Showing 9001 words to 12000 words out of 83501 words
yana ci da sauri kafin su Ankara su hanashi, rikewa tayi suka fita Imran ma ya fita, hawa mashin ɗin tayi shima ya hau ya zauna ta mika mishi flaks tace "gashi rike"
hararan kanta yayi yace "ban gane rike ba"
tace "kafi karfin rikewane malam ABDUL-RAHMAN?"
ganin ba zai karɓa ba ta riko hanunshi ta damƙa mishi taja mashin ɗin suka fara tafiya, cikin jin daɗi tace "first time da mace take jan namiji kenan idan zasu je unguwa akan mashin"
yace "ai kece baki yadda na jamu saiki janyo kowa yayi ta kallon mu kawai"
tace "oho dai ai ban taɓa zubar damu a kasa ba"
rankwashi yayi mata a kanta yace "waye ya taɓa zubar damu?"
tace "kai mana"
suna cikin tafiya har suka isa check point, tsaki taja tace "wallahi na tsani check point yanzu zasu ɓata mana lokaci"
shiru yayi yana kallon mashin da kuma layin motoci, yace "my meesha?"
tace "yes"
yace "watarana zanso na siya mana mota mu rinƙa yawo dake muma mu zama masu kuɗi"
tace "ni kuma banson hakan"
yace "sabida me?"
da mamaki sosai akan fuskanshi yayi mata tambayan, tace "sabida idan ka samu kuɗi harma ka siya mota zaka iya daina jirana mu fita unguwa tare, idan kayi kuɗi zaka iya mantawa dani ni kuma ba zanso haka ba, rayuwarmu a haka yafi min daɗi, dani da kai da Imran da kuma farhan ga mama ga kuma umma muna rayuwa cikin nishaɗi duk da bamuda kuɗi hakan baisa munyi rayuwa cikin kunci ba, sabida mu muke bawa kanmu farin ciki, duk abinda zai tarwatsa wannan abota na tsawon shakera da shekaru wanda ya fara tun akan Abba ba zanso shi ba, kasan kai kaɗai ne abokina bansan kowa ba banida kawa banida sai kai, daga kai sai Imran sai farhan kune abokaina, har mutane suna cewa ni bana yin abu irin na mata kullum ina cikin maza, harma bana iyasa riga da skirt na sake a ciki nafi gane riga da wando kaga ai ba zanso mu rabu ba koda na second ɗaya ne, yanzu ma aikin da zamuje nema nima da takadduna saimu nemi aiki iri ɗaya ko?"
jin yayi shiru tace "ya kayi shiru?"
a hankali yace "koda me na zama a rayuwa bazan taɓa iya mantawa dake ba meesha, dake na saba tun ina yaro kece kusa dani ba zanso abinda zai rabam...."
daidai lokacin taja mashin ɗin suka tafi an basu hanya, manal dake zaune a cikin motarta ta sauke glass sabida batason zufa ya ɓata mata kwalliya tafison iska yana shiganta, ɗan yaye mayafinta tayi ganin an basu hanya taja motar, iska ne ya kwashe mayafin ya fitar waje, da sauri tasa hanu zata rike saide kash mayafin ya riga ya gudu, tsaki taja taji gaba da driving, cikin sanyin murya yace "meesha ai idan mun samu aiki duk problems ɗinsu zamuyi solving domin kuɗi zai rinƙa shigo mana, zan kaiki super market ki siyi duk abinda kikeso da farkon albashina"
tana murmushi ta buɗe baki zatayi magana taga farin mayafi ya rufe mata fuska, waro ido tayi ganin kan mashin ɗin ya suɓuce mata, tangal tangal ta fara dasu man yayi saurin riketa yace "meya faru?"
zuwa yanzu idonta ya rufe sosai da mayafin tambul mashin ɗin yayi suka faɗi kasa, karan azaba tayi jin hanunta kamar baya jikinta, da kyar tace "man kana lafiya"
shima cikin dauriya yace "eh kefa?"
tace "hanuna"
mashin ɗin ya faɗi akansu mutane ne suka ɗaga mashin ɗin suka fara ɗaga man, da sauri ya fara ɗaga ta, cire farin mayafin yayi wanda yake kamshin turare sosai, ya riketa yana goge mata jikinta daya ɓaci da ƙura yace "sannu"
hanunta ta nuna mishi idonta cike da hawaye tace "naji ciwo"
farin mayafin ya ɗaura mata a hanu yace muje chemist"
kwance mayafin tayi ta wurgar a ƙasa tace "wannan mayafin yasa muka kusa rasa rayuwarmu na tsaneshi"
murmushi yayi yace "tunda bamu rasa ba ai bai kamata ki tsana ba"
taka mayafin tayi cikin masifa tace "wallahi da naji kana kareshi sai naji kamar na ƙona"
dariya yayi sosai ya rike hanunta yace "sorry my meesha yanzu bari na kaimu chemist"
tace "a,a muje wajen aikin kada muyi late banji wani ciwo ba"
zaiyi magana tace "mujeeee"
hawa mashin ɗin yayi ta hau bayanshi yaja suka tafi, tana duba address ɗin da aka sanar har suka isa wajen, mutane suka gani dayawa a wajen, ya kalleta itama ta kalleshi, hanunshi ta rike tace "muje"
yace "kinga fa da mutane dayawa"
tace "addu'an samun sa'a zakayi ba wai ka karaya da wuri ba"
a kofa suka zauna kamar yadda mutane suke a zaune, abincin dake kula ta ɗauko da cokali tazo gabanshi ta zauna, kallon kyakkyawan innocent face nashi tayi sannan tace "haaaa"
murmushi yayi yace "meesha banajin yunwa"
tace "ba kaine kace a gida kana jin yunwa ba?"
girgiza kai yayi yace "ke kici sabida nasan bakici komai ba"
shiru tayi ta ɗibo tasa a baki, sannan ta ɗiba ta kai bakinshi, ganin ta ɓata rai yasa ya karɓa yana ci, da haka har suka cinye tace "good bari na kai kan kulan kan mashin"
zazzafan mota ne yayi parking da alama shine me company ɗin, fasa kai flask ɗin tayi ta aje a wajen tana hamdala, saida ya shiga aka buɗe musu suka shigo, fitowa yayi daga motan yana karewa dukansu kallo, Alhaji faisal shine me wannan company cewar wani dake bayansu ameesha, saida ya shiga ciki da jimawa kafin ya aiko a fara kiransu, koda me kiran yazo da alama shine manager ya nuna manal yace "yace ke ki fara zuwa"
kallon man tayi cike da murna tace "muje"
girgiza kai yayi yace "kece akace ba mu ba"
da sauri tace "ai tare nake da kai"
yace "no kije idan yace nazo saina shigo"
jijjiga kai tayi sannan ta wuce cikin tafiyanta me sauri da ɗaukan hankali, sam bata sani ba idan tana tafiyan duk jikinta na girgiza, knocking tayi yace "yees"
shigowa tayi ta tsaya tana murmushinta me kama da dariya domin ta saba da hakan, sosai yake kallonta bata kawo komai ba tace "good day sir"
wajen zama ya nuna mata, cikin sabo da sa riga da wando ta gyara ɗaurin rigan sanyi da tayi a waist zata zauna yace "kwance rigan sanyin"
sam ameesha bata kawo komai a ranta ta riga ta saba dasu Man tana iya ma canja kaya a gabansu saida umma ta hanata take ɗan dainawa wataran, a ganinta kowa ma haka ne normal, ta kwance rigan sanyin, kallon shape nata yake yana lasan baki, ya kalli gaban riganta data rufe da bottle yace "juya"
juyawa tayi, yace "juyo"
juyowa tayi yace "god of creation amma wannan saurayin da kuke tare baisan kayan da yake tare dashi ba ko?"
bata gane ba kawai tayi mishi murmushi, batada kawaye bale tasan irin wannan maganan na batsa ne, yace "da alama yasan darajanki saboda shape da kike dashi, irin wannan kayan dole ya rinƙa zuwa ko ina dake mana sabida kada wani ya taɓa mishi ke"
shiru tayi zuwa yanzu ta fara tsarguwa, ganin kamar batada wayo sosai yace "sau nawa yake yi dake a rana?"
cikin rashin fahimta tace "me?"
cikin iya barikanci yace "s**"
tashi tayi a fusace ta bige kujeran data zauna akai, tace "dama maganan banza ka kirani kamin?"
tashi yayi ya fara matsowa kusa da ita baya baya ta fara tana neman kofa ta buɗe ta gudu, saida ta jingina da jikin kofan ya matso kusa da ita yace "kina nufin wannan kyakkyawan gayen dana ganki dashi baya taɓa wannan tsadadden jikin?"
yayi magana yana kai hanu kirjinshi, bige hanunshi tayi da karfi tace "maaaaaaan"
toshe mata baki yayi da karfi, hanu yasa a gefen cikinta inda tasa belt na wandon yanaso ya kwance, girgiza kai ta fara tana kwace kanta.
Man yana tsaye yaji shaƙuwa yana damunshi da sauri yace "tunda ina shaƙuwa akwai abinda yake faruwa da meesha"
shaƙuwan ya kara karuwa, da sauri ya nufi hanyan zuwa office ɗin, tareshi manager yayi yace "dakata idan oga yana ciki babu me shiga"
tureshi yayi yana shaƙuwa yana karuwa, direct kofan office ɗin yaje ya fara knocking, ganin ba'a buɗe ba ya fara bubbugawa da karfi
"meesha? meesha?"
jin tayi shiru yayi baya da karfi yazo ya buga kofan da jikinshi, kara komawa baya yayi ya kara bugawa nan take kofa ya ɓalle waro manyan idanunshi yayi ganin suna kokawa, cikin zafin nama yaje ya janyeshi, maruka ya fara wankeshi dasu, dukanshi ya fara yana cewa "meesha kake yiwa haka?"
cikin zafin rai yace "kasan wacece ita a wajena?"
dukan da yake mishi ya fara bawa Ameesha tsoro karfa ya kasheshi, da gudu taje bayanshi ta rungumeshi tana cewa "mu tafi ka kyaleshi haka"
cikin zafin rai da tsananin huci ya wankeshi da marin da yasa hancinshi ya fara jini, man yanada karfi sosai tafi kowa sanin hakan domin bayason faɗa ko marin mutum yayi zai iya ji mishi ciwo, yace "macen da zata iya sadaukar da farin cikinta sabida wasu kake nema kaci mutuncinta? ameesha dake sona fiyeda yadda take son kanta kake yiwa haka? babbar kawata da banida kamar ta a duniya kake yiwa haka?"
kuka ta fara tace "dan Allah ka kyaleshi"
ganin ba zai kyaleshi ba ya ɗaga hanu zai kara ɗukanshi tace "ya isa Abdool"
cak ya tsaya bai karasa da hanun jikinshi ba, dunƙule hanun yayi ya fesar da Iskan bakinshi, a hankali ta fashe da kuka ta faɗa jikinshi, rungumeta yayi tsam yana shafa bayanta, a hankali yace "shiiii"
jin sautin kukanta kamar ana zuba mishi wuta a zuciya, hanunta ya rike suka fita daga wajen, hawa mashin yayi itama ta hau, shiru sukayi suna tafiya.
ranta a ɓace ta isa wajen taron domin mayafinta daya faɗi ya bata haushi abin, fitowa tayi daga motar tana taku tamkar ɗawisu, kallon mutanen dake wajen tayi komai ya tsaru da kyau, waje ta samu ta zauna tana ɗagawa Ammi da dady hanu, nan aka fara gudanar da taro manal na zauna tana bin kowa da kallo, da haka har aka fara kiran kowa ana basu statement of result nasu tareda iyayensu suna basu kyaututtuka, lokacin da aka iso kan manal duk ƴan matan suka fara hararanta sabida sun tsaneta bata kulasu gata da girman kai da rashin sakewa a wajen mutane, gata da kyau domin duk wajen babu wanda ya kaita kyau a cikinsu, dady ne ya karɓi result ɗin zai mika mata ya haɗa da makulli yace "wannan makullin company ɗinki ne na M.U.M fashion designer, wato manal umar maidawa fashion designer inason kara tallata company ɗinki duk masu buƙatan decoration na kowane event a nemi m.u.m fashion designer"
tafi akayi sosai tareda taya ta murna, sannan ya ɗauko wasu takaddu yace wannan sune takaddun private jet ɗinki wanda nayi miki alkawari tun kina karama"
rungumeshi tayi tana share hawayen farin ciki, ammi ta bata atm tace "wannan atm ɗin account ɗin akwai naira biliyan goma inaso ki zama billionaire ba millionaire ba"
rungumesu tayi dukansu biyu ta karɓi mic cikin murna ta yiwa iyayenta godiya da pure english wanda yasa duk mutanen wajen suka tafa, da haka suka koma wajen zamansu, koda aka tashi dady da Ammi da sauran mutanen suka rakata domin buɗe sabon babban company ɗinta, tun daga kofa tasan dady ba karamin kuɗi ya kashe ba, lokacin da suka shiga ciki saida taji kamar ta haɗiyi dady dan murna, mutane suka tayata murna da kuma fatan alkhairi, cikin jin daɗi suka koma gida, Ammi tana farin cikin ganinta haka tana murna, manal bata sakewa bata dariya koda yaushe fuskanta a ɗaure, bata son wasa tun tana yarinya haka take, wannan yasa ammi take son ganin sun sata farin ciki.
*Jiddah Ce....✍️*
08144818849
[09/04 à 08:05] JIDDA MAPI: 🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*DUHU DA HASKE*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
Na
*Jiddah S mapi*
*Chapter 4*
~A kofan gidansu ameesha ya tsaya itace ta fara sauka sannan shima ya sauko, hanunsu sarke dana juna suka shiga cikin gidan, karamin gidane madaidaici, yana da ɗan kyau irin na masu rufin asiri gini da komai irin na gidansu man ne, wata kyakkyawar mata ce tana da ɗan kiba zaune akan kujera tana gyara farcenta, ganin sun shigo jikinsu a mace taji a ranta yauma babu sa'a kamar kullum basu samu aiki ba saide yau taga yanayinsu ransu a ɓace sosai musamman man, cikin sanyin murya tace "Abdul kuna lafiya?"
a hankali ya jijjiga kai, ganin gashin kanshi a hargitse ta kalli ameesha dake kakalo murmushi da kokarin nuna ba abinda ya faru tace "Ameesha kuna lafiya?"
da sauri tace "eh Unty muna lafiya"
girgiza kai tayi tace "ameesha nice na haifeki nasan halinki da ɓoye damuwa shima Abdul nice na raineshi tun yana jariri kullum yana tare dani nasan ɓacin ranshi kuma nasan farin cikinshi akwai abinda kuke ɓoyemin"
danne kukan da yazo mata tayi sannan ta durkusa kusa da ita ta zuba hannayenta akan cinyarta tace "Anty muna lafiya babu komai"
daga nan ta tashi ta shiga ɗaki, akan kujeran da sukaji jiki kaɗan ta zauna ta kifa kanta a hanun kujeran ta fara kuka, shigowa yayi ya tsaya a bakin kofa ya harɗe hanu a kirji ya zuba mata manyan sexy eye's nashi masu kama dana turawa, ganin kukan yana karuwa ya taka a hankali ya isa inda take, zama yayi a kasa daidai inda ta aje kanta shima ya kwantar da kanshi a wajen yana kallon fuskanta da yake kusa da nashi, cikin kuka zata juyar da kanta yasa hanu ya hanata juyawa shima hawaye ne ya fara wanke mishi fuska, da sauri ta share hawayenta tace "man kukan me kake?"
yace "kin manta munyi alkawarin ba zamu bar ɗaya a cikinmu yayi kuka shi kaɗai ba? kin manta munce zamu rinƙa sharing damuwanmu tare? munsha wahala tun muna yara ƙanana iyayenmu maza suka mutu suka barmu a cikin wannan rayuwan da babu daɗi, bana samun farin ciki idan ban ganki ba, koda rabin awa nayi ban ganki ba sai na kira wayarki naji muryanki nake samun nutsuwa haka kema, kinsan kowane ɗigon hawayenki yanasa zuciyata tana zafi sosai, meyasa kike kuka bayan kin san haka? ba kince ke jaruma bace?"
share mishi hawayen tayi sannan ta share nata, murmushi tayi tace "na daina kuka, ba zan kara kuka ba, kaima ka daina?"
jijjiga mata kai yayi, tace "to yanzu sai ina kuma zamu fara neman aiki?"
ɓata rai yayi yace "ni gaskiya ki daina min maganan neman aikin nan kullum bana hutawa"
jan kumatunshi tayi tace "kaine babba a cikinmu ya zama dole ka nemi aiki domin ka ɗauki duk ɗawainiyanmu idan ka zama me kuɗi ai zamu huta"
yace "ba kince bakya son nayi kuɗi ba?"
tashi tayi tana kwance rigan sanyin dake waist nata tace "no faɗa kawai nake nasan koda wani irin kuɗi kayi ba zaka taɓa mantawa da childhood friend naka kuma babbar kawar ka ba wato Ameeeeeeshaaaaa"
dariya yayi dan yadda take magana kamar karamar yarinya harda ɗaga hanu, ya leka kofa yace "Anti akwai tea?"
daga can zaune tace "akwai amma ku ragewa farhan dan ya kusa dawowa daga makaranta"
yace "to"
wajen da suke aje tea flaks yaje ya ɗauko cup guda biyu ya zuba a ciki, tea sai kamshi yake, ameesha canja kaya tayi zuwa riga dogo na material, cire ribbon tayi ta bazo gashinta baya sannan ta zauna a kasa inda yake zaune akan carpet ɗin ɗakin, ta ɗauki shayin itama ta fara sha, ido ta zuba mishi yace "what?"
girgiza kai tayi tace "nothing"
cigaba sukayi da shan shayin har suka gama yace "muje mu ɗauko fahad a school"
tace "ka manta wannan rakwaɓaɓɓen motar taka ta ɓaci?"
yace "a kafa zamuje saimu biya school nasu Imran mu dawo tare"
tashi tayi tasa hijabi dogo ta fesa turaren da Anty ta siya mata sannan tazo wajenshi tace "kaima bari na fesa maka"
fesa mishi tayi yana murmushi yace "kinason kamshi"
aje turaren tayi tace "kamar yadda kake so ba?"
fita sukayi a tare suna hira cikin farin ciki kamar babu abinda ya faru, yace "Anty bari muje school mu ɗauko fahad kafin nan an tashi wasu Imran saimu ɗaukoshi"
tace "to shikenan ku kula sosai Allah ya tsare"
Ameen suka amsa a tare, binsu tayi da kallo a ranta tace "suna warware matsalarsu tare, ya Allah kada ka karesu daga kowane sharri"
tafiya suke akan titi suna hira man yana dariya domin ameesha tana bashi labari, dama idan kanaso kaga yana dariya to saide idan suna tare da ameesha saɓanin haka mugun miskili ne, baya magana kuma baya sakewa da mutune, sun iso dab lokacin da aka tashi wasu fahad, kyakkyawan yaro ne fahad yana kama sosai da yayarshi ameesha ba zai wuce 12years ba yana ganinsu yazo da gudu ya faɗa jikin man yace "yeeee ya Abdul yau nasan zaka siyamin ice cream ɗin can"
nuna mishi me ice cream yayi, waro ido man yayi sanin baida ko sisi a aljihunshi, zaiyi magana ameesha tace "ai gashi ma ya bani kuɗin da zan siya maka dashi"
nuna mishi ɗari biyar na hanunta tayi da mamaki man ya kalleta sai kuma yayi magana a kunnenta ta yadda fahad ba zaiji ba yace "aina kika samu kuɗi?"
a kunnenshi itama tayi magana cikin raɗa tace "a jakan umma ɗazu na sace"
waro ido yayi fahad yace "muje to"
zuwa sukayi suka siyi na 500 aka basu guda huɗu karɓa tayi tana sha shima man yana shan nashi fahad ma haka, rike ɗayan tayi wa Imran, saida suka shanye suka tafi zuwa school ɗinsu Imran, a lokacin aka tashi musu sabida secondary suke, yana ganinsu farin ciki ya kasa ɓuya a fuskanshi, ameesha tace "guess what?"
taɓe baki yayi alaman bai sani ba, ta ciro hanunta data ɓoye a hijabi tace "ice cream for you"
cikin jin daɗi ya karɓa yana mata godiya, sha zai fara ta karɓe