Showing 27001 words to 30000 words out of 83501 words
cikin nashi suna jiran layi yazo kansu, manal zaune take akan kujera tana kallon duk waɗanda suke wajen a cikin computer dake gabanta, idonta akansu ameesha wacce suke rike da hanun juna, komawa baya tayi da kujeranta tana kallon duk masu shigowa, duk cikinsu bataga wanda ya kware ba, Ameesha ta gaji sosai domin suna jimawa kafin su fito, ga ciwon cikin da takeji yana damunta sabida tana period, ɗaura kanta tayi a kafaɗanshi ta fara bacci a hankali yace "ko dai zamu tafi naga kamar baki da lafiya"
tace "ina lafiya bacci kawai nake ji"
yace "to yi bacci kafin azo kanmu"
bacci ta fara a hankali yayi shiru yana jin numfashinta a jikinshi, a hankali ya rike hanunta sosai dake cikin nashi, sun kara jimawa sosai kafin akace su shigo, tashinta yayi da sauri ta buɗe ido yace "muje an kiramu"
kallon time tayi a agogon hanunta tace "mun jima sosai"
hanunta ya rike zasu shiga, manal dake juyi akan kujera tana kallonsu har ya tsaya yana gyarawa ameesha hulan rigan sanyinta zasu shiga tace "kuce an tashi sai gobe kuma"
hanu yasa akan handle ɗin akace "an tashi sai gobe kuma"
ranshi ne yayi mugun ɓaci zaiyi magana ameesha ta rike mishi hanu tareda girgiza mishi kai alaman yayi hakuri, shiru yayi taja hanunshi suka tafi, basuyi magana ba har suka isa gida, rai ɓace ya wuce ɗaki umma tana ganin yanayin ameesha tace "to yauma haka"
Imran kam ɗauke kai yayi baima yi magana ba, ɗakin ta shiga ya kwanta akan gado ya juya baya, zama tayi a kasa ta ɗaura kanta a gefenshi tayi shiru, a hankali ya juyo ya shafa gefen fuskanta yace "karki damu na miki alkawari gobe zamu koma"
murmushi yaga tayi wanda yake burin ganin tana yinshi a kullum tace "ka tabbata?"
yace "eh"
ya faɗi haka ne dan yasan da kyar yau tayi bacci zataga kamar ya fasa zuwa tasan halinshi, tashi tayi tace "to shikenan bari naje nasha magani cikina na ciwo"
zai rakata tace "no koma ka kwanta ka huta"
yace "bye"
fita tayi ya lumshe ido, ameesha itace rabin rayuwarshi.
washe gari tana jin ciwon ciki amma ta daure tazo tana hon a kofan gidan tana kiranshi kamar yadda ta saba "MAAAAAAAAN"
gani tayi ya fito rataye da jakan takaddun a bayanshi da sauri yazo ya hau mashin ɗin suka tafi, tace "good morning"
yace "morning princess ya jikin?"
tace "da sauki"
yace "har kin kai fahad school?"
tace "yes gashi har na dawo kanata baccinka"
yace "gaskiya meesha ina ganin kokarinki bakya bacci kullum ɗawainiya kede sai kinga kowa yayi successful hankalinki yake kwanciya"
tayi murmushi kawai, Allah yasa basuyi late ba, suna shiga suka zauna akan kujera ta jarɓi jakan takaddun ta rungume, karan takalminta sukaji kowa ya tashi daga zaunen da yake itama ameesha ganin kowa ya tashi ta tashi, lokacin manal ta shigo tana waina makulli a hanunta, idonta ya sauka kan man wanda yake gyangyaɗi baima san ta shigo ba, cikin tsoro ameesha ganin ta zubawa man ido ta fara janshi alaman ya tashi, buɗe ido yayi yace "me kina jana?"
idonshi ya sauka kan manal wacce take aika mishi mugun kallo tana huci, ameesha tace "tashi"
a hankali ya tashi, wucewa tayi bata amsa gaisuwan kowa ba, saida ta wuce suka zauna, akan kujera ta zauna tana tuna wani irin abu zatayi mishi yaji zafin da taji lokacin data ganshi a zaune? ta nuna mishi ita ɗin wacece?"
kallonsu take ta cikin laptop ɗin har ta fara kiran interview, saida akazo kansu sannan tace an tashi sai gobe, cikin fusata ya dunƙule hanu zai buɗe kofan ameesha ta fara janshi, da kyar ta lallaɓashi suka fita, gani yayi tana hawaye yaji jikinshi yayi sanyi, yace "kar kiyi kuka gobe zamu dawo kinji?"
gyaɗa kai tayi, dama tayi kukan ne sabida tasan dole zai karaya bayason ganin tana kuka.
*Jiddah Ce...✍🏻*
08144818849
[09/04 à 08:06] JIDDA MAPI: 🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*DUHU DA HASKE*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
Na
*Jiddah S mapi*
*Chapter 9*
~Kullum tare suke fita aiki saiya ajeta kafin yake tafiya aiki, komai yana tafiya daidai, shine yake fitar da sabbin style's a kullum yana basu, zuwa yanzu ya saba da kowa na wajen banda manal wacce take aika mishi harara a duk lokacin da suka haɗa ido, kamar kullum yauma shida Ameesha da Imran da kuma fahad ne a cikin motar, tayi kyau sosai cikin black dress dogon riga tasa hula sannan tayi rolling siririn mayafi akai, tayi kyau sosai kamar sarauniyar kyau, fatar ta duk da bata cikin wani daɗi amma yana glowing sosai, tace "Imran kasan me?"
girgiza kai yayi fuskanshi ba walwala da alama yana cikin fushi dan tunda suka fara tafiya baiyi magana ba, a hankali ta juyo tana kallonshi, murmushi tayi tasa hanu ta shafa gefen fuskanshi sannan tace "Imran a koda yaushe idan na ganku cikin fushi baku san yadda nake ji bane a zuciyata, ko kaɗan banason ganinku kuna fushi, dan Allah kayi murmushi kaji?"
a hankali yace "ni ki kyaleni"
cikin son neman tsokananshi tace "to shikenan na barka amma ka tuna wancan beb ɗin?"
alama ya fara mata tayi shiru yana nuna mata man, dariya ta fara tana cewa "a,a barni na faɗa wancan kyakkyawar beb ɗin da tace tana san...."
da sauri ya rufe mata baki, shiru tayi yana sakinta yayi murmushi yace "gashi nayi"
man yana jinsu baice komai ba har ya ajesu a school, jakan fahad ta bashi tace "kaga an canja maka school ka dawo school ɗinsu Imran yanzu ba kai kaɗai bane kaida yayanka ne duk abinda kayi na rashin ji Imran zai faɗa mana"
kanshi ya sunkuyar yace "to"
karɓan jakanshi yayi tana ɗaga musu hanu har suka shiga ciki, juyowa tayi daga ɗaga musu hannun da murmushi akan fuskanta kamar kullum haɗa ido sukayi da man ya ɗaga mata gira, taɓe baki tayi tareda yin alaman "what?"
girgiza kai kawai yayi yaja motan suka tafi, driving yake ita kuma ta zuba mishi ido, juyowa yayi yaga ta ɗauke kai, baiyi magana ba, lips nashi na kasa a bakinshi yana tsotsa a hankali yake kallon titin, kara juyowa yayi suka haɗa ido da sauri ta ɗauke kai, murmushi yayi yaci gaba da driving, saida suka isa wajen aikinta ya juyo zasuyi sallama yaga ta zuba mishi ido da sauri ta ɗauke kai, zata fita taji ya rike hanunta, shiru tayi batayi magana ba, yace "meesha meyasa kike satan kallona?"
ji tayi gabanta ya faɗi, murza yatsunta yake a hankali cikin nata yace "kalleni"
kin kallonshi tayi
yace "kalleni mana meesha"
da sauri ta juyo ta maida fuskanta kamar na yara tace "gashi na juyo na kalleka me aciki? ban isa na kalleka bane? ko so kake na daina kallonka? gani kake kamar kana da kyau ko?"
murmushi kawai yayi ganin ta maidashi yaro, sakin hanunta yayi yace "kiyi aiki lafiya"
tace "bye"
hanu take ɗaga mishi har ya tafi bata daina ɗaga mishi hanu ba, juyowa tayi zata shiga ciki da sauri tayi baya tana waro ido ganin wannan katon yana kallonta yana huci, hannaye ta haɗa alaman roko tace "please please please"
cikin shaƙaƙƙen muryanshi yace "kullum sai kinzo late sai shegen bada hakuri da wannan karamin bakin naki kamar na kifi"
tace "dan Allah"
yace "yimin shiru kina wani kallona da wannan idanun naki kina ganin zaki iya tsoratani ne dasu?"
kanta ta sunkuyar kasa yace "wuce"
da sauri harda ɗan gudu ta wuce tana cewa "wayyo Allah wannan ƙaton ya samin ido da murya kamar an shaƙe mage"
zama tayi akan kujeranta ta fara rubuce rubucen duk abinda ya faru kafin tazo da wanda yake faruwa yanzu, satan kallonshi tayi taga yana kallon wayarshi, ciro wayarta tayi ta kira numbern man, yana ɗauka tayi kasa da murya tace "ka isa?"
yace "yes princess"
hamma yayi tace "yunwa kake ji?"
gyaɗa kai yayi tareda shagwaɓe fuska yace "yunwa meesha banci komai ba"
da sauri tace "sorry"
kashe wayan tayi ta ɓoye a aljihu, a hankali ta tashi taje wajen mutumin, kanta a kasa tace "sir inaso naje gida na ɗau wayata sabida na manta kuma rubutun jiya duk na tura a wayan"
cikin masifa yace "ban taɓa ɗaukan unserious yarinya kamar ke ba, bakida kokari shashasha jeki ɗauko ki dawo da wuri"
cikin sauri ta fita tana rufe ido kamar yara irin basu son a gansu ɗinnan, cikin kasa da murya tace "niba shashasha ba, nama fika wayo"
napep ta shiga zuwa gida da gudu ta fita a napep ɗin ta shige gida, Anty ta dafa kirji tace "Ameesha lafiya? ba dai wani laifin kikayi aka koreki ba?"
tana tafiya da saurinta kamar kullum tace "ba laifin da nayi na dawo na dafawa man abinci ashe da yunwa ya tafi kuma nasan wannan muguwar boss ɗinshi ba zata barshi yaje ya siya abinci yaci ba"
kayanta ta cire tasa riga da wando, wandon kamar three quarter a buɗe sosai pink, man ne ya siya mata da riga baƙi me faɗi, ta shiga kitchen ta fara dafa mishi shinkafa, cikin sauri take yi bata bari ruwa ya tafasa ba ta zuba kawai ta zuba gishiri me yawa da magi, ɗanawa tayi tace "gishiri ya ɗan wuce kaɗan"
da haka ta gama girkin, karamin mayafi tasa a kanta sannan tasa takalmi canvas wanda sukayi anko da fahad fita tayi daga gidan tana cewa "Anty na tafi"
napep ta shiga zuwa m.u.m"
Manal zaune take a office nata cikin riga da wando na suit fari, tayi parking gashinta da farin ribbon tasa hulan net ganin a mota take zuwa yasa bata damuwa da mayafi, takalmi me tsini ne a kafanta ta ɗaura glass nata baki a saman hulan, kafa ɗaya kan ɗaya ta ɗaura tana kallon laptop na gabanta duk abinda yake faruwa a cikin company tana gani, ido ta zuba mishi lokacin da taga yana knocking, a takaice tace "come in"
shigowa yayi, kamar kullum ya zauna kafin tace ya zauna, ɗago kai tayi daga kallon laptop ɗin yayi mata murmushi tareda cewa "gani"
tace "tashi"
tashi yayi ta ɗau takadda plain ta mika mishi tace "yanzu aka kirani anason zanen sabon motan da zasu fitar dashi a wannan shekaran sunce nan da minti goma suke bukata domin jirgi zai tashi nan da minti goma kuma kasan idan muka rasa wannan opportunity mun rasa babban aiki, samun wannan aikin zaifi mana duk aikin da mukayi a baya, na zana ɗaya tun jiya sai yau na gama, bansan biyu suke so ba sai yanzu suke faɗamin, nasan kai kaɗai ne zaka iya a cikin minti goma, daga yanzu na fara irga lokacinka, ɗauka yayi yace "an gama"
fita yayi da sauri ya zauna akan kujeranshi ya ɗau kaloli ya fara zane, tana zaune akan kujeran tana kallonshi yadda yake aiki da kwarewa, murmushi tayi ta gyara zama daga kan kujeran, wayar office aka kira ta ɗauka tasa a kunne tayi shiru, saida akayi magana kafin cikin muryanta me sanyin gaske tace "hello aiki zai kare nan da minti goma driver ɗinku ya tsaya a bakin kofan"
shiru tayi sai kuma tace "kun san bana karya alkawari"
katse wayan tayi tana kallonshi tana irga lokaci tasan zai gama a cikin minti goman, camera ta juya zuwa waje taga driver ɗinsu yana tsaye a bakin kofa, komar da camera ciki tayi idonta akan Abdul saura kaɗan ya gama, wayarshi ne yayi kara da sauri ya ciro daga aljihu ya amsa kiran ganin sunan da yayi saving da my meesha, sawa yayi a kunne yana cigaba da zanen yace "ya akayi?"
yace "Man fito waje ina jiranka yanzu a kofan company ɗinku*
da sauri yace "are you serious?"
tace "yes fito da wuri"
zaiyi magana ta katse, aje kalan yayi ya ture takaddan ya tashi da sauri ya fita, kallonshi take ta cikin computer ganin ya ture takaddan ya fita taji zuciyanta yana zafi, dunƙule hanu tayi ganin ya fita wajen wannan yarinyar da suke tafiya kullum tare, ji tayi wani abu ya tsaya mata a wuya, take idanunta suka sauya zuwa jajur, dunƙule hanu tayi ganin ameesha ta buɗe flaks na abincin ta ɗibo a spoon tasa mishi a baki, kallon agogo tayi taga saura minti huɗu, gani tayi ya rike hanun Ameesha sun samu wajen zama sun zauna tana bashi abincin a baki yana ci, da haka har minti goma ya cika, dunƙule hanu tayi ta buga jikin computer ta tashi a fusace zata fita, wani tunani tayi a hankali ta dawo ta zauna kan kujeran tana kallonsu, man yana jin gishiri har kwalwalwan kanshi amma yayi murmushi yace "my meesha abincin yayi daɗi naji daɗi sosai"
tace "amma gishiri ya ɗan wuce min ɗan kaɗan"
murmushi yayi yace "ba abinda ya wuce yayi daɗi"
tashi tayi tace "zan tafi"
kallon kayan jikinta yayi sannan yace "my meesha wannan wandon ai yayi guntu"
kallo tayi tace "guntu kuma? kaifa ka siyamin kuma kasan na saba"
cire rigan saman nashi yayi me ɗan tsayi yasa mata yace "ko kefa"
kuɗi ya ciro a aljihu ya bata yace "hau napep ki koma wajen aiki dan nasan karya kikayi"
tace "kamar ka sani nifa yunwa wannan lukutin ya dami rayuwata"
yace "karki damu zaki samu aiki anan very soon kinji?"
gyaɗa kai tayi, yayi mata kiss a gefen kumatu yace "bye?"
tafiya tayi yana kallonta har saida ta fita ya koma ciki, rufe ido manal tayi lokacin da taga yana mata kiss, gani tayi ya koma ya zauna yana aikinshi, kiran wayarta akayi, tana ɗauka sukace "mun fasa wannan aikin dake, yau kin karya alƙawari"
zatayi magana suka katse wayan, a fusace ta tashi zuwa waje, direct wajenshi taje tasa hanu duka biyu akan table na gabanshi ta zuba mishi manyan idanunta da suke cike da ɓacin rai, huci take tana kallonshi, da mamakinshi yake kallonta, ganin kallon yayi yace "me kuma nayi..."
cikin tsawa tace "rufemin baki"
shiru yayi, tace "meyasa baka gama zanen ba har saida sukace sun fasa? kasan wannan aikin shekara nawa nayi ina jiran samunshi?"
ganin baiyi magana ba tace "banza useless"
shima cikin ɓacin rai zaiyi magana ya tuna da maganan ameesha "koda me za'a maka ka danne zuciyarka ka dubi halin da muke ciki"
a hankali ya sunkuyar da kanshi, a fusace ta koma office nata tana bubbuga hanu kaɗan kaɗan akan table ɗin, koda aka tashi ameesha tana jiranshi a kofa kamar kullum, hanu ta ɗaga mishi yayi mata dariya kafin ya buɗe mata marfin motan tazo da sauri ta shiga, shima shiga yayi suka tafi.
washe gari sun aje fahad da Imran a school suna tafiya, ya kalleta yaga tayi shiru ba kamar kullum ba, baiyi magana ba har sukayi nisa batayi magana ba itama, a hankali yace "meesha me yake damunki?"
a hankali tace "dama dama akwai abinda nakeso na faɗa maka"
murmushi yayi yace "to meesha yaushe muka fara haka dake? inace kullum magana kawai muke kai tsaye bama ɓoyewa juna komai ki faɗamin menene?"
kanta kasa tana wasa da hanunta tace "dama...dama...dama....ni ina so...."
wayarshi aka kira yace "two minutes"
yana dubawa yaga sabon number ɗauka yayi yasa a kunne tareda cewa "salam"
muryan manal yaji cikin rashin son magana tace "yau bazanzo office da wuri ba, kafin nazo ka bawa kowa ya zana new dress guda biyar kai kuma guda goma sha biyar sauri ana buƙata da wuri"
kafin yayi magana ta katse wayan, bin wayan yayi da kallo ya maida muryanshi kamar nata yace "sauri dan ana buƙata da wuri, kamar wata uwata yadda take bani umarni"
ameesha a hankali tace "wacece?"
yace "boss ɗita ce"
gabanta taji ya faɗi tayi shiru shima bai kara ɗago maganan data fara ba harya ajeta a bakin kofan ta fita, gani tayi yaja motan da gudu ya bar wajen, yana zuwa ya sanar musu abinda zasuyi shima ya fara nashi.
manal ta fito daga ɗakinta sanye da rigan bacci tana mika, cikin takunta me cike da class ta isa kofan ɗakin ammi knocking tayi sannan ta tura ta shiga, ammi zaune akan gado tana kuka hankalinta ma baya nan tana kallon zoben dake sanye a ƙaramin yatsan ta, cikin kuka tace "ka tafi ka barni umar banajin daɗin wannan duniyan nafi son kana kusa dani"
harɗe hanu tayi a kirji ta jingina da jikin kofan tana kallonta, cikin kuka ta ɗago zata share hawaye ido huɗu sukayi da ita, da sauri ta share hawayen tace "ma..ma..manal yaushe kika shigo?"
murmushin gefen baki tayi mata kafin ta kame gashinta daya zubo ta fuska ta mayar bayanta hanunta ta zuba a cikin aljihun rigan baccin sannan ta karaso inda take, ɓoye hanun dake ɗauke da zoben ammi tayi, zama tayi a gefenta ta rungumeta tashi shiru kanta a kafaɗarta, a hankali ta ɗago ta kamo hanun dake ɗauke da zoben, cirewa ta fara ammi ta fara girgiza kai tana janyewa, saida ta cire zoben ta tashi ta fita, cikin gidan taje ta ɗauko wani katon dutse, ammi tana zaune taga ta shigo da dutsen, idanunta s waje take kallonta ganin ta nufota ta fara yin baya tana shigewa kan gadon sosai, murmushi manal tayi sannan ta aje zoben a kasa, dutsen ta ɗaga ta buga akan zoben saida ya tarwatse domin da karfi ta buga dutsen kuma manal tanada karfi sosai, ammi a tsorace take kallonta, ɗaukewa tayi ta fita dasu duka batayi magana ba, zubarwa tayi sannan ta koma ɗakinta, wanka tayi tazo ta shirya cikin dark green na shadda dogon riga anyi zubi da light green na zare, ba karamin kyau tayi ba bayan ta ɗaura ɗankwali ta rike siririn mayafi light green a hanunta, takalminta me tsayi da tsini sosai tasa baƙi sannan ta rike jaka baƙi, kamar kullum batayi kwalliya ba lipstick fari kawai ta shafa sannan ta fesa tsadadden turarenta ta rike makullin mota da kuma car key tana fito ta fara tafiya.
Ammi wayarta aka kira ta ɗauka tayi shiru, ji tayi ance