Showing 51001 words to 54000 words out of 112373 words

Chapter 18 - AGE MATE'S Complete Document book by Momy Fareesa .txt

23 Dec 2024

12819

can"Allah yasa Alkhairi"Ahyaan dai batace komai ba ta wuce ciki shi kuma yafita.


*Monday*��


wannan book d'in na kudine! idan kina buk'atar siya serious 500 normal grp vip grp 1000
Acc n 2230373842 NABILA ALIYU UBA BANK kituro shaidar biyanki 08100084251


dan girman Allah da dajarar iyayenki karki mun mgn idan baki shirya siyaba


Bana son kira a what's app kawai zakimun mgn


Idan kika karantamun book baki biyani hakk'ina ba ko kika siya kika fitar mun Allah ya isa banyafe miki ba
#Mommyn fareesa
#Dr Nura Darma
#Ahyaan
#mr Mahuta
#AA mashi
#mu'az
#Khairiyyah
#Ammah
#Ummah
#ikkhee
7/21/24, 11:01 - Buhainat: � *AGE MATES*��♀�


*37&38*








*Littafin kud'i ne!*


*Monday*
misalin k'arfe 10:38 am"Ahyaan ce zaune a office nata tana danne danne a laptop "saidai gaba d'aya hankalinta ba'a nan yake ba tana tunanin meyasa Dr darma yak'i sake mata kamar da?"ita ba damuwa tayi da hakan ba .kawai tana so tasan meyasa yayi hakan?"tun bayan mamy ta shiryasu,yanzun iya karta dashi da safe su gaisa shikenan "idan ya shigo tana a parlourn zaice mata sannu da hutawa"ya dena fira da ita kamar Abaya idan suna shiri,ya dena tsokanarta ,ya dena sakata Aiki "kawai dai hidima da ita ne be dena ba"idan yasan tana buk'atar Abu zai bada Abata ko kuma ya Aiko mata dashi"yanzun haka tanaso suyi shawarah game da soyayyar ta da AA Mashi"Amma bataga fuska ba Awajensa "danko fara'a yadena yimata shiyasa yanzun har kwarjini yake mata a fuska....dukan table d'in da Akayi ya saka ta sauke numfashi tana d'ago kanta suka had'a Ido dashi.yana sanye da suit sky blue da farin gilashi"ya wanku sosai"wani tattausan murmushi ya jefeta dashi yana furta tunanin me kikeyi haka *Aminatu* ? dam ! K'irjinta ya buga "wannan ne karon farko da taji Ainahin sunanta Abakinsa"dukda batayi mamakin jinba sbd Anan kowa dashi yake kiranta"saidai yadda ya furta d'in sai taji wani iri daban"gaba d'aya sai taji duk duniya kamar Dr darma yafi kowa iya furta harafin sunan nata har yayi dad'i....wai baza'a mun mgn bane na juya?"ya fad'a still yana daga tsayen"I'm sorry Ina d'an wani nazari ne, kasan yanzun nan na shigo sbd nad'an huta kafin 11 tayi mu cigaba daga inda muka tsaya ko?"hakane Amma niba wannan ne ya kawoni ba"nazo naji Amsata ne.ta sunkuyyar da kai "kinji?"ta sauke Ajiyar zuciya tana d'ago kanta ta juya fararen dara daran lulu eyes d'inta murya can ciki tace"na Amince dakai.... Alhamdulillah! ya fad'a yana yin d'an tsalle tamkar wani yaro"ta saki murmushi,yaja kujerah ya zauna yana tsura mata Ido"thank you so much my sweet heart"in sha Allah indai nine miji Agareki baza kiyi dana sani ba"so pls idan ba damuwa inaso ki sanar Agida zan cigaba da zuwa"sannan zanyi mgn dasu daddy sbd su bani damar turo magaba tana Ayi mgn sbd da gaske nakeyi Ina sonki da Aure.Atak'aice dai kinsan sunana"ni haifaffen garin nan ne"muna zaune nida iyayena Anguwar modoji "mahaifinah d'an kasuwa ne , Asalin sa d'an jihar MASHI LG ne"duk dangin mu nacan"kasuwanci yakawo mahaifinah Anan garin har yayi Aure aka samemu...mu 13 ne Agidan mu"nine d'a na farko "mu 7 ne wajen Ammi nah"sai Anty Amarya nada y'ay'a 6"Anan garin nayi karatu nah gaba d'aya har na kammala na fara Aiki"banida wani Amini sama da haisam"shi yayi Aure harda y'arsa.....wannan shine tak'aitaccen tahirina Ahyaan "idan kina son jin fin haka ko kuma halayena na baki dama kije ki bincika"ya fad'a yana d'an murmushi "ba tare data kallesaba tace" Masha Allah! ya jinjina kansa yana mik'ewa tsaye yace"bara naje kar Ace muna office muna soyayya ko?"kanta ta gyad'a masa shi kuma yafita....
zaune take A parlourn gidan su suna kallon TV itada yayanta da k'anwar su"dududu befi kwana 2 da dawowa k'asar ba....can Aka hasko kyakykyawar fuskar Ahyaan tana labarai"Atake Ikkhee taja tsaki tana kallon kausar tace"ke dallah canza mana channel"bana son ganin shegiyar yarinyar nan na tsaneta....da mamaki Mr mahuta ya kalleta yace meyasa kika tsaneta?"cikin wani yanayi Ikkhee ke sanar masa mak'asudin Abin"ta kuma nuna masa ma son juna Ahyaan da Dr darma keyi"toke meyasa ba zaki hak'ura dashi ba?"Ai na jima da hak'ura dashi yaya tunda yanuna baya sona"saidai inada wani buri Araina game da ita dashima gaba d'aya"inaso nayi mata wani gib'i Arayuwa"yanzun haka na saka kullum Ana bibiyarta"tana banza talaka me Aiki abiyata Albashin har zata nemi takani. nace makafa yaya Alokacin yaso ya kulani Amma y'ar iskar yarinyar nan ta kama yimasa chakulkuli suka wuce ta gaba suna dariya. bayan kuma cikin chemist d'in ta yadamun bak'ak'en magan ganu nacin fuska son ranta.....shiru Mr mahuta yayi yana nazari"domin fad'uwa tazo daidai da zama"saidai bayaso yasaka k'anwarsa cikin case d'in "dan shima ya lashi takobin saiya d'and'ani zumar Ahyaan kota halin k'ak'a"saidai dole kafin k'udurinsa yacika ya samu wani yasaka cikin case d'in sbd karta kwab'e musu"iya saninsa tunda ya d'ora idanunsa Akan yarinyar yake fama da sha'awarta"ya kalli Ikkhee dake sauraren jin yace wani Abu"ke tashi kije ciki"ya fad'a yana kallon kausar"bata ce musu komai ba tabar wajen"yayi k'asa da murya Ahankali yace"karki damu ki cigaba da bibiyarta idan kin samo inda take ,kuma ba mutane A wajen kimun mgn ta waya"zan turo Asaceta cikin badda kama Ayi reping nata..... tabbas yaya shine kawai Abinda za'a mata na huce"kuma ta haka ne shima Dr d'in zai tsaneta ya juya mata baya"saidai ta yaya hakan zai faru yaya? sbd karta gane mune kuma daga baya Asirinmu yatonu , musammun tunda y'ar jarida ce! karki samu damuwa wad'anda za'a saka su saceta bata sansu ba"ke kuma bazata gankiba balle ta zargeki"sannan sai Ambata Abinda zai bugar da ita komai zai faru"daga nan sai a yasar da ita saman titi. kinga bazata san kosu waye suka Aikata mata hakan ba"iyaka kawai kiyi k'ok'arin sanin wad'anda zaki saka su bibiyenta bazasu fallasama kowa ba"ah ah yaya basuda matsala course mate d'ina, kuma mayun kud'i ne"ta fad'a tana d'an murmushi sbd k'arya ta zabga masa"k'ananun y'an dabane ,kuma y'an shaye shaye wajensu take siyan kayan maye"Adalilin hakan ta sansu"shi kuwa Mr mahuta beyi zaton komai ba ya Amince...


*****************
tun lokacin da Ahyaan ta sanarwa Abdallah Mashi tayi Accepting d'in soyayyar sa "gaba d'aya wajen Aikin nasu Akasan suna son juna"sbd yadda yake nuna mata soyayya k'arara da tsantsar kulawa"Ayanzun duk Friday yake zuwa kai mata ziyara"su daddy da Abba sunsan dashi"sbd sun saka Ayi bincike game dashi da iyayensa da halayyarsa"kuma Alhamdulillah harma yaturo iyayen nasa sun kawo kud'in gaisuwa"rana kawai za'a saka yanzun" duk Abinda ke faruwa Dr darma yasani saidai be saka kansa cikin hidimar ba"ko wajen bincike da Akace zasuje da khaleel uzurin Aikinsa yakawo shiyasa beje ba"saidai duk yana Ankare da hidimar da Akeyi "sarai ya fahimci Ahyaan naso ta masa zancen Amma bataga fuska ba Awajensa.....tun lokacin da yaga haka jikinsa yayi mugun sanyi"Ada yana ganin kamar wasa zuciyarsa keyi masa ba son Ahyaan yake ba"Amma yanzun data kasance tana gab da zama rabon wani ya fahimci zuciyarsa ta jima da mutuwa a soyayyar yarinyar"wacce sai bayan yadawo Nigeria ne yafara jin Alamar soyayyar ta da zafin kishinta Aransa Amma Ada baya jin hakan"ya kuma fahimci bata sonsa"idan tana sonsa bazata kula wani ba"shi kuma Ayanzun baya jin zaima iya furta mata"gara kawai ya bari daga shi sai zuciyarsa....da wannan tunanin yaci gaba da rayuwa"duk yayi rama ga Azumi duk litinin da Alhamis sai yayi"ga wani irin shiru shiru yak'arayi ,ba sosai yake kula kowa ba"dukda dama ya kasance bame yawan surutu ba"dama yawan firan tasa da ita ne"saidai sarai halin damuwar daya saka kansa Aciki mamy na lura"kuma jikinta yayi sanyi itama"saidai dukda haka tana Addu'ar Allah ya musu zab'in Alkhairi gaba d'aya "garama Ahyaan d'in ita tanada samari"shi kuwa baya kula mata.....Acikin gidan kuwa har yanzun tsakanin zaman luba da Abba babu Abinda ya sauya zane"saidai tanama shirin zuwa k'asar nijar itada wata k'awarta da zata rakata ,sbd suje Akarya sihirin daya koma kanta na warin jab'a datakeyi"sbd har yanzun bata dena warin ba"kuma tana so Ayima Ahyaan Aikin da za'a koreta daga wajen Aiki.sai kwatsam Aka kawo kud'in gaisuwar Ahyaan d'in"hakan yakoma dagula ma ummah luba lissafi"Ayanzun ta yanke shawaran siyar da gadonta da tumakai 3 datake kiwo gidan mahaifiyarta sbd ta tafi nijar...Allah ya tsare mana imaninmu yasa mudace duniya da lahira....
Ayau yakama week end ba office "kuma Ajiya Ahyaan ta d'auki Albashin farko nera 200f...."Ayau kuma taje ta cire duka kud'in da safe ta bama mamy"sai ta kama dariya tace"Ahyaan Ai kud'inki ne ko?"zan d'auki 2k na saka Albarka"saina kaima Alh ya gani"kuma suma su mama zaki kai su gani su d'auki Abinda zasu d'auka "itama Ammah da musty yaka mata ki basu wani su saka Albarka"dato ta Amsa"mamy ta d'auki kud'in ta samu daddy har d'aki takai masa"sai yakama murmushi yace"toni meye sai An kamun na d'auka ?"na gani Allah yasa Albarka"Ameen Amma Alh ka d'auki wani Abin"shima 2k ya d'auka"mamy kuma da kanta taje ta kaima su mamah kud'in "saidai kason ya canza"dubu ishirin ishirin Abba yace su d'auka itada daddy"suma shida mama haka zasu d'auka, sai Abata sauran ta bama y'an uwanta Abokan haihuwa wani Abu"sannan kuma da kanta ta bama Ammah"badan daddy yasoba ya Amince suka Amshi kud'in sai dan sbd Abba yanuna beji dad'i ba"lokacin da sauran kud'in suka zo hannun Ahyaan biyu ta raba ta kalli mamy tace"gashi ki Ajiye ma broth"haba Ahyaan! wannan wane irin Abune? Ina Aka tab'a haka?ah ah mamy dan Allah nidai ki barshi nida broth duk d'aya ne"Abinsa nawane ,Abuna nasa ne ko?"mamy na k'ok'arin mgn shi kuma ya shigo cikin parlourn "wanda sarai yaji kalamanta"Atake zuciyarsa tayi wani irin rauni"yabita da kallo itama shine take kallo"Atake ta fahimci yayi rama"saidai suna had'a Ido ta janye idanuwanta"ya zauna kan kujerah yana fad'in mamy da y'arta sannunku! yauwa sai yanzun ka tashi ?"cewar mamy"uhmm" kawai yafad'a "ita kuma saita bar musu parlourn"Ahyaan ta saci kallonsa yana sanye da k'ananun kaya yayi kyau sosai da haske"Ashe ita yake kallo"wai broth baka lafiya ne?"me kika gani?"ba naga ka rame ba"shiru kawai yayi yana dannah waya"gashi tunda baza kayi mgn ba"ta fad'a tana Ajiye masa 50k saman jikinsa"ya kalleta ya kalli kud'in"tamkar baya so yace na meye?"naka ne jiya na d'auki Albashin farko"Masha Allah! Allah yasa Albarka "Amma sunyi yawa ki bani 5k ma sunyi nagode"nidai Allah ah ah ka d'auka duka indai nida su khaleel d'aya ne Awajenka"shiru kawai yayi sbd shine kawai yasan me yakeji sbd shagwab'ar datakeyi"shi yaushe rabonma daya zauna har suyi mgn irin haka da ita?"kaji broth?"girgiza kansa yayi ya mik'e tsaye rik'e da kud'in ya zare 5k"saiya kalleta da rinannun idanunsa da har sun fara sauya kala"sosai yayi mamakin ganin Idanunta sun ciko da k'wallah....indai bazaka Amsa duka ba toka bani"ta k'are maganar hawaye na ziraro mata saman kyakykyawar fuskarta"yana k'ok'arin mgn kira ya shigo wayarsa"dukda yau week end ne yayi mamakin ganin kiran daga Asibiti ne"sallama kawai yayi"Dr Marwan ya Amasa tare da cewa" pls doctor idan kana kusa kazo ka taimaka mana An kawo patient emergency wlh"ko numfashi batayi"ni kuma ba irin wannan matsalar na sani ba"gashi likitoci basufi 5 bane A Asibitin sbd yau week end "wlh Akwai matsala huhun yarinyar ne keda matsalar"kamar yanda Dr John ya fad'a"kayi hak'uri pls kazo ko zaka iya dubata mugani...okay kawai yafad'a yana yanke wayar "ya duba gefensa yaga wayam babu Ahyaan"saiya saka kud'in cikin Aljihu ya fita daga cikin parlourn da sauri.....
Tsaye yake gaban emergency room d'in da farar jallabiya Ajikinsa "yayi uban gumi sbd tashin hankali da mamakin yaushe yarinyar nan ta fara shaye shaye har ya fara yimata irin wannan illar haka Ajiki?"kansa ya d'ago yana furzan da huci daga bakinsa yabi Dr Marwan da kallo daya gama wayar zai wuce....pls doctor ya kukayi dashi ne?"kodai mu canza wani Asibitin ne tunda babu doctors Anan"kasan yau weeks ends dama Ana samun irin wannan matsalar ta rashin doctors da yawa "sannan yanzun kafin kuje da ita wani Asibitin Adubata An samu matsala"gara kayi hak'uri nanda 10 minit zai iso"shima Alfarma muka nema gunsa, dukda tsarin Asibiti nan idan lokacin da bana Aiki bane bai zama dole likitah yatsaya ya duba patient ba"Amma da yake shi babban likitah ne koda wane lokaci zamu iya kiransa"it's okay"mr mahuta ya fad'a cikin gamsuwa yaci gaba da safa da marwa Awajen"ba'a fi cikakken minti 10 ba Dr darma ya iso wajen"daddad'an k'amshin turarensa ya fara kawowa Mr mahuta ziyara"ya juyo da sauri sbd yaji kamar yasan me wannan k'amshin....Ido hud'u sukayi dashi"k'irjin Mr mahuta ya buga! musammun daya san shi likitah ne"fatansa Allah yasa ba shine aka kira yanzun ba..... doctor ka k'araso ne?"cewar Dr Marwan daya fito shida wasu nurses guda biyu daga cikin wani office "Anutse ya juyo fuska Ahad'e yace"uhmm Ina patient d'in?"tana nan ciki su Dr John na'a kanta"gama yayanta nan daya kawota yadamu sosai"pls Dr Abata taimakon daya dace"Cike da shan k'amshi Mr mahuta yace"Eh ka dubata ko nawane zamu biya indai Akanta ne"nasoma mu tafi private hospital da tafi nan to kuma time ya k'ure"Dr darma beyi mgn ba saidai wani shegen murmushi kawai daya keyi yatura k'ofar emergency room d'in ya shiga"Mr mahuta ya sauke Ajiyar zuciya "saidai befi 5minit da shiga ba yafito"dama ya shiga sbd yaga fuskar patient d'in da kuma duba file nata"dan yaga mak'asudin ciwon nata....yaya ka fito kuma?"cewar Mr mahuta yana shan gabansa"cike da jinkai Dr darma yabishi da kallo fuska Asake yace"nuna dukiya ko Mulki da isah basu sakawa nayi Aiki nah! saidai na kanyi Aikin sbd tausayi ko Alfarma! saidai kashhhhh"kai baka daga cikin wad'anda zanji tausayi balle har nayima Alfarma"sbd Aganina duk me tunanin kud'i suna iya maganin duk wata damuwa ta duniya"to kamata yayi duk sadda ya tashi yin wani Abu to yayi Amfani da kud'in wajen neman abun yaga ko zai iya samu"ya k'are maganar cikin gadarah yana sakin wani makirin murmushi ya rab'a ta gefen Mr mahuta ya fara tafiyarsa cikin k'asaita yana basarwa" tamkar tauraron dake haskawa haka kowa ya bishi da kallo"wasu nurses d'in najin inama inama....cikin tsananin b'acin rai da damuwa Mr mahuta ya fara masifa da cewa waye kai?"yaushe kayi karatun harka zama likitan balle ka gayan mgn?"Ayanzun ko k'asar waje ne Ake da buk'atar Akaita zamu kaita"kuma yanzun zamu bar wannan banzar Asibitin "saidai inaso kasani wlh wlh !! sai kayi nadamar Abinda kamun"kuma daga yau kadena Aiki Anan "Dr darma beko kalli gefen dayake ba ya Ida yin gaba yabar wajen"dama burunsa ya bashi haushi ya gaya masa mgn "ya kuma gaya masa bashida matsala"batun kurarin da yakeyi da maganga nunsa na burga basu damesa ba"saidai yayi mamakin ganin bilkisu ce k'anwar mr mahuta"sannan beyi zaton kamarta duka 25 yrs tana irin wannan shaye shayen "da yake neman yima lafiyarta lahani ba...da wannan tunanin ya wuce chemist"sai bayan sallar la'asar yanufo gidan sbd yunwar daya kwaso... Ada sashen su mamah yayi niyar tafiya saiya tuna ba itace keda girki ba"hakan yasa ya wuce wajen su mamy"tsakar gidan ya kallah yaga ledar biscuits dasu chiweengum dasu sweet"ga kuma abun goro"haka nan yaji fad'uwar gaba "saiya dake ya shigo cikin parlourn da sallama.....katan d'in biscuits kusan guda 12 dana ruwa da lemo dasu sweets ya samu tsume gefen bango Ajiye"mamy na zaune da wasu gabanta tana d'aurawa Afaran leda"ta bishi da kallo tana Amsa sallamarsa"saida ya zauna kafin yac"e wai goro da Alawan meye ?"na saka ranar Auren Ahyaan ne"gama naka nan"wata 5 aka saka ranar"ta kare maganar tana mik'a masa k'ulli me d'an girma dake d'aure cikin bak'ar leda......��


sharhi �
pls bana son k'orafi kunl zuba����
wannan book d'in na kudine! idan kina buk'atar siya serious 500 normal grp vip grp 1000
Acc n 2230373842 NABILA ALIYU UBA BANK kituro shaidar biyanki 08100084251


dan girman Allah da dajarar iyayenki karki mun mgn idan baki shirya siyaba


Bana son kira a what's app kawai zakimun mgn


Idan kika karantamun book baki biyani hakk'ina ba ko kika siya kika fitar mun Allah ya isa banyafe miki ba


#Mommyn fareesa
#Dr Nura Darma
#Ahyaan
#mr Mahuta
#AA mashi
#mu'az
#Khairiyyah
#Ammah
#Ummah
#ikkhee
7/21/24, 11:01 - Buhainat: ��♀� *AGE MATES* �


*39&40*








*Littafin kud'i ne!*


.......tamkar saukar Aradu ! haka Dr darma yaji kalaman mamy cikin kunnuwansa"ga wani irin mahaukacin bugu da k'irjinsa keyi fat fat fat!!!....cike da dauriya had'e da b'oye yanayin daya tsintsi kansa Aciki ya had'a haruffan guda ukku wajen furta"Allah yasa Alkhairi! yafad'a da k'yar ba tare daya Amshi ledar da mamyn ke mik'o masaba"yadai girgiza kansa Alamar baya buk'ata"daga haka ya mik'e tsaye yabar parlourn "Abincin da baiciba kenan ya wuce d'aki ya kwanta ciwon kai me tsanani ya masa sallama"sai gab da sallar magrib ya watsa ruwa ya fito sbd ya tafi masjeed"idanunsa sunyi wani irin jaa"inda da yawan mutanan dake a *gida biyu* sun gansa Alokacin da sun tabbatar da babu lafiya"gaba d'aya jinsa yakeyi wani iri kamar bamai rai ba"Ahaka ya tursasa zuciyarsa yayi sallar magrib ya zauna yafara karanta Alkur'ani me girma sannan ya jira Aka gabatar da sallar isha'i"ba laifi yaji zuciyarsa tayi sanyi"saidai tunanin Abin na'a ransa daram"ji yakeyi yanzun daya Ida tabbata ita ba tashi bace yake jin wani sonta na fusgarsa"sunan Allah kawai yake Ambata Azuciyarsa yana jin tausayin kansa"sbd yasan Abanza yake damuwa sbd wacce yakeyi Akan ta ita ba tasan yana yiba..... Awannan dare Dr darma yayi shi cikin wani irin yanayi.
mamy kuwa bata ji haushin k'in Amsar kayan saka ranar da baiyiba"hasalima tausayinsa taji"saidai tasan matar mutum kabarinsa"kuma idan har Ahyaan na sonshi da bazata kula kowa ba"iyaka zata cigaba da yimasa Addu'ar dangana da samun wacce ta fita"sbd ta jima da fahimtar matsalar yaron nata shiyasa yake yawaita Azumi "kasancewar sa me jin nauyinsu yasaka ya kasa fitowa zahiri ya nuna musu matsalarsa"Amma tana lura da komai"tasan da dalili da yasa yake yawaita yin Azumin nafilah"ta kuma tabbatar da kafaffiyar zuciyarsa ta hanashi ya bayyanah soyayyar sa ga Ahyaan"gashi ta sub'uce masa "wanda tanada yak'inin k'ilan sbd kar tace bata sonsa dan suna AGE MATE ita dashi shiyasa yak'i sanar mata da soyayyarsa...tana cikin wannan tunanin Ahyaan ta fito daga cikin d'akin ta zauna tana

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login