Showing 1 words to 3000 words out of 85238 words
Chapter 1 - Tambarin Talaka Part 1 Complete Hausa Novel By Maryam Obama.txt
[12/10, 22:01] Maryam Muhammad Fkb Hausa Novels Kd: 💅 TAMBARIN TALAKA 💅
1to5
https://www.facebook.com/Maryam-Obam-Novels-441847396162695/
Alhmdlh godiya ya tabbata ga Allah wanda ya sake bani daman rubuta wannan labarin bayan na kammala "SAINA AURESHI" Allah ka bani ikon gama wannan littafin lafiya dan alfarman annabi Muhammad (S A W)
PLZ BANDA YAWAN KORAFI BANCE KAR AMUN GYARA BA, BUT IN ZA'AYI GYARAN AYI TA HANYAR DAYA DACE PLZ👏
Gida ne ginin kasa wani wajan ya rufta, an rufe da buhu, saman kwanan ya tsofe duk yayi tsatsa, kana ganin gidan kasan lallai talauci yana cikin gidan dumu2, dan haka na shiga gidan in dauko muku bayani dakyau, daki uku ne a cikin Gidan, ciki da falo guda biyu,sai wani karamin daki, dakunan duk ba wasu girma garesu ba, jin gunjin kuka a karamin dakin yasa na le'ka, wata yarinya da bazata wuce shekara goma sha bakwai ba, naga Tana kuka tare da shesheka, fara ce amma saboda wahala farin nata ya boye, Tana kukan ne rike da cikinta domin yunwa take ji, kaman zata mutu,wata mata ta leko dakin ta Saki baki tare da fadin au kuka kikeyi sai kace wanda aka bigeki, jar uba, shiga dakin tayi ta cakumi wuyan yarinyar Tana fadin bari inci ubanki sai kiyi kukan da hujja, matsiyaciya, dukanta takeyi tako ina, yarinyar na fadin dan Allah inna tani kiyi hakuri,amma Tani ko a jikinta domin hakurin da take bata kaman ma Kara zugata takeyi, saida ta mata lilis ta tabbatar data daku sannan ta barta Tana fadin yar iskan yarinya kinzo kina kuka a daki, maza ki fito kije ki siyomin garin tuwo, kuma wlh idan kika dade sai jikinki ya kuma gaya miki, dakyar ta tashi jiki babu kwari ta amshi kudin sannan ta fita, bata wani dadeba ta dawo, tani ta watsa mata harara tare da fadin maza kije ki hadamin huta kafin yan sa ido suce bana baki abinci, ta amsa da toh, ta nufi murhun, wata mata ta fito daka dayan dakin Tana fadin wlh tani kiji tsoran Allah, yarinya bata miki komai ba kullum ki kamata ki jibga, anya tani kina tuna mutuwa kuw...... Dallah dakata munafuka ke har kin isa ki dinga shiga sabga ta wlh ahir dinki, ni nafi karfinki wlh, kuma karki manta a karkashina kike domin nan gida nane, matar tace gidanki ko gidan marayu? Nan Suka dunga gayama juna magana ita dai indo tuwo ta daura amma ji take kaman a tsakiyan kanta suke wannan ihun,..... Wacece Indo?
WACECE INDO
Mlm aminu shine mahaifin indo, mazaunin taraba ne a karaman hukuman karan lamido, fulani ne na taraba, yana da mata daya maryam, mlm aminu talaka ne bashi da kudi, domin nanin takalmi yakeyi, gidansu gidan kasa ne,duk da talaucin shi, gidanshi Alhmdlh suna ci koda babu dadi ciki zai dauka, domin mlm Aminu yace TAMBARIN TALAKA CIKINSA, koda ba'a sami tuwo ba za'asha fura ko gari,cikin farin ciki, Mlm Aminu suna zaune da kanin shi a gidansa mai suna musa, yana da mata tani, tana da yara biyu mata, bintalo tayi aure sai abu, Sa'ar indo, tani azabbar Mace ce domin sai abunda tace ma musa yakeyi, ita kuma maryam Tana da hakuri sosai sai yasa mijinta ke sonta, yaran mlm Aminu biyu, yusuf wanda saida ya shekara biyar kafin aka haifi aysha indo, wanda suke kira da indo, aysha tun Tana jaririya take dakyau gata fara sol, Tana da shekara 7 a duniya mahifinsu ya rasu, tun daka lokacin rayuwa ya canza musu, musa ya kanaye gidan duk da bashi da Gado domin Yusuf ya musu katanga, wannan abun yasa Mlm musa tsanan maryam da yaranta musamman ma Yusuf, maryam tun rasuwan mijinta take ta fama da ciwo sosai, wata rana Tana zaune da yusuf da indo a daki bata jin dadin jikinta, ta kalli yusuf wanda ya kusa gama secondary, tace yusufa dan Allah koda bayan raina inaso ka kula Min da indo karka bari tayi maraici domin bata da kowa sai kai, Yusuf jikinshi yayi sanyi yama kasa magana yana sauraranta idonshi ya kada yana zubar da hawaye, itama indo duk da batayi wani wayau ba ganin halinda suke ciki yasa itama ta nutsu Tana hawaye, maryam taci gaba da fadin yusufa duk rintsi ka kulan min da ita karka bari tayi zaman kadaici ka zame mata uwa da uba, domin bata da kowa sai kai, ni nasan ciwan nan bazai barni ba, naso inyi tsawan rayuwa dan in kasance daku, amma bana jin hakan zata faru, Tana zuwa nan ta fara hawaye taci gaba da fadin sannan inaso kabar indo tayi karatu dan Allah domin tayi alfahari da kanta wata rana,rayuwan Mace kalilan ne, Tana fadin haka ta kamo hannun yusuf dana indo ta rike tana murmushi, lokaci daya bakinta yayi motsi Tace ga garinku nan, Allah ya mata rasuwa, Yusuf da indo sunsha kuka sosai har tani ta tausaya masu, haka rayuwa ta kasance musu tun daka lokacin rikonsu ya dawo hannun kanin babansu mlm musa da Matar shi tani, mlm musa ya kane naye gidan ya zama nasa, dan haka ya kullama Yusuf shairi kan cewa yana neman kanwarsa, mai gari ya kori Yusuf daka garin kan cewa duk sanda ya sake zuwa sai an kashe shi, wannan ne sanadin barin Yusuf garin mlm musa da tani Suka kanai naye gida Suka sa yar haya mai suna jamila, tana tausaya ma indo sosai sai dai babu yanda ta iya, tani taci gaba da musguna ma indo bata zuwa islamiya balle boko sai daukar ma tani tallan kayan sana'a yau tani tayi wannan gobe tayi wancan kuma idan Indo bata saida ba sunanta sorry, domin ranan sai taci duka sosai, kuma ta hanata abinci, mlm musa idan ya dawo shima ya kara mata wannan shine rayuwan Indo.....
Taku Maryam obam😘
[13/10, 22:52] Maryam Muhammad Fkb Hausa Novels Kd: 💅 TAMBARIN TALAKA 💅
NA
MARYAM ALHASSAN DAN'IYA
5to10
https://www.facebook.com/Maryam-Obam-Novels-441847396162695/
Indo ta kammala tuwan ta kwashe sannan ta daura miyan kuka, bata jima ba, ta kammala miyar koriya shar dan ban tunanin ansa manja a ciki, dakin tani ta nufa da sallama, kaman dai kullum tani bata amsa ba dan haka tace inna na gama, tani tace toh dan uwarki a bakin kofar zaki tsaya ba zaki shigo ki Kawo min ba? Cikin sauri ta bude bakin labulan daya canza kala daka fari zuwa milk colour, ta Shiga jiki a sanyaye bayan ta ajiye ta dan tsaya ko zata bata nata, tani tace uban Me kike jira kuma mayya mai bakin hali, Ai yau tunda kika ja wancan bakar matar tamin tujara wlh baza kici wannan abincin ba , ta sakar mata rankwashi mai zafi tare da fadin fitar min a daki kar ki tasar min y'a, simi2 ta fice hannunta nakanta Tana hawaye dan taji zafin rankwashin sosai, dakinta ta shiga ta kwanta akan tabarman ta, kuka takeyi Tana fadin yusufa dan Allah kazo ka tafi Dani tun kafin inna tani ta kashe ni, duk da inda Tana yarinya lokacin da mamanta ta rasu ta rike wasu abu, musamman burin mahaifiyarsu na indo tayi boko, amma gashi babu islama balle boko, duk da itama indon tana so amma babu dama dan tani fur tace talla zata dinga mata domin kan indo bana boko bane, na daukan kayan tallah ne, haka indo ta kwana da yunwa duk da baccin da tayi rabi da rabi ne domin yunwa ga yunwan dare bashi da hankali amma duk nacinta haka tabar indo,
Washe Gari tunda asuba indo ta fara share tsakar gidan wanda babu suminti sai 'Kasa, duk da garin bai gama haske ba, domin tani tace indai ta fito batai shara ba sai taci ubanta sai yasa takeyi daka ta idar da sallah, bayan ta gama sharan ta dauki bokiti domin dibo ruwa a rijiya, gidan da take dibo ruwan basu tashi ba dan yar kofar kyauran nasu a rufe yake dan haka ta nufi rafi domin ta dibo rafin akwai nisa sosai kuma yawanci maza Suka fi zuwa, domin yan iskan garin anan suke taruwa in Suka ga mace har fyade suke mata, haka indo ta nufi rafin dan tasan indai ta koma tani taga babu ruwa toh kashinta ya bushe , Allah ya taimaketa bata ga kowa ba harta gama diba, sannan ta fara hada kayan wanke2 a lokacin tani ta fito Tana hamma kaman za taci mutum, gefen murhu ta kalla sannan ta kalli indo tare da fadin amma ke ko matsiyaciya yanzu murhun ma baki hada ba, dan iskanci, indo tace kiyi hakuri inna So nake idan na gama wanke2 in hada, tani tace au yanzu har sai kin gama wanke2 bayan Kin san abu bata da juriyan yunwa, wlh kafin in fito daka bayi ki hada murhun nan, indo da sauri ta nufi murhun Tana hadawa bata dadeba wutan ya kama danma itacen busashene, tani ta fito daka bayi ganin wutan naci tace maza ki daura ruwan kunu tunda kullum ke sai an fada miki, Daura tukunya tayi,tare da hada kayan wanke2 Tana cikin yi abu ta fito Tana fadin tani an gama kunun? Tani tace ina fah wannan mai idon kaman na mayu ta tsaya bata lokaci kuma tasan sarai bakya jure yunwa, Abu tace wlh tani laifinki ne aida kinci ubanta nidai yanzu yunwa nakeji gaskiya, tani ta tashi ta nufi indo wai dan uwarki ba zaki duba ruwan koya tafasa ba, Indo jiki na rawa ta tashi dan kar tasha duka ga yunwa Tana ji, bude tukunyan tayi ruwan yana alaman tafasa, ta kalli tani tace inna yanzu zaiy....kafin ta karasa taji saukan mari ke wace irin yar iska ce, kunu tun dazu kin kasa gamawa, bayan kin san sarai abu bata da hakurin yunwa shegiya mai bakin hali, dakikiya komai sai anyi ta nanata miki, bakya daukan komai, indo data rike fuska dan zafi ta nufi tukunyar dan taga alaman ya tafasa, daukan ruwan tayi ta juye a kunun tare da rufewa, tani ta dauki kunun tayi daki dashi ,indo taci gaba da wanke wankenta, duk wannan abunda akeyi jamila na daki Tana ji amma babu yanda ta iya, bayan indo ta gama aikinta ta nufi dakin tani tare da fadin inna na gama, mlm musa yayi tsaki tare da fadin wannan yarinya ko mayya naso ace itama ta mutu tabi iyayenta matsiyaciya ita dai kanta na kasa dan bata san yana ciki Bama, tace ina wuni abba, yace ni ba abbanki bane ki kirani da musa na, mara mutunci kawai, tani ta tura mata kunu dan kadan a kofi tare da fadin gashi mayya dan nasan danshi kikeyi, indo ta amsa tare da fita daka dakin tunda ta kafe kanta a kofin saida ta shanye kunun sannan ta ajiye, jinta take kaman bata sha komai ba, domin kunun dan kadan ne, Tana zaune a dakinta tani ta bude dan kyauren Tana fadin au ba zaki zo ki fere rogon ba, indo tashi tayi tani ta kai mata rankwashi akai, tare da fadin mayya kawai, indo fere rogon take tayi, sannan ta daka, bayan ta daka ta dauko karamin abun nikansu na dutse, haka ta dinga nikawa yana laushi sannan ta kwashe tasa wani, bayanta da hannunta babu abunda yake sai ciwo kaman zata mutu dan azaba domin bayanta yayi mugun rikewa, ga rogon da yawa, bayan ta kammala tani ta fito ta hada tare da mummulawa harta gama sannan ta kirga tace ma indo ta soya, bayan ta gama suya tani tace na dubu biyu da dari hudu da ishirin ne wlh ki tabbata kin dawo mun da kudina dai2 sannan karki dawo min gidan nan in baki siyar ba, indo ta amsa da toh sannan ta dauki buta dan ta wanke Jikinta tani tayi saurin cewa ajiye min buta uban me za kiyi dashi? Indo tace zan wanke jiki nane, tani ta tabe baki tare da fadin dama kinzo kin wuce dan banga amfanin wanke jikin ki ba, haka ta ajiye butan ta fita, hanyar tasha ta nufa domin tasan anan zata fi saurin yin ciniki wata mota ce ta danno da gudu indo garin saurin ta matsa wainar rogo ta kife a kasa.......
Taku maryam obam😘
[14/10, 20:53] Maryam Muhammad Fkb Hausa Novels Kd: 💅 TAMBARIN TALAKA 💅
NA
MARYAM ALHASSAN DAN'IYA
10to15
https://www.facebook.com/Maryam-Obam-Novels-441847396162695/
DEDICATED DIS PAGE TO AYSHER HUYMERAH LIKYMO❤
Indo kuka ta Saki Tana kallo ganin babu komai a roban domin duka ya zube a kasa, gashi mai motan bai tsaya ba, yara ne Suka fara wawa suna diba, indo ta tashi Tana kuka Tana kora yaran idan tabi wannan ya gudu wani ya dawo haka Suka maidata kaman mahaukaciya, ganin yaran Sun kwashe duk da kuwa akwai kasa a kai yasa indo zama a gefen titi Tana kuka kaman wacce akace mamanta ta mutu, duk wanda yaga yanda take kuka saiya tausawa mata, sai dai kuma duk masu tausaya mata babu wanda zai iya biyan kudin domin kowa nata kanshi, duk wanda yaji abunda ya faru sai dai yace mata Allah ya kyauta ko kuma yace yara basa duba hanya sai suyi ta sako kai bakin titi, indo saboda tashin hankali yasa ko yunwa bata ji duk da kuwa ta diba lokaci mai tsawo a wajan Tana kuka, domin bata ma tunanin Zuwa gida, dan tasan yau in taje gida kwananta ya kare domin tani kasheta za tayi, indo ta tsine ma mai motan nan yakai sau dubu tare da fadin ko waye wannan ya cuceta
Tani keta faman surfa ashar Tana fadin wlh yau saina ci uban wannan yarinyar yanzu har an kira magrib bata dawoba, kai wannan ko yar iska, kullum sai ta Sani surutu yau zanyi maganinta wlh saina nuna mata ni tani bani da imani wlh, abu tace yoo tani bakece kike Raga mata ba, sai yasa ta raina ki ba, inda kina dukanta kullum kaman sau goma a rana aida tabar miki iskanci, Tani tace kin san gidan akwai yan tsurku masu jira ayi suyi ta yayata ka, kaman ka kashe mutum ko an Kama ka da kato, abu tace tani yasin mu kori wannan jamilan munafuka ce, rannan fah da kika fita har daba indo abinci tayi ina daki ina ji, Tana cewa tayi sauri taci Kafin ki dawo, tani tace bura uba yaushe akai hakan shine baki fada min ba, abu tace rannan mana, tani ta tashi fuuu tayi kofar jamila ta fara fadin fito bakar munafuka, jamila dake daki duk Tana jin abunda suke fada,ta fito Tana fadin karki balla min kofa wlh tani ki fita a idona, tani tace jar uba, ni kike fadama haka toh wlh yau sai kin kwashe kayanki kin bar min gida, bakar munafuka, jamila tayi dariya tace saiki dawo min da kudin hayan dana baki, nan tani tayi shuru domin ta rasge kudi, ganin tani tayi shuru yasa jamila fadin wlh tani kiji tsoran Allah yarinyar nan marainiya ce, bakya jin tsoran hakkinta ya kamaki duk kin kanai naye dukiyar su keda Mi...... Dallah yimin shuru ina ruwanki wlh jamila ki fita daka idona wlh ni da kaina ina tsoran kaina wlh karki hasala ni wlh idan baki fita daka idona ba saina maidaki abun tausayi, jamila tayi murmushin takaici tare da fadin wlh tani ina guje miki hakkin yarinyar nan ya kamaki amma tunda kince haka kije kiyi tayi kema Ai kin haifa, tani tace toh mai bakin baki babu abunda zan gani Dani da yarana sai alkhairi, nan tani taita zagin jamila ganin haka yasa jamila ta koma daki tare da fadin kudinsu na karewa zasu bar gidan dama mijinta tun tuni yake cewa su tashi amma tace ita tafi son zaman nan, yaso ta bishi cikin taraba inda yake aiki tace a'a, amma wannan karan zata bishi ko kuma su canza Gida.
Wani makeken gida ne, naga motoci nata shiga, nima dai nace bari inje inga mai akeyi a ciki, motoci sunkai talatin a cikin gidan daka ganin alama taro akeyi a cikin gidan, dan haka nima na kusa kai, wani katon falo na gani fadan tsaruwan falon bata lokaci ne, jin magana nayi kasa2 dan haka na nufi inda nake jiyo maganan, subhanallah wani hadaddan Guy na gani kaman balaraban kasar dubai, wannan daka ganin shi ya hada jini da larabawa, daka gani meeting sukeyi, sun dauki wajan 30mnt sannan mutanan Suka fara fita, wannan Guy din na gani ya tashi ya haura sama wani naga ya bishi yana fadin majeed yaushe zamu je wajan mum ta kirani yakai sau goma, Majeed ya tsaya tare da kallon shi yana fadin kai, abdul wlh kana takura min tun dazu kake min mita ka bari in huta mana, yana fadin haka ya nufi wani daki, bedroom ne dakin babba ne komai na dakin brown ne yayi kyau sosai, rage kayan jikinshi ya fara yi, sannan ya shiga toilet, yayi wajan 30mnt sannan ya fito yana goge gashin kanshi da towel, saida ya gyara gashin nashi sannan yasa wata jallabiya ya kwanta, wayanshi yaga yana haske, tsaki yayi tare da daukan wayan lokaci daya yayi murmushi ganin sunan Mum ne a jikin screen din wayan, dauka yayi tare da fadin Mum cikin shagwaba yake magana, tace son kai nake ta jira, yace Mum am so tired wlh sai yanzu muka gama meeting, ga surutun abdul, Mum tace kai son Abdul dinne yake da surutu, yace eh Mum dazu fah muna hanyar zuwa nan wata yarinya tazo zata shiga mu kuma mun zo wucewa shine ta zubar da kayan kanta, shine wai mu tsaya a biyata, dan na hana