Showing 54001 words to 57000 words out of 83501 words
/>
cikin bada umarni tace "kace mata yace yana meeting baison haɗuwa da kowa yanzu"
yace "amma fa madam mahaif...."
ji yayi ta katseshi tace "mahaifiyarshi babu lafiya kwarai naji ka koma kace mata yace yana meeting baison haɗuwa da kowa"
shiru yayi, a tsawace tace "ko bazaka faɗa ba?"
a hankali yace "zan faɗa"
kashe wayan tayi, ya kasa tafiya na tsawon minti biyar kafin ya buɗe kofan, da sauri tazo tace "ina yake? yana zuwa ko?"
girgiza kai yayi yace "yana meeting yace bayason haɗuwa da kowa a halin yanzu"
cikin razana ta kalleshi, sannan ta girgiza kai tace "karya ne ba man bane ya faɗi haka ka buɗemin kofa kafin nayi maka ihu anan"
yace "shine"
tace "karya ne"
wayarshi ya buɗe ganin message ya shigo, video ɗin man yana zaune dasu mr chang ya gani manal ce ta turo mishi tace "ka nuna mata"
ameesha tureshi tayi da karfi zata shiga yace "kinga"
tsayawa tayi tana kallon wayar, ganin man tayi zaune a kyakkyawan office sanye da shadda me tsada yana juyi akan kujeranshi da aka rubuta manager suna tattaunawa da wasu fararen fata sanye da bakaken kaya suit, baya tayi bata buɗe kofan ba, tace "wan...nan ba... man ba...ne shi bada kayannan ya ya..fita ba"
cikin in ina tayi maganan ya matso mata da wayan yace "gashi kina ganinshi kuma ai shine manager ɗin wannan company kinga motarshi can"
buɗe kofan yayi yadda zataga motan taga an rubuta "ABDOOL MD"
a jikin motan, shiru tayi cikin shock take tsaye a wajen, yace "bai jima da dawowa daga gidansu madam ba ya jima acan shiyasa yayi late ɗin meeting ɗin"
cikin shocking ta buɗe bakinta da yake rawa, idonta ya tsaya da hawayen tace "m..ma.manal kenan?"
gyaɗa kai yayi yace "kwarai ai kullum yana zuwa idan yazo sai an kusa tashi suke dawowa tare"
a hankali ta juya baya ta fara tafiya, bata ce komai ba sai tafiya take kamar batada lafiya, hawayen sun tsaya, zuciyarta yana harbawa da sauri da sauri, duk maganan da ya faɗa mata yana dawowa kanta, saita tuna idan suna waya sai yace ana kiranshi har dare idan ta kirashi sai taji yana waya ta zaci ko aiki ne yasa hakan har tayi bacci sai safe suke haɗuwa, har ta hau kan kwalta bata sani ba, saura kiris wani mota ya bigeta bataji ba kuma bata gani ba tafiya kawai take, sauke glass yayi yace "ke makauniya ce? ki matsa akan hanya dalla"
matsawa tayi akan hanyan taci gaba da tafiya, tsayawa tayi ganin zata ɓata lokaci ta tari napep tayi mishi bayanin zai kaisu asibiti sannan ta shiga, har kofan gida ya kaisu ta fito ta shiga gidan da sallama, Anty da Imran da fahad har suna rige rige wajen tambayan "ina Abdool?"
a hankali tace "ban sameshi ba may be wani waje ya tafi"
Anty tace "ina zaije ya bar wayanshi?"
tace "mu fita da ita me mashin yana jiranmu a waje"
tare suke rike umma suka ɗagata har waje zuwa napep ɗin, kulle gidan sukayi suka shiga napep ɗin su duka, tafiya sukayi ameesha sai ɗauke kai take tana share hawaye "ai shine manager kullum tare suke tafiya da madam sai an kusa tashi suke dawowa, yace bayason ganin kowa yana meeting"
toshe kunne tayi tace "no.no..no"
Anty tace "ki nutsu ameesha zata samu sauki insha Allah"
city hospital ya kaisu ameesha ce ta yiwa likita magana sukazo da gadon suka ɗaurata akai tareda su Imran suke turawa har zuwa bakin kofan emergency room, suna tsaye su duka a bakin kofan kowa yayi shiru, ameesha sai kai kawo take yi, sun jima sosai sun kai awa biyu kafin aka buɗe kofan ameesha data zauna a kasa tayi tagumi ta taso da sauri har tana tuntuɓe tace "ya jikinta Dr?"
yace "da sauki amma kunyi late na kawota asibiti hakan yasa jikin yayi weak sosai, tanada hawan jini me karfi sannan abu kaɗan zai iyasa ta faɗi ƙasa ba fata ba zata iya kama struck wato shanyewan ɓarin jiki sai an kiyaye"
ameesha tace "Innalillahi wa inna ilaihiraji'un me yake damun umma daya kawo mata hawan jini? tunanin me take?"
Imran yace "zamu iya shiga?"
dr yace "eh amma idan ba zakuyi surutu ba dan hayaniya kaɗan zai iya kawo mata matsala"
sukace"to dr"
shiga sukayi duk jikinsu a mace musamman ameesha wacce har yanzu take cikin shock.
man sun jima suna meeting kafin suka tafi, saida aka tashi ya fito da sauri dan yasan yayi late ameesha zatayi ta jiranshi, yana fita ya shiga motar da aka bashi yayi hon zai fita megadi yace "yallaɓai?"
tsayawa yayi, megadi yace "ɗazu wata naga tana binka kuma sai kaga kuna tafiya tare da ita, daga baya naga tazo tace min wai mamanka babu lafiya zanyi magana naga ta juya a zafafe ta tafi"
da sauri yace "meesha?"
yace "ban san sunanta ba amma naga kuna tafiya tare tana jiranka anan..."
fita yayi da gudu yake driving zuwa gida, manal dake tsaye a gaban mirror ta kira wayan megadi tace "well done ka tsira da ranka"
kashe wayan tayi yabi da kallo, a kofan gida yayi parking yaga basa nan, juya motan yayi zai tafi gidansu ameesha yaji makocinsu yace "Abdulrahman"
tsayawa yayi yace "mutanen gidanku naga sun tafi asibiti da mamanka"
ido waje yace "yaushe?"
yace "da jimawa kuma naji sunce wa me napep city hospital zai kaisu"
da sauri yace "na gode"
tada motan yayi da gudu ya bar kofansu kamar zai kife da motan haka yake driving, city hospital yaje yayi parking da sauri ya fito ya fara nemansu, saida ya samu dr yace "ina neman waɗanda aka kawo yau?"
yace "ai sunada yawa wanne daga ciki?"
yace "babbar mata da yaro karami da kuma wani ɗan babba sai yarinya budurwa..."
da sauri yace "Ameesha sunanta?"
yace "eh su"
yace "okay ga can ɗakinsu"
da sauri da gudu yaje, knocking yayi kafin ya tura kofan ya shiga, tsayawa yayi a bakin kofa yana kallon umma dake bacci hanunta ɗaure da drip duk da akwai fanka amma ameesha tana fifita ta, jiki a mace ya fara takowa har zuwa wajenta, hanu yasa ya taɓata yace "umma"
ameesha ɗauke kai tayi daga kallonshi, da sauri ya kalli ameesha yace "me yasa baki gayamin ba kika tafi?"
idanunta da suka rikiɗe suka koma jajur ta kalleshi dasu, batayi magana ba yace "ba magana nake miki ba?"
murmushin da yafi kuka ciwo tayi sannan ta tashi tana gyarawa umma drip ɗin, fita zatayi ya rike hanunta, tace "sakarmin hannu"
yace "ba zan sake ba saikin faɗamin meyasa baki fadamin ba kika tafi?"
juyowa tayi tazo har gabanshi ta tsaya, cikin idonshi ta kalla sannan s fusace tace "ban faɗa maka ba? kana can kana meeting shine zan faɗa maka? kana can kana zuwa gidansu manal kana yin late shine zaka samu daman zuwa wani waje me amfani...."
cikin tsawa yace "shout up meesha, kina bibiyana kina zargina ne kenan?"
tace "ba bibiyanka nake ba"
yace "bibiyana kike mana baki yadda dani ba"
Imran yace "yaya, meesha dan Allah kuyi hakuri karku fara haka"
share hawaye tayi tace "yaushe zanje ina bibiyan wanda yake bibiyan wata"
cikin zafin rai ya juyo da ita yace "meesha ban bibiyi kowa ba kisan me zaki faɗi"
"shiyasa aka baka manager?"
cikin tsawa yace "ban karɓa saboda so na ba"
tace "bakaso shiyasa ka karɓi kayan babanta kasa?"
cikin zafin rai ya nunata da yatsa yace "meesha ki iya bakinki"
itama ranta yana tafasa tace "idan naki fa? zaka dakeni ne?"
dunƙule hanu yayi ta matso tana hawaye tace "dakeni mana, dakeni Man"
hanunshi daya dunkule ta warware hanun ta fara marin fuskanta dashi tace "da dukan kayimin zanfi jin sauki akan naje kiranka kazo umma babu lafiya kace bakada lokaci"
a fusace cikin tsawan da yasa umma ta gama buɗe idonta jin abinda yake faruwa kamar a mafarki yace "karya kike yi"
ba ita kaɗai ba har Anty dasu fahad saida suka kalleshi, a fusace ta fita daga ɗakin ta turo kofan gauu, umma tace "me nakeji haka man? wa kake yiwa tsawa?"
shiru yayi tace "wa kake yiwa tsawa nace?"
baiyi magana ba tace "in dai ameesha ce kasan ba zan karɓa ba ko? wannan yarinyar data shigo rayuwarku itace takeso ta fara haɗaku faɗa?"
yace "ammi babu fa ruwan manal a wannan faɗan...."
cikin tsawa tace "ka rufemin baki, nifa dama kallo ɗaya na yiwa yarinyar naji na tsaneta, to tun wuri ka san abinyi ko ka aje aikin ka fita a harkan yarinyar ko kuma kasan yadda zaka rinƙa lallaɓa ameesha ta yadda ranta ba zai rinka ɓaci ba"
shiru yayi tace "jeka bata hakuri"
a hankali ya juya ya fita, tana zaune a waje ta haɗa kai da gwiwa tayi shiru, a gefenta ya zauna ya jingina kanshi da bango yayi shiru shima, sun jima a haka kafin yace "am sorry"
bata ɗago kai ba tace "ba komai bazan iya fushi da kai ba, amma inaso ka faɗamin gaskiya"
hanunta ya rike ya fara irga mata duk abinda ya faru, a hankali ta share idonta tace "na sani zuciyata tana faɗamin gaskiya dannewa nake, nasan ba zakayi komai babu dalili ba"
yace "ki yafemin"
a hankali tace "na yafe maka"
yace "you are the best friend a wannan duniyan"
shiru tayi, saide zuciyanta yana zafi kawai dannewa take sabida ga umma babu lafiya kada abin yayi mishi yawa, da haka suka zauna har dare.
washe gari ameesha ce ta tafi gida tayi musu breakfast tazo dashi, tun daga nesa taga motar da take ganin manal a ciki, fitowa tayi daga napep tana rike da flasks ta shiga cikin ɗakin, tsayawa tayi turus ganin manal zaune a kan kujera tana yiwa umma sannu, umma amsawa kawai tayi ta rufe ido kamar me bacci, a hankali ta karasa ciki ta aje flaks ɗin tace "fahad ina man?"
manal cikin murmushin da take mata tace "yaje karɓo magani"
shiru tayi, manal ta kalli umma wacce take ɗauke kai tace "to umma zan tafi Allah ya kara sauki"
umma tace "ameen"
shigowa yayi yace "meesha har kinzo?"
tace "yes"
manal tace "rakani zan tafi"
aje maganin yayi ya rakata, baiji daɗi ba da yaga babu wanda yayi farin ciki da ganinta, ita kanta manal zuciyanta tafasa yake ganin umma sai ɗauke kai take, a hankali tace "family ɗinka basa farin cikin ganina"
yace "no ba haka bane kinsan a asibiti ne kowa baya yanayi me daɗi"
tace "to shikenan tunda kai kana farin ciki idan ka ganni hakan yasa nake jin dadi a raina"
tausayi ta bashi, ta shiga motan yace "kinashan maganinki?"
a hankali tace "eh"
yace "kada kiyi wasa da magani kinji?"
a hankali tace "to"
tafiya tayi yana ɗaga mata hanu, komawa ciki yayi ameesha tana zaune a gefen umma tana cin Irish, zama yayi kusa da ita yasa hanu suka fara ci tare, danne damuwanta tayi ta taɓa gashinshi daya taru tace "yau gashinka yayi yawa sosai"
yace "eh kitso nakeso kimin"
dariya tayi tace "waye zaiwa namiji kitso? wannan gashin naka da uban laushin ina zai kamu"
yace "ai bai kai naki laushi ba"
tace "karya ne"
zame hulan kanta yayi zai taɓa gashinta ta kauce tace "karka taɓamin kai"
ganin haka ya tashi ya zame ribbon ɗin kanta, girgiza kai take tana matsawa nan take gashin ya baraje ya rufe mata fuska saida ya taɓa, ɓata rai tayi tace "nika bayamin gashina umma tamin parking me kyau ka warware"
yace "to kawo na kame miki"
kame mata yayi sukaci gaba da surutu umma dake kwance sai kallonsu take a ranta tace "Allah ka karesu daga kowane sharri"
*Jiddah Ce...✍️*
08144818849
[09/04 à 08:06] JIDDA MAPI: 🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*DUHU DA HASKE*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
Na
*Jiddah S mapi*
*Chapter 15*
~Har dare yana tare dasu su faruk sun tafi sai shi da ammi da manal kawai, tagumi yayi yana tunanin ta yadda zai fara yiwa su umma maganan kuma ba zai ɓoye musu ba sabida kada suzo suji a wani wajen suyi fushi dashi, cikin dare ya turawa ameesha text "kuyi hakuri zan dawo gobe da safe akwai abinda ya taso ne"
tana gani tace "ina fatan lafiya?"
yace "lafiya ƙalau"
daga nan bai kara tura nata text ba itama bata kara ba, ammi tunda tayi salla ta kwanta akan sallayan tana bacci shi kaɗai yake zaune idonshi biyu yana kallon manal dake bacci da oxygen, juyi ta fara zata fizge drip ɗin yayi saurin rike hanunta, a hankali ta buɗe ido jin an rike mata hanu, ido huɗu sukayi tayi mishi alaman ya cire mata oxygen ɗin, cirewa yayi kaɗan, a hankali tace "ka ciremin duka zan iya numfashi da kaina"
murmushi yayi ya cire mata, a hankali tace "ka aureni?"
gyaɗa kai yayi, tace "yanzu kai mijina ne?"
gyaɗa kai yayi, tace "ni matarka?"
ya kuma gyaɗa kai, tace "zan rinƙa ganinka kullum?"
gyaɗa kai yayi idonshi cike da hawaye, tace "zan rungumeka?"
a hankali yace "eh"
rungumeshi tayi ta kankameshi, shima rungumanta yayi tace "na gode, yanzu zaka tafi dani gidanku matsayin matarka?"
a hankali yace "eh"
kallon ammi data tashi tayi tana dariya tace "ammi Abdool ya aureni yanzu ni matarshi ce ni kaɗai yake dashi nice kaɗai zan raɓeshi, zan taɓashi a duk lokacin da naga dama, bayan ni babu wata mace da zatayi hakan ko Abdool?"
gabanshi yayi mummunan faɗuwa tunawa da ameesha, tace "ko?"
da kyar yace "eh"
ganin zata sauka a gadon ya riketa yace "ki nutsu drip ɗin saura kaɗan ya kare"
fizge drip ɗin tayi tace "na warke yanzu bana jin komai mu tafi gida kawai"
ammi tace "manal ya zaki cire drip kinga hanunki yana jini?"
kallon hanun tayi yana jini sosai tace "yes na gani ammi"
man yayi sauri ya rike hanunta yace "kina ganin jini a jikinki?"
tace "ban damu ba da jini ya fito a jikina"
a ranta tace "matukar zan samu biyan bukata ta"
a fili kuma tace "ssbida na saba da hakan"
auduga ya danne wajen dashi jinin ya tsaya, ammi tace "dole sai kin hakura saboda dare yayi zuwa safe saimu tafi"
sauka tayi a gadon tasa takalmi tana jin jiri sosai tace "muje na warke banson kwanan asibiti"
man ya kalli agogo karfe biyu na dare yace "kiyi haƙuri gobe saimu tafi"
tace "no"
ammi zatayi magana yayi mata alaman tayi shiru, shirun tayi ya tashi yace "to shikenan tunda kinaso mu tafi saimu tafi"
cikin jin daɗi ta rungumeshi tace "thank you abdool I love you"
shiru yayi, ammi ta shirya ta ɗau sallayansu kawai da maganin manal already sun biya kuɗin, a motarshi suka shiga suka fara tafiya, shiru motan yayi Abdool yana tunanin yadda zai fara faɗawa su umma hankalinshi a tashe yake, hanunta yaji akan nashi baiyi magana ba har suka isa gidan, yace "ku shiga ni zanje gida sai gobe"
girgiza kai tayi tace "ba zan barka ka tafi a wannan daren ba saide mu tafi tare"
yace "no ki...."
rufe bakinshi tayi tace "nifa matarka ce ko ka manta?"
girgiza kai yayi, tace "muje ko kuma mu kwana anan"
a hankali ya shiga cikin gidan dasu, fitowa yayi tayi mishi sight hug suka shiga ciki, ɗakinta sukaje ta canja kaya zuwa na bacci sannan ta kalleshi tace "wani zai kwana babu kayan bacci yau"
tayi mishi gwalo, murmushi yayi yace "saiki bani naki nasa"
dariya tayi sosai tace "ka taɓa ganin namiji da rigan mata? ai saide mata da rigan maza"
yace "eh fa hakane sabida ameesha kullum kayana take yawan sawa"
ɗip jinta da ganinta suka ɗauke, wani irin kishi taji a ranta a hankali ta juyo tana murmushi tace "ina ganinta ai kuma yana mata kyau"
dariya mara sauti akan fuskarshi da alama idan anyi magananta yana jin daɗi, kwanciya tayi akan gadon ba zato yaji ta ɗaura kanta a cinyarshi tayi shiru, hanunshi ta ɗaura a kan gashinta dake tsantsi, shafawa ya fara a hankali ya jingina bayanshi da jikin gadon yana kallonta har tayi bacci, a hankali ya zameta zai kwantar da ita a gefe yaji ta rikeshi gam taki sakinshi, barinta yayi taci gaba da baccin, wayanshi ya buɗe yana kallon hotunan Ameesha, murmushi yake yi yana kallonta kullum tana cikin dariya ga son wasa kamar yarinya karama, yana kallon hotonsu tare ta turo baki ta shagwaɓe fuska shi kuma yana dariya, yana kallo har bacci ya ɗaukeshi wayar a hanunshi, a hankali ta buɗe ido jin yana numfashi a hankali, kallon kyakkyawan fuskanshi tayi ta shafa sajenshi dake kwance luf, karamin bakinshi me ɗauke da pinkish lips, taga gashin idonshi me tsayi a kwance, gashin kanshi me yawa da kyau da tsanti ta kalla, sai kuma ta kalli kirjinshi dake da faɗi, ta wuyan riganshi daya ɗan sauka tana iya kallon gashin dake kwance a kirjinshi, zame wayan tayi ta yadda ba zaiji ba, hoton ta kalla taga shi da ameesha ne, goge hoton tayi ta kashe wayarshi sannan ta aje a saman gadon, rungumeshi tayi taja blanket ta rufasu dashi, cikin muryan baccin da take ji tace "Abdool nawa ne ni kaɗai, babu macen da zata raɓeshi koma wacece ita"
a haka sukayi bacci Abdool a zaune ita kuma kwance a jikinshi.
washe gari a firgice ya tashi yana salati, gani yayi tana bacci sosai cikin kwanciyan hankali, tunawa yayi da duk abinda ya faru jiya, zameta ya fara daga jikinshi yaji ta rikeshi sosai, cikin sanyin murya tace "good morning"
yace "morning ya kika tashi? ya jikin?"
a hankali ta tashi tayi mishi kiss a gefen kumatu tace "da sauki"
sauka yayi daga gadon yaje toilet yayi alwala yazo ya shinfiɗa sallaya yayi salla, itama taje tayi alwala tazo tayi salla hijabin yayi mata kyau maroon, yana zaune akan sallayan ya rasa da wani ido zai kalli su ameesha ya fara faɗa musu yayi aure a daren jiya?"
a hankali tace "zamu je gidanku? Acan zan zauna?"
jijjiga kai