Showing 66001 words to 69000 words out of 175038 words

Chapter 23 - KASUWANCINA BOOK COMPLETE BY ASMA BAFFA.doc

25 Sep 2025

6866

yace Sameera kece How u?longest time,tace am great ina ta so mu hadu wlh amma ba dama tun aurenka na farko fa gaskiya mun dade.

Wani kishi da bacin rai ya taso min na bata rai nayi kicin kicin na tashi hankalina gaba daya ina Harare harare,itace second wife din naka? Ina Yarima yana dariya yace yana lfy yar duniya kin buya amma dai kin sake aure yanzu ko? a'a aure ai sai na huta ina aiki ina samun kudina matsalar maza ta isheni baku da kirki Sam ni sai na huta zan yi Insha'allah,Jin bata da aure yasa na kara fusata na daure fuska na dawo gaban Aayan na juya bayana tare da kwantar da jikina a jikinsa muna facing juna da Sameera sai kallon Banza nake mata,Hannunsa na jawo guda biyun na sakalosu ta kafaduna ina wasa da yatsunsa,Murmushi Sameera tayi tare da cewa am sorry to say Aayan kasan bana boye abinda ke raina amma wannan tayi maka yarinya da yawa Aayan kamarka da auren kamar wannan da gani ma baza ta wuce 15yrs ba,ga mata a gari zunduma zunduma da ka fada mana ai da mun zabo maka manyan yara amma irin wannan ai kuruciya zaka sha baza kaji dadinsu ba.

Dariya sukayi gaba daya tare da wani tafawa abinda ya bani haushi kenan ya kara kuleni mene nasa na tafawa da mace,nan take naga fa ta fada min baka zata barni da takaici ban san sanda nace uhm Allah sarki kuma a hakan bashi da kamata dan ina masa abinda Babba bata isa tayi masa ba,tunda tsab nake daukeshi wanda nasan ko uwarki yafi karfin.....kafin na karasa yasa tafin hannunsa ya rufe min baki da karfi dan yasan sai na karasa ko za a mutu sai na rama,ina so na kwace baki na amma yaki Sakina ya toshe min da tafin hannunsa yana fada min a kunne kina magana wlh yau na lahira sai ya fiki jin dadi bakya jin magana ko ke ba a isa an miki abu kin hakura ba sai kice sai kin rama wannan wacce magana ce ta marasa kunya uwarta fa kika ce,Sameera ta kalleni sosai tace da Sameera kike zance yarinya zaki san kin zagi uwata,wlh sai kin San wa kika cewa haka,Allah ya taimakeki yanzu Kinci darajar Mijinki amma a sannu zan goge miki abinda ke kanki,Bakina na kwace nace Ba Sameera ba Allah yasa kece Sameeran Gaya>?#? wlh nafi karfinki kina magana kina cijewa ke ga yar daba karewar Daba munga Amana ta Alim ma=?
? Sameera dama irin Masu takama da yan daba ne har yara ne da ita yan daba,bata da kunya duk abinda taga dama haka zata fadawa mutum shi yasa ko zaman aure bata iya yi,sabo da ko yaushe a shirin daba take kana mata zata sa yara yan daba suyi ma kaca kaca tana takama da kudi sabo da ubanta ita kadai ya haifa ya rasu ya bar mata dukiya me tarin yawa,Tun kafin ya mutu ya raba gado yaba yan uwansa ya barwa yarsa komai,shi yasa take abinda taga dama,kuma bata San mutunci ba duk inda take da kai zata iya ci ma mutunci ta ko wanne hanya,Aayan kuwa Business ne ya hadasu tsakanin Company nata da nasa tun da dadewa.

Ni kuwa nace komai dabancinki baza ki bude min ido ba kiyi duk abinda zakiyi nima baki San ko ni wace ba shi yasa har kike magana dani haka ina kyaleki,ki Bari watarana Business ya hadamu anan zaki gane true color dina,Tsaki taja ta bar wajen a fusace,Aayan yana ta kallon yanda nake tsiwa yar ficika dani gaban sangamemiya irin Sameera ko tsoro bana ji,na kalleshi nace girma ya fadi wlh ka ba dani ina ma kallon Ustaz har wani hannu kake hadawa da yan tasha,da gani wannan yar tasha ce gaka da fyallelliyar budurwa me zaka ji a hannun wannan me suffar mazan, kayi dacen mata amma baka godewa Allah kana wani rikewa wata hannu bayan ga hannun da zaka samu lada Allah kyauta ka daina irin wannan a gabana dan wlh ni bazan dauki a wulakantani ba dan baka darajani ba Sam,ka zubar min da mutunci ace Namiji yana da kamata yana rike hannun wata banza,wannan babban matsalace dole na tuntubi kaina Ashe ma ban kai mace ba.

Yana jina ina ta masifa kamar uwarsa yana dariya a ransa,yace to yi hakuri masifaffiya tunda bakya so na daina,wai nice budurwa shi baya daukana a budurwa Sam,yace wai ke nan budurwa ce? Bacin rai ya kamani sai na danne a fili nace a'a kwaila ce,a na dinga masa masifa ina zan rama zaka San ba budurwa bace ni daga yau na Canja salo again na fasa wannan Business din da mukace za muyi wani zanyi daban sai na sa kayi nadama har ni za a wulakanta dan anga ina biyayya ina cusa kaina ina kokari naga an zauna lfy shike nan za a gani,dariya yayi yace a'a dan Allah tsokanarki nakeyi fa muyi Business dinmu zan biya kudin,nace anki din sai na rama nima.

Mun gama siyayyar komai yasa aka kai boot din mota ya biya muka fito kenan sai ga Ameer da Khaleel tare da wasu yan mata masu suffar karuwai sai chewgum suke taunawa su a dole manyan yara,na kalli Aayan na bata rai nace kalli Meenat a gabanmu tsaya kaga abinda sukeyi kalli,ya kuwa kalla sosai ni kuwa wai dan kar ya kalli yan mata nayi masa wayo,Muna zuwa Ameer sai kallona yakeyi zasu shiga mu kuma zamu fito na bi ta tsakiyar yan matan nan a hankali yanda zasu ji nace yan iska sun dauko yan iska su a dole yan mata ana yaye baki a titi na wuce fit na koma kusa da Aayan,Khaleel ya fusata kwarai da maganata haka yan matan ma,Ameer kuwa so yasa baya ganin laifina sai dai ma birgeshi da nakeyi aransa ma cewa yayi wannan gaskiya kika fada Mufeedata tabbas yan iska ne suka dauko yan iska Allah ya baki basira tare da saurin ganewa>?#?

Yan matan zasu zageni Ameer yace wlh duk wacce ta fadi ko bakar magana a kaina sai ya mata illa har fada suka so yi da Khaleel..
Muna shiga mota na tuna zanyi girki kuma kayan miyarmu ya kare nace Aayan kayan miya na manta,Yace to mu koma store din nace a'a danyi gaba wajen yar kasuwar can zamu samu.
Muna zuwa yayi parking nace sai ya fito munje tare,yace a'a nifa ban taba siyan abu a kasuwa ko gefen hanya ba a store nake siya,Na fara rokonsa dole haka ya fito muka karasa wajensu,sabo da tattalina da son kudi nace Malam kwano nawa nawa? Aayan yace nidai a zuba kawai mu tafi,nace a'a so kake ayi mana tsada bazai yuwu ba yo ni akan barkono kwano daya idan nazo sarowa Basai na yini a wajen ba ana ciniki ba kuma karshe kaga na siya arahar banza,Dariya Aayan yayi yace yini guda fa? Nace Cass ma kuwa, Agogon Dubu biyu ina siyoshi a Dari biyu da hamsim ni highest Dari biyar zan siyi shege,ka dinga zuwa dani siyayya kaga araha,Aayan kallona kawai yake yana dariya,Nace kai me kayan miya kwanon tattasan ne dari biyar a garin gaba gaba muke da zan siya haka,yace gaskiyar magana Dari hudu da hamsim baya tsada bana nawa kike so a siyar miki,Nace to ka rage,nafa San kan kasuwar nan,Aayan yace Haba Ke kuwa har kwano guda Dari hudu da hamsim kacal a kasa siya mene na tsada a nan? Harara na watsa masa tare da dan zungurinsa nayi masa magana a hankali bana son haka ba a yiwa yan kasuwa haka,zaka kashe min ciniki idan kasan haka zaka min ka koma mota yanzu duk ragi ai ragi ne,Aayan yace Malam zuba mana kwano biyar ga kudin ya zaro kudi ya mika,na fara rigima na cumimiye a jikinsa baza a biya ba kwano har Dari biyar gwara Ku tafi gida ni Ku barni a nan nayi cinikin ko Dari hudu na siya sai na samu Dari Dari ta Zama tawa,na dawo a taxi, ko kulani baiyi ba yace to tumatir fa,nace a tsaya ni zan Zaba da kaina,me kayan miya yana ta dariya yace kudi kudi ne ga gwalagwaje wanda ya gama lugwiguwicewa daf yake da rubewa kudinsa daban,ga masu kyau manya da kanana,nayi layin marar kyau gwalagwajen nace duk tumatir tumatir ne tunda dafashi za ayi mu sharbe miya Malam ga me sauki ba sai anyi asarar kudin ba a bamu wannan,Aayan dariya ta kamashi ta gaske ya dinga yi yace wlh baki isa ba gwara da Allah ya kawoni na gani dama abinda kike sawa muna ci kenan? Nace to sau nawa ka shanye miyar sa kana Santi ai ni in kaga lafiyayyan tumatir a fridge to na cin salat ne,ai ko harda kwalla Aayan yake dariya ni kuwa ko a jikina,yace Allah na gode ma da na gani da Ido na shi yasa Ashe ba kya yarda a bawa kowa yayi cefane sai ke Ashe Guba kike bamu muna ci.

Aayan yace Malam me kyau wanda yafi kowanne tsada zaka zuba, na hangame baki ina jimami shike nan za a ci kudinmu a banza,akan dan tumatir har yan Dubu Dubu na fitowa naji kamar na fisge kudin,na bata rai ina ta fushi nace ai gwara ni ka bani na dinga tara ma kudin watarana sai mu dakko a siyi abu me amfani dasu amma wlh wannan Almubazzaranci ne, mukaje layin Albasa nan ma dan yaga yanda zanyi yace zabi da hannunki one by one ki dinga zubawa a ledar mu gani,me Albasa yace ai kwano kwano muke saida wa,Aayan yace bari ta Zaba sai a auna zan biya ko nawa ne,aiko na fara Zaba sai na duba wacce ta tsage ko ta kusa lalacewa ko marar kyau sai na dauka na nunawa me kayan miya nace kaga dai wannan araha zata yi ehe,wannan ma ba me tsada bace,Aayan yana murmushi yace pick the nice one mana,na kai hannuna kan me kyau sai na koma na faki idonsa na jefa marar kyan a leda yana kallona yana dariya har na gama sannan yace to Malam juye wacce ta bari bata Zaba ba su zamu siya,haka aka auna ina gani kamar na fashe sabo da ni kudin da aka kashe kawai nake jin haushi da an tattala su ai sai a moresu watarana Rayuwar Manage na iya a haka na taso da ita na saba.

Na dauko shima ya dauki wasu muka zuba a mota ina ta harararsa yana kallona ta gefen Ido yace daga yau tsinke baza ki kara siyowa da kanki ba da kaina zan siyo ko na bayar a siyo,nace girkin ma ba sai kayi abinka ba,wlh ya kamata ka koyi adani sabo da rayuwa ni gaskiya nake fada ma.Maeesha dama suna gani sun San halina sun San yanda nakeyi a kasuwa dariya suma sukeyi Meenat tace Yaya Aayan ya kaga mutuniyar taka ta iya Zabe ko?

Dama kadan yake jira ya dinga dariya yace ai naga Zahiri yau Meenat,haka takeyi ko a gida Ammah ta dinga ta mata fada amma baza ta ji ba cewar Ma'eesha.
Meenat tace ai baka San abin haushi bama shi yasa bama Rakata kasuwa watarana akan egusi da zamu siya wlh sai da muka yini a table din me egusi har fada sukayi ya koremu gaba daya,kai ai kadan ka sani, turmi ma ba a cin arziki a gidanmu ko daka wasu sukayi a ciki sai ka biya ashirin, haka gugan Rijiya ma ko kurar Ciro guga duk na haya ne hhhhh Aayan ya dinga dariya Meenat suna ta bashi labari suna min dariya,sai da na saki Kuka sannan sukayi shuru.
Haka ma Ya Aayan watarana ta siyo min jakar makaranta me kyau ina ta murna wata kawarta Nawwara tace gaskiya jakar tayi kyau nima zan siyo aiko Mufee na jin haka tace Dari uku na siyo ta bani Uku da hamsim na siyar miki,ina kuka haka ta siyar da jakar nan taci ribar Hamsim,Aayan yana driving yana dariya.

Malamin Hajja ya hado mata muggunan da za a sa min tare da Aayan a abinci,da sauran wasu iri iri na wajen Malamai shi yasa yanzu ta saka rigima wai Daddy ya fadawa Aayan a dawo damu ai muma jikokinta ne taga abinda tayi bai dace ba bata kyauta ba
Daddy yasan ba gaskiya bane amma yasan Allah na nan ba matsala ya Sanarwa Aayan.









AsmaBaffa
[1/16, 5:51 PM] Asmabaffa:
KASUWANCI NA







66-70






Official







By
AsmaBaffa







JANNAT wannan page naki ne.


Godiya gareku House of Hausa Noveld kun iya Sharhi.




















Bayan yayi parking a cikin gidan fitowa mukayi tare da jidar kayan muna kaiwa muna dawowa har muka kwashe komai ya rufe motar take away na abinci da ya siya mana na karba ina ta masa godiya da addua ya wuce abinsa nima na shiga Bedroom dinmu, Bayan munci mun koshi wanka nayi na shirya cikin sabuwar Nighty dina iya cinya me siririn hannu peach color na fito fes ina kamshi Meent ce ta shigo Sis kije inji Ya Aayan amma fa yana compound jikin motarsa da alama fita zaiyi,Hijab nasa har kasa kamar zai ja kasa na fita lokacin tuni munyi sallar Isha,saman Motar na ganshi a zaune cikin kana nan kaya ba karamin kyau yayi ba,wani abu ya tsirga min na tsinci kaina cikin wani yanayi na shauki wanda bazai misaltu ba wani dadi yana ratsani, kallona yake cike da tsantsan nishadi kwance a?????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????? fuskarsa zuciyarsa cike take da farin ciki wani Sanyi na ratsashi.

Ina murmushi na karasa tare da cewa au akace fita zakayi kuma naga ka zauna saman bayan mota,yana murmushi yace zance fa nazo kinyi sabon saurayi kuma kina wani cewa fita dariya nayi nace kaima dai baka rabo da tsokana a haka zubin mugaye gareka, am serious ni fa zance nazo dama gori kike min kece kullum kike zuwa zance,Dariya nayi nace to nan gaba idan zaka zo ka dinga bugo waya sabo da ai banyi kwalliyar zuwa wajen saurayi ba na fada kamar gaske, muryarsa naji yace duk fa cikin business ne ki daina tunanin da gaske ne kudi za a biya ki wannan fitowar ma da kikayi kin ci kudade masu yawa,dadi ya kamani nace an gama ko kalma daya ce duk kudi ne? Yace of course, murmushi nayi tare da gyara tsaiwata yana sama na matsa jikin kafafunsa, yace yan mata suna na Aayan duk da cewa baki tambaya ba,ban san lokacin dana fara dariya ba ni abin ma kunya ya bani amma na daure nace ai yanzu gashi ka fada, yaci gaba da tunda na ganki kika shiga raina naji bazan iya bari ki wuce ba batare da na miko Kokon Barata ba gareki, uhmm nace tare da tunani sannan nace kasan me ni ban iya so farar daya ba dole sai mun zauna da mutum idan naga halayensa sun min sai na yarda amma yanzu bazan amince ba, sama naji yayi dani ya daudarani saman motar nima kusa dashi jikinmu na gugan juna,baki na bude tare da cewa wannan saurayine ko dan Shan minti ne kawai,dariya yayi ai an daura mana aure da Budurwar kawai bata sona ne shine nake zuwa zance sabo da na lallabata.
Murmushi nayi nace to naji game din tayi kyau back to our business nawa na samu? Yace ai Dari biyar kika samu sabo da kin kasa magana baki fadi kalamai masu sanyi ba taya zaki samu kudi.

Masu Zafi zan fada yanzu ma kuwa na irin fuske ba wasa nace look in to my eye aiko ya kalla da mayun idonsa I was kidding u but u I knew I love u,i wish I can show u how much I love u,i care for u,my heart is full wth ur love my Prince, yana murmushi yace proof what u have just said, nan take da gaske nakeyin kalamai na ni, bana karya bane amma a boye a raina nace na samu Damar jin dadi na sai na fake da kudin,a fili kuwa sai na ce ka tabbata zan samu kudin nan da yawa,kai ya daga min tare da kara matsowa jikina sosai yatsunsa ya sarke da nawa tare da jawo ni jikinsa, hannayena na sakalo ta wuyansa a hankali na rungumeshi a jikina sannan na dago kaina tare da shigar da bakina cikin nasa ya fara tsotsa kamar ba gobe, tunawa nayi ko yan aiki na zirga zirga a wurin nace yan aiki fa?yace ai basa kwana a nan gidan da safe suke zuwa nemi kudinki na Business yarinya,dariya nayi a raina nace Ina ta masa wayo ya kasa ganewa,nace ni dai mu koma bedroom,lallai kudi zaki nemo da yawa karfa ki karar min da dukiyata,ina dariya nace hau dani baya wannan ni zan baka kudin cikin nawa ka cire Dubu guda,baki isa ba sai dai na daukeki,nace ni dai baya nake son hawa,ko baka da karfi ne? Hannu yasa ya daga ni sama sosai kamar ya dauki tsinke ya dauri a kafadarsa naga ya mai Dani bayansa kamar yar jaririya,nace kai karfinka yayi yawa amma a haka dan Lange Lange da kai, murmushi yake har bedroom dinsa karki cire Hijab din, why? Zaki gani ya furta yana dorani saman bed sannan yazo ya daga hijab din tare da shigewa ciki,dariya nayi yanda yake min abubuwa a ciki don tuni ya zare min rigata tare da kashe light, gaba daya ya gama haukatani ni kaina abinda nake masa ba a cikin hankalina nakeyi ba, ba komai a jikinmu haka muke murzar juna, kalamai yake sabo da sucking na fara masa ko gidan ubanwa na koya oho wannan abu kamar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login