwarsa ce ta k'one "shine na tsaya na kula da ita da Abinda ya dace"wayarma tana silent yanzun me nafef ya saukeni"Ajiyar zuciya suka saki tare da fad'in Allah ya kyauta"daga haka suka wuce ciki"Dr darma ya rufe get d'in gidan ya nufi k'ofar d'akinsa yana tunanin Abinda yaga Mubarak nayi d'azun"da hanzari ya bud'e k'ofar d'akin ya shigo ya kunnah haske ya nufi bath room "Agaggauce ya d'auro Alwallah ya fito ya kabbara sallar isha'i,bayan ya idar yayi shafa'i da wuturi "wajen k'arfe 11:30 pm ya fito daga cikin d'akin sanye da fara k'ar d'in jallabiya ya nufi inda yaga mubarak d'azun yaduk'a yana binnewa"k'arfen dake hannunsa ya saka yafara hak'o wajen.....k'irjinsa yayi wani irin bugu sbd ganin wasu layu had'e da Allurai da gefen zani da mayafi an yanka an daure"cike da mamaki da Al'ajabi ya d'aukesu ya Ajiye gefe ya maida ginar tsab ya rufe,kafin ya d'auki tarkacen layun yanufi d'aki dasu"dukda kasancewarsa masanin Abubuwa masu yawa yanada ilimi Akansu"Amma beyi gigin bincikaba ya barsu zuwa safe zaije wajen malaminsa daya koyar dashi Abinciki me layun suka k'unsa?"ransa yafi bashi kodai Ahyaan ko mama ummah tayima Asiri,shine  ta bama Mubarak ya binne Acikin gidan"yaja wani kakkauran tsaki had'e da furzan da wani irin zazzafan huci daga bakinsa yana taunar lips nasa kamar zai hudasu"ya lashi takobin muddin harda Ahyaan Acikin wannan sihirin wanda yayi shi ya jama kansa"da wannan tunanin bacci yayi Awon gaba dashi ba tare da yama shiryama baccin ba.....washe gari misalin k'arfe 2:38 pm"Ahyaan na zaune kan kujerah y'ar tsugunno  Atsakar gidan gaban tape tana wanke inner wears d'inta cikin roba"sanye take da plate d'in takalmi fashion pink colour masu taushin gaske"sunyi matuk'ar k'ara k'awata kyawun k'afar tata"yayinda da take sanye da doguwar riga ta Atamfa da hula navy blue tayi goshi style "fuskarta ba make up Amma tayi Shar da ita sai zuba k'amshi me kashe jiki takeyi"duka lips nata na cikin bakinta "tana pasin k'ofar shigowa tsakar gidan"mamy bata jima da fitaba wajen sunan k'anwar daddy"daga ita sai hamzavne Agidan"shi yana d'aki yana kallo"gaba d'aya cikin nishad'i take sbd tun safe Abba dazai fita ya Amshi takardunta ya tafi dasu"tana jiran dawowarsa"duka yau kwananta biyu da dawowa KT Amma bataje ko inaba in aka cire fitarsu ta jiya da Dr darma"har gidansu Khairiyyah taso taje yau mamy tace ta bari sai gobe Friday....k'amshin turarukan Dr darma masu kashe gangar jiki da zuciya suka fara rige rigen kaima kokafin hancinta ziyara ,kafin ta d'ago kanta har taji Amon jarumar muryansa me dad'in sauti na ratso kunnuwanta yana yin sallama "shi kuwa yana shigowa idanunsa Akanta suka fara sauka"sai Akayi sa'a ta d'an kallesa ta zabga masa wata uwar harara sbd tuna Abinda yamata jiya"kallon second 2 ta masa ta tab'e baki had'e da d'auke kanta"sanye yake da k'ananun kaya da p cap da takalmi sawu ciki"wanda sukayi shige da gogonsa da p cap d'insa "hannayensa na rik'e da ledoji guda biyu"fuskarsa ta d'an fad'a sbd Azumin daya tashi dashi"saidai ya k'ara haske"karan hancinsa yad'an fito"lips nasa sun k'ara yin jaa"directly inda take yak'ara so Aransa yaji dad'in ganin ta rufe gashin kanta"sosai yaji tausayinta dalilin binciken da aka masa d'azun akan layun dayaga Mubarak na binnewa"ita bata damu da rayuwar kowaba tana hidimar gabanta Amma wasu najin zafinta"ya Ayyana Aransa.......tsaye yayi gefenta in low voice ya furta"ba sannu da zuwa sai harara da za'a Aiko mun da ita *Amun dago* ? k'in tankashi tayi sai kuma ta dinga b'abb'aka dariya "ya tab'e baki yana fad'in Allah yaka miki sauk'i"hmmm! mlm ka wani shigoma mutane gida da ledoji kamar wani magidanci"sannu da zuwa Akanme zanyiwa k'anina sannu da....shiru tayi sbd ganin yayo kanta ta rintse Ido "yaja tsaki yana fad'in matsoraciyar banza"magidanci kuma saura k'iris na zama"bud'e idon tayi tace"Ashema tsoro?"ta k'are maganar Asadda  take matse under ware nata"kiyi ki gama wannan wankin  gulmar"Azumi nakeyi ki had'amun Abin bud'a baki "ya k'are maganar yana cin magani ya Ajiye lodojin gabanta"Anutse yaci gaba da cewa"kiyi mun kunun gyad'a "ga kayan fruit nan ina son fruit salad"wannan naman kiyi farfesu dashi"Allah ko?"ban sani ba"ni wlh kana bani mamaki da wannan Abin da kake mun"sai kace wata k'anwarka ko wacce kake iko da ita? kuma babuma irin ko dan Allah  kimun Abu kaza "ah ah umarni kawai kake bani"Eh na baki ko bazaki yiba ne ?"Eh banayi"Allah bara mamy ta tashi saina gaya mata "uhmm! mamyn Ai bata nan ta tafi sunan gidan uncle nuhu"ki tashi ki matse kayan kije toilet ki shanya"daga yau na hanaki shanya inner wears Atsakar gidan nan"murmushi ta saki tana mik'ewa tsaye ta nufi gaban tape d'in tace"yanzun Agabanka zan shanya saika hana idan ka Isa...bece komai ba ya zaro Allura daga cikin Aljihun wondonsa dake cikin siringi harda ruwa ma cikinta"ya wani tsuke fuska yana binta da wani irin kallo me wuyar fassara yaga ta zaro Ido"murmushi yakusan sub'uce masa "kinsan Allah?"mintina 5 na baki muje Agabana ki shanya ki fito muyi Aikin nan nata yaki ko kuwa babu ruwana da lafiyan ki qlau Allura zan d'irka miki....haba broth wannan wane irin mugunta ne?"nidai ka maida Alluran bana son ganinta, Ai zanyi yadda kakeso "dama fa wasa nakeyi"shiru yayi yak'i mgn ya maida Alluran inda ya fiddota yana cin dariya Azuciyarsa"gaba d'aya jikinsa ya mutu sbd yadda ta kwantar da murya tana mgn Amairairai ce....to ka d'auki robar muje na shanya"Amamakinta bece komai ba ya d'aukar mata kamar yadda ta buk'ata.....har cikin toilet d'in mamy ya Ajiye mata sannan ya fito ya barta ciki ya tsaya daga cikin parlourn gefen k'ofar bed room d'in yana kallon hamza dake kallon TV "wanda yayi hakane sbd yasan zata iya zuwa ta rufe k'ofar bed room d'in "shi kuma beson kad'aicewarsu Adak'in su kad'ai ,yasan mamy bata so kuma shima yana son bin dokar Allah da Abinda Addini yace Ayi"yana nan kiran bilkisu ya shigo cikin wayarsa wacce tuni yama haddace number nata"saidai harta tsinke be d'aga ba"sai tsaki yaja sbd ganin ko Awa guda basuyiba da rabuwa yanzun ba"taje chemist nashi wai tana zazzab'i yamata Allura"shine yace"saidai ya mata ga hannu"ta Amince ya mata yabata magani"zata biya 1500 Amma saita bada 50k "harara ya wurgo mata"ya zari y'an 500 guda ukku yace"ta d'auki sauran kud'inta taje ta bashi waje"yana jin k'awarta na cewa haba *Ikkhee* ! ba girmanki bane ki tsaya namiji na miki irin wannan cin fuskar.....yaja tsaki yana tunanin meyasa mutane ke nuna zasu iya mallakar komai idan sunada kud'i? dama tunda yafara ganin yarinyar ya fahimci y'ar gidan masu dashi ce"kuma sangartacciya ce.....ka matsa na wuce"siririyar muryar Ahyaan ta katse masa tunani"saida ya d'an lumshe Ido yakoma bud'ewa kafin yad'an gyara ta wuce rik'e da robar"saiya biyo bayanta zuwa tsakar gidan"ganin zata wucesa ya sakashi shan gabanta"oh yah rabbih! pot& knife zan je na d'auka a kitchen" wlh matarka ta shiga ukku da fitinarka haba"ta fad'a tana wucesa"shi kuwa Akaron farko ya saki k'ayataccen murmushi yaje ya zauna kan kujerah d'in data tashi"yana nan zaune ta iso gefensa ta Ajiye tukunyar ta jawo ledar naman"kaji ne manya guda biyu "Amma yayyankasu daga can inda ya siyo su"kawo na kama miki"to baka zauna mun kar kujerar ba"ta fad'a tana zuwa ta zubo ruwa cikin tukunyar"beyi mgn ba  ya tashi ya tsugunnah"tana dawowa ta zauna"ta fara wanke naman yanata kallon yatsun hannunta dana k'afarta"can kuma ya fara kama mata tana ragema masu girma yawa"daga k'arshe suka wanke naman atare, ita ta yanka Albasa"bayan takai tukunyar kitchen ta fito da morning fresh sbd su wanke hannuwansu"dukda ba wata fira sukeyi ba"Amma tayi mamakin tayata Aikin da yayi"jefi jefi idan sun had'a Ido dashi harara take sakar masa "shima yana kallonta ta k'asan Ido"yak'i ya tankata"zoki zubamin na wanke hannuna"ya fad'a yana tsayawa gefen tape d'in yad'an duk'a"batace komai ba ta matso ta zuba masa ya fara sab'e duka hannayen nasa"ita kuma ta kunnah tape d'in ya fara wankewa"koda ya idar sbd Jan mgn saiya watso mata ruwan hannunsa saman fuska yana fad'in" *Amun dago* kema zoki wanke saina zuba miki ko?"ba k'aramin haushi tajiba ,ta rasa mesa be iya kiranta da Ahyaan ?Amma saita sharesa"tak'i bashi yazuba mata saita zuba da kanta"koda yaga haka saiya wuce kitchen ya d'akko wata robar da wuk'a yadawo yasamu ta gama wanke hannun "tashi muje parlour"batayi mgn ba ta d'auki ledar fruits d'in tabishi"kashe kayan kallon yayi sbd ganin hamzan yayi bacci"Akanme zaka









