Showing 63001 words to 66000 words out of 83501 words
tace "akan wannan gold digger kake yiwa ummanka tsawa kake marin kaninka? yaushe ka zama butulu ne man?"
kwace hanunshi yayi yace "kece gold digger ameesha, ashe kina kishi da manal shiyasa kika danneta umma ta sareta tanaso ta kasheta"
murmushin da yafi kuka ciwo tayi kana tace "kishi? kishi fa kace, akan wannan zanyi kishin?"
manal gefe ganin tana mishi tsawa tace "ya isheki haka"
cikin fushi ta wani shaƙe wuyan manal ɗin tana huci, kakarin mutuwa manal ta fara, tace "dake nake magana? nace dake nake magana? da wanda ya ajeki nake magana"
fizgeta man yayi ya juyo da ita da karfi, yace "to saiki kasheni ni ba ita ba"
tace "man sakarmin hannu"
yace "bazan sakeki ba, toma ina magana da family ɗina me yasa bakinki ciki?"
tace "abinda yasa wannan matar taka ciki shi ya sani ciki butulu kawai..."
cikin ɓacin rai yace "karki kara kirana da butulu"
tace "na faɗa butulu butulu butul...."
marin daya ɗauketa dashi saida ta faɗi kasa kusa da Imran, dafa kunci tayi har gefen fuskanta yayi jaaa, Imran yace "kada ka kara sa hanunka koda wasa ka taɓa ta"
matsowa yayi kusa da ameesha yace "idan na kara fa?"
yace "zan rama mata"
mari ya kuma ɗauketa dashi, Imran ya wankeshi da maruka har uku a jere, duka ya fara kaiwa Imran shima cikin ɓacin rai ya fara ramawa, umma ihu tayi tace "ameesha zasu kashe kansu"
ameesha jan Imran ta fara ita kuma manal tana jan man, da kyar suka raba su, bakin Imran yana jini yace "mugu mara imani"
zai yi magana manal tace "dan Allah kayi shiru, na yadda zan bar gidan ka sakeni kawai zan tafi dan Allah kuyi hakuri ku daina hakan"
tana magana tana hawaye, kallon kyakkyawan fuskanta yayi sannan ya share mata hawayen yace "babu inda zakije ke kaɗai ina tare dake tare zamu tafi"
jan hanunta yayi zuwa ɗaki, duk suna tsaye a wajen har ya tattara kayansu duk ya zuba a akwati yasa mata hijabi ya ɗau duk wani abinshi me amfani yaja hanun manal suka fito tare yana jan akwatin, Anty sai a lokacin ta shigo duk abinda sukeyi taji kuma ta gani, fahad yana gefenta, manal tana kuka tana cewa "me kakeyi haka abdool family ɗinka nefa wannan bakada kamar su"
baiyi magana ba saida ya tsaya a gaban umma dasu yace "tunda bakwa sonta ni ina santa zan bar muku gidan kafin kun kasheta"
jan hanunta yayi umma tace "Abdulrahman karka tafi ka barni, dan Allah ka dawo"
kallon Anty da fahad yayi, fahad wani kallon tsana yake aika mishi, baiyi magana ba yaja manal dake kuka, jikinta duk jini, saida ya fita ta juya baya tana kallonsu, murmushi tayi musu sannan ta bishi, a mota yasa kayansu yace "shiga"
shiga tayi yaja da karfi ya bar kofan gidan, asibiti ya fara kaita akayi dressing ciwon jinin ya tsaya amma taji rauni sosai, riketa yayi tana takakawa da kyar ganin haka kawai ya ɗauketa ya kaita motan, tana iya hango wani yanayi da yake ciki na tashin hankali me wuyan fassara"
kakkarya sim ɗinshi yayi ya watsar a wajen kafin yaja motan suka tafi, tace "gidanmu zamuje?"
girgiza kai yayi, tace "to ina zamuje?"
yace "barin garin zamuyi"
da sauri yace "kenan zan tafi na bar ammi? ka manta komai namu yana wannan garin? ka manta company ɗinmu anan yake? ka manta anan ƴan uwanka da ammina suke? muje gidanmu tunda zamu iya zama acan"
girgiza kai yayi yaci gaba da driving yana hawaye, haɗa kai tayi da gwiwa a hankali ta fara raira kuka, gani tayi ya juya kan motar ya nufi hanyan gidansu, da sauri tace "zamu koma gidanmu?"
gyaɗa kai yayi, tace "na gode Abdool"
a compound yayi parking kana ya zagayo ya ɗauketa yace a shigo mishi da akwatin, tana rungume a kirjinshi ya shiga da ita ciki, knocking yayi sannan yayi sallama, ammi tana jin muryanshi tace "Abdool bismilla"
shiga yayi da murmushi akan fuskanta tace "Abdool kaine..."
turus ta tsaya ganin manal kwance a hanunshi jikinta duk ya ɓaci da jini, da sauri ta karaso tace "meya sameta?"
cikin ɗacin rai zaiyi magana manal tace "yanzu ba lokacin magana bane"
kasa daurewa yayi saida ya faɗawa ammi abinda ya faru, dafa kirji tayi tace "Innalillahi wa inna ilaihiraji'un, yanzu ka dawomin da ita gida ba? na gode tunda ka dawomin da ita da rai"
kwantar da ita yayi akan sofa yace "mun dawo tare alkawari nayi zan kula da ita ba zan taɓa barinta ba"
ammi tace "na gode Abdool".
umma jikinta yana rawa ta fara jin kamar zata faɗi, da kyar ta iya magana a hankali ta yadda babu wanda ya iya jinta bakinta yayi nauyi idonta ya rufe tana ganin duhu tace "ameesha Imran ku rikeni zan faɗi..."
kafin ta karasa maganan ta zube a kasa, a firgice ameesha da Imran sukayo kanta suna kiran sunanta "umma? umma?"
Imran ya fara bubbugata da karfi yace "umma dan Allah ki tashi karki tafi ki barmu, kinga ya man ya tafi ya barmu yabi ta kema tafiya zakiyi ki barmu?"
ganin bata tashi ba kawai ya kalli ameesha wacce ta kasa motsi sai rarraba ido take cike da tashin hankali, ji tayi Imran ya rungumeta ya kankameta sosai ya fashe da kuka, da kyar ta iya ɗaga hanu ta ɗaura akanshi ta shafa sumanshi daya hargitse tsaban tashin hankali, bata iya tayi magana ba kawai ta zameshi daga jikinta fita tayi daga gidan babu ko takalmi a kafarta, a haukace take gudu akan titin, Allah ne ya kaita wani chemist lafiya, ta shiga da gudu tana haƙi ta kasa magana sai nunawa me chemist ɗin hanyan gida take, me chemist yace "wai meya faru ameesha kiyi magana mana"
da kyar tace "ka...ka...taimakemu umma ta faɗi bata numfashi"
da sauri yace "subhanallah muje"
fita sukayi suka nufi gidan, Imran ne ya ɗagata ya kaita ɗaki yana tsaye a kusa da gadon yana kai kawo, umma kwance flat bata motsi, fahad da Anty sai kuka suke, shigowa sukayi ameesha tace "gata can"
dubata ya fara yana gwaje gwaje, kasa tsayuwa Imran yayi a hankali yaje gaban ameesha ya tsaya yana kallonta, taɓe baki yayi wani kukan yana kara zuwa mishi, a hankali ta janyoshi jikinta tana tapping bayanshi tace "shiiii ya isa ka daina kukan haka ya isa zata samu lafiya"
cikin sanyin jiki dr ya tashi ya kalli ameesha da sauri tace "menene?"
yace "akwai babban matsala"
Ameesha jikinta yana rawa tace "na me?"
yace "ɓarin jikinta ɗaya ba zai kara aiki ba, ba zata kara iya tafiya ba".
_Jiddah Ce...✍️_
08144818849
[09/04 à 08:06] JIDDA MAPI: 🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*DUHU DA HASKE*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸
Na
*Jiddah S mapi*
*Chapter 17*
~Waje Ameesha ta samu ta zauna domin jiri take ji, Imran yayi shiru shima ya zauna yayi tagumi, sautin kukan Anty ya karu fahad ma kukan yake.
"kuyi hakuri kowa da ƙaddaran da Allah ya ƙaddara mishi, zan baku shawara ku rinƙa bata magani akan lokaci sannan ku siya mata wheelchair ta yadda zataji sauƙin rayuwa babu tafiya"
hawaye ameesha ta share tace "babu wani taimako da zamu samu ta fara tafiya?"
yace "gaskiya babu ko ina zakuje ta riga ta kamu ba zata iya tafiya ba"
shiru sukayi, zai tafi ameesha ta ciro kuɗi a aljihu ta bashi, yace "a,a ki barshi Allah ya bata lafiya"
tafiya yayi, Imran ya ɗaura kanshi akan cikin umma yayi shiru, duk wajen babu wanda ya kara magana.
Abdool kula ya fara bata da ciwon ya hana ammi yi mata komai shi yake mata, duk abinda yasan zai sata farin ciki yinshi yake, tana samun farin ciki saide kullum idan sun kwanta da dare sai taji yana kuka ƙasa ƙasa, wannan kukan da yake ne yake taɓa mata zuciya, saide ta rungumeshi ta rinƙa taping bayanshi da haka yake samun sauki ya rage kukan har yayi bacci.
Ameesha ce take kula da umma su Imran suna zuwa school ta hanasu zaman gida, ta kwashe duk kayansu umma dana Imran sun mayar gidansu, makulli tasa ta kulle gidan sannan ta bawa Imran makullin tace "kun dawo gidanmu da zama daga yau,
acan zamufi samun sauƙin kula da umma tunda muna da yawa gani ga Anty ga fahad kuma gaka, idan kun tafi school na tafi wajen aiki Anty zata kula da ita"
ya karɓi makullin yace "to"
tafiya sukeyi akan mashin nata har suka isa gidan, umma tana zaune akan wheelchair da ameesha ta siya mata, tana ganinsu tayi murmushi ameesha ta karaso ta zauna akan cinyarta ta rungumeta, tace "umma kin fara samun sauki gashi har kin daina ramewa"
cikin maganan ta da baya fita tace "eh ameesha kulawanku ne yasa hakan na gode sosai"
murmushi tayi bata kara magana ba, Anty ta kawo musu abinci tace "to lokacin cin abinci yayi sai a sauko ko?"
sauka tayi daga ƙafan umma ta ɗau abincin ta fara bata, saida ta koshi ta bata magani, tare dasu Imran suka zauna suna cin abincin, umma tayi tagumi tana kallonsu, har yau basu dawo normal ba dauriya kawai suke yi, haɗa ido sukayi da ameesha tayi mata murmushi kawai,
washe gari akan mashin nata ta kaisu Imran school kafin ta wuce wajen aikinta, saide ta tarar da mummunan labari me company ɗinsu ya rasu, tun a ranan aka rufe company, jikinta a mace ta koma gida, koda ta shiga umma tana zaune a waje ɗaya kamar kullum, zama tayi a kasa kusa da ita ta ɗaura kanta a cinyar umma, hawaye masu zafi ya zubo mata, bata damu data share ba, umma ce ta ɗaga hanunta mai aiki ta fara share mata hawayen tana mata alaman kada tayi kuka, a hankali tace "umma komai yana daɗa lalacewa, numbern man baya shiga naso na kira miki shi kullum wayanshi a kashe, naje company ɗinsu ance basa zuwa daga shi har manal ɗin, duk inda nasan muna zuwa tare zan ganshi naje dan na sanar mishi rashin lafiyanki ban ganshi ba, sannan yau me company ɗinmu ya mutu an rufe company, ɗan kuɗin da nake samu ina siya miki magani muna cin abinci a ciki aina zan samu?"
kuka take yi sosai, umma sai shafa kanta take, da sauri ta ɗago kai ta share hawayen tace "ba komai ni ameesha zan kara neman wani aikin, ai niba raguwa bace ko umma?"
a hankali ta gyaɗa mata kai, murmushi tayi tana gyara fuskanta tace "nayi alkawarin zan kula dake har karshen rayuwata zan rinƙa siya miki magani har Allah yasa ki samu sauki, sannan ki kwantar da hankali man zai zo watarana kinji?"
jijjiga kai tayi, Anty tace "kin sata a gaba kuna kuka kin manta batada lafiya ne?"
tace "mun daina ai yanzu dariya zan sata"
dariya umma tayi itama ameesha tayi dariya, da dare bayan kowa ya kwanta tayi shiru tana zaune tana kallon umma suna bacci, sam bacci yaki ɗaukant, a hankali ta sauka daga gadon ta buɗe drower cikin sanɗa ta ciro hotonansu da man, fita tayi daga ɗakin ta koma falo ta zauna, kallon hoton take tana hawaye tace "rana ɗaya ka tafi ka barmu baka kara juyowa ba, na kira wayarka a kashe inaso na faɗa maka umma batada lafiya sosai"
Imran dake tsaye a kanta yayi gyaran murya da sauri ta ɓoye hoton tace "Imran bakayi bacci bane?"
saida ya zauna a gefenta yace "banyi bacci ba, taya zanyi bacci yayata idonta biyu tana tunanin mutumin daya tafi ya barmu?"
tace "bafa tunaninshi nake ba kawai de ina kallon hoto ne"
yace "tunanin mutum yake sawa a kalli hotonshi, nasan kinyi kewan babban abokinki da wuya ki manta shi, amma ki sani shifa bai damu ba, yana can yana tareda matarshi hala ma yanzu suna can suna romancing juna, ke kuma kinzo kina tunani, idan har munason ganin ya Abdool saide muje gidansu manal, sabida an tabbatarmin suna can da zama, saide ni bana bukatan ganinshi idan ke zakije bismilla"
da sauri tace "a'a babu inda zanje, tunda naji inda yake hankalina ya kwanta amma ba zanje ba Imran"
hanu ya mika mata yace "alkawari"
sarke yatsanta tayi cikin nashi tace "alkawari"
karɓan hoton yayi yace "good night jeki kwanta"
a hankali ta tashi ta tafi ɗaki, ba karamin daɗi taji ba da taji yana gidansu manal koba komai tasan inda yake, Imran tunda jimawa yasan Abdool yana gidansu manal yaki faɗa mata ne kawai dan yaga babu amfanin Abdool ɗin yanzu a wajenta, saide yaga bata bacci da alama tunanin inda yake takeyi, hakan yasa ya faɗa mata domin ta fara bacci kada ta kamu da depression, kwanciya yayi a falon yayi bacci.
yau tsawon wata biyar kenan babu man suma suna rayuwa basu damu da gashinshi ba, ameesha ce sanye da dogon riga jallabiya na mata, tayi kyau sosai tana shirya musu abincin rana tace "duk ku fito an gama"
shiga ciki tayi ta janyo umma daga kan wheelchair tana turata tace "umma yau nayi abinci me daɗi"
murmushin karfin hali umma takeyi amma yau tana jin jikinta sosai, su Imran sun fito suka fara cin abincin da Anty sai hira suke cikin nishaɗi, akan cinyan umma ta zauna kamar yadda ta saba ta fara jansu akan wheelchair tana turasu tare tana dariya a koda yaushe idan tayi hakan tana jin farin ciki mara misali, saida ta gama juyasu Imran yace "abincinku fa yana sanyi"
sauka tayi ta kawota wajen abincin ta zuba mata ta fara bata, a hankali Imran yayi mata raɗa a kunne "masu siyan gidan sun turo kuɗin na basu takaddun"
cikin ɓoyewa su umma maganan ta jijjiga kai sannan taci gaba da bawa umma abinci, saida ta gama tace "Imran zo muje mu siyo pure water"
da sauri ya tashi yace "to"
fita sukayi tace "kuɗin sun cika?"
yace "eh"
idonta cike da hawaye tace "yanzu Imran saida muka saida gidanku? nace maka mu saida namu amma kaki yadda idan umma taji ba zataji daɗi ba"
yace "Ameesha ya zama dole ne mu saida gidan zamu siya mata magani zamu kaita asibiti domin ina ganin yadda take runtse ido a koda yaushe tana jin ciwo, faɗa mana ne kawai batayi dan tadan babu kuɗi, bakya aiki, gashi abinci ya kare, kuɗin school fees namu zamu biya sabida har sun fara kori, ya zamuyi?"
share hawaye tayi tace muje mu siyo pure water mu dawo kada hankalinta ya kai wani abin, tare sukaje suna tafiya tana sharan hawaye yana bata hakuri har sukaje suka siyo, dawowa sukayi manal rike da ledan ruwan Imran kuma ya rike ledan kayan miya da suka siya, gani sukayi Anty tana kuka tana girgiza umma amma bata motsi, wurgi ameesha tayi da ledan shima Imran ya wurgar, tare sukaje suna girgizata "umma umma ki tashi"
a hankali ta buɗe ido ta kallesu cikin ciwo, da kyar tace "Abdulrahman"
ameesha cikin tashin hankali tace "umma" buɗe idonta ta kara yi cikin ciwo ta rike hanun Ameesha tace "Abdool kiramin shi"
da sauri tace "zanje na kira miki shi ki buɗe ido kinji? na miki alkwari zanje na kira miki shi"
a kiɗime tace "Imran kira napep"
da gudu ya fita zuwa kiran napep tare suka ɗagata suka shigar da ita napep suka shiga ameesha babu takalmi shima Imran haka, asibitin world care suka kaita, a hanya tana magana a hankali, Ameesha saida ta kai kunnenta wajen bakinta taji tace "Ameesha Abdool"
tace "zanje na nemo miki shi yau na miki alkwari umma"
suna shiga asibitin bakinta ya rufe bata kara magana ba sai kallon ameesha take, Imran yana damƙe da hanunta, emergency aka karɓeta Imran da ameesha hanunsu a cikin nata a hankali suka zame hanun lokacin da zasu shiga da ita, Imran ya zauna yayi shiru, ameesha tace "zanje na kira man, ka kula da kowa anan kaji?"
yace "ko zamuje tare?"
girgiza kai tayi tace "ka zauna ka kula dasu zanje kuma insha Allah zamu zo tare jikin umma yafi na kullum tsanani Imran ya zama dole naje na kira abdool"
Imran cikin yadda da magananta shima ya cire rai yau da umma yace "Allah ya tsareki ki dawo da wuri idan kina wuri kowa yafi samun karfin gwiwa"
jijjiga kai tayi
da wani irin gudu ta fita a asibitin mashin ta shiga ta faɗa mishi inda zai kaita.
manal tana zaune akan sofa tayi shiru ta ɗaga kanta sama tana kallon p.o.p na saman ɗakin, wando ne me taushi a jikinta da riga baƙi me guntu, tayi parking gashinta ta saki a bayanta, sosai tayi kyau ta kara zama fara sal, Abdool ne ya fito daga ɗaki yayi kyau shima cikin armless da gajeren wando baƙi, kallonta yayi yaga tayi shiru gaba ɗaya tana zama shiru a rayuwarta, rashin magana da take yi yake sata yawan ciwo a zuciya, idan tayi magana dashi kaɗan sai taga kamar tayi hira sosai, a hankali ya kwanta akan sofan da take ya ɗaura kanshi a cinyarta yayi shiru shima yana kallon saman ɗakin, kallonshi tayi tace "ka fito?"
jijjiga kai yayi yace "kina nan bakici komai ba kuma kin san bake kaɗai bace"
zatayi magana ya tashi yaje fridge ya ɗauko fruits yazo ya zauna kusa da ita ya fara bata, ture hanunshi tayi tace "na koshi"
yace "no banso baby na ta zauna da yunwa a cikinki"
dariya tayi tace "wai a kaina aka fara ciki ne honey?"
ya kara kaiwa bakinta yace "kici sabida ki haifomin kyakkyawan baby me kama dake, itama ta zama kamar balarabiya"
ammi ce ta shigo sanye da leshi fari tayi kyau, Ameesha tace "ammi wai nikam da gaske ina kama da larabawa?"
dum dum kirjin ammi yake duka, da sauri tace "A,a bakya kama dasu dani kike kama"
murmushi tayi tace "ammi ko lokacin da nake karama ance ina kama da larabawa a time ɗin saina fara tunanin waye balarabe a cikin ke da kuma dady, kuma akwai ranan da naje kai zane wani