Showing 3001 words to 6000 words out of 85238 words
Chapter 2 - Tambarin Talaka Part 1 Complete Hausa Novel By Maryam Obama.txt
driver shine yake ta surutu, Mum tace son ai gaskiya abdul yake fada maka, kaida na sanka da tausayi aiko bakai bane sila ya kamata ka tsaya ku bata kudin asaran da tayi , ganin Mum din kaman itama tana supporting Abdul yasa yace Mum bari in huta anjima zan shigo, murmushi kawai tayi tare da fadin sai kazo......... ku biyo ni domin jin waye majeed
Taku maryam obam😘
💅 TAMBARIN TALAKA 💅
NA
MARYAM ALHASSAN DAN'IYA
15to20
https://www.facebook.com/Maryam-Obam-Novels-441847396162695/
Abdul-majeed d'ane ga governor din Taraba state, mai ci yanzu wanda yake neman kujeran Sanata a halin yanzu, govn Muhammad mutum ne mai tausayi dajin qan na kasa dashi, govn muhd iyayenshi masu kudi ne gaba da baya, ya taso cikin kudi a kasar Egypt yayi karatun sa, inda a nan ya hadu da fatima suka fara soyayya fatima balarabiyar kasar Egypt ce, soyayya suke sosai lokacin da iyayenta Suka sani hankalinsu ya tashi sosai domin basu taba Kawo yarsu zata fada soyayya da wanda badan kasar suba, dakyar iyayenta Suka yarda akayi bikin ganin gudan yar tasu ta nace, haka akai biki na gani da fada, aka kawo fatima Nigeria taraba state,shekaransu biyu da aure Suka haifi abdul Majeed tun yana karami yake dakyau domin sak mahaifiyarshi zaka rantse mahaifinshi ma balarabe ne idan ka ganshi, ga gashi irin na larabawa da yake dashi gwanin ban Sha'awa, tun daka kanshi haiyuwa ya tsayama fatima, duk da abun yana damunta amma mijinta ko a jikinshi ,govn muhd bayan ya gama karatu ya fada siyasa dan abunda ya karanta ma kenan political science, tun daka Chiarman ya fara yaci zabe, yazo dan majalisan taraiya, ganin irin aikin da yake ma Al'umma yasa Suka ce ya fito takaran govn da farko yaki yarda amma ganin magiyan mutane yasa ya yarda cikin ikon Allah kuma ya haye, govn Muhd ya Kawo ci gaba sosai, wanda a yanzu yana neman takaran sanata, A Majeed tun yana yaro iyayenshi suka sangartashi domin shi daya garesu a London yayi karatu kuma a nan ya hadu da yar president mai suna zainab suka Fara soyayya, bayan sun gama karatu Suka dawo suka ci gaba da soyayansu a nan A Majeed yana da taimako da tausayi ga kyauta, bai dade da dawowa ba ya samu appointment daka CVN Central Bank of Nigeria, aka bashi mukamin mataimakin GM tun daka lokacin ya koma abuja da zama, yana yawan zuwa taraba sosai shekaranshi biyu akan mikamin akai bikinsu shida zainab bikin da aka kashe naira kaman babu gobe, Zainab mace ce mai nuna isa da gadara harta masu mata aiki tsoran yi mata laifi suke gata Tana da kishi sosai duk da bawai wani kula da mijin nata take ba, yau Tana can kasar gobe tana wancan kasar duk da abun yana damun A Majeed amma haka yake hakuri domin yana sonta sosai, zainab Tana da Kyau sosai Tana da diri mai kyau uwa uba ga kudi ga babanta president sai yasa take yin abunda take So, ga miji ta samu na nunama tsara domin A majeed namiji ne wanda duk wata Mace za tayi burin samu ga kyau ga kudi ga miskilanci idan kaga yana magana da dariya To shida iyayenshi ne ko abun kaunar shi zainab, amma bai cika magana ba, sai dai akwai kyauta da tausayi,zainab duk wani abu ta samu sai yasa take taka wanda taso, A Majeed yaso su zauna a taraba shida Zainab amma taki gidan daya gina a taraba in yazo a nan yake sauka harta meeting ma in yana Dashi a nan yake yi wani zubin abdul abokin a Majeed ne yaron abokin mahaifinshi ne abdul tare suke aiki a cbn abdul yana jure halin miskilancin A Majeed amma shi bashi da aure wannan kenan.
MUN DAWO KAN LABARI
A Majeed sai wajan 4 ya tashi, toilet ya nufa yayi alwala sallah yayi, sannan ya koma toilet yayi wanka, ya fito yana shiryawa cikin wata riga da wando masu kyan gaske, ya dauki lokaci yana gyara gashin shi, tare dasa Turare kala2, kamshi kawai ke tashi tako ina, kai tsaye ya fito falo abdul ya gani yana cin abinci a takeaway, A Majeed, ya tabe baki tare da fadin yanzu takeaway kake ci ba zaka bari muje gidan Mum ba, Abdul yace sai inyi ta jiranka yunwa ya kashe ni koh? A Majeed ya tabe baki tare da fadin inka ga dama ka fito muje, Abdul tashi yayi yabi bayanshi, A Majeed a baya ya zauna driver yaja motar Suka fita abdul kuma cikin motarshi ya shiga shima ya bisu a baya, kai tsaye wani dangareren gida naga Sun shiga ga sodoji da police makil a wajan gidan, harta cikin gidan ma security ne makil, bayan driver ya faka A Majeed ya fito shima abdul ya bude tashi motar ya fito nan security Suka Fara gaida A Majeed amma ko kallo basu isheshi ba danshi haushin gaisuwan ma yake ji, sai abdul ne ke amsawa, falon gidan yayi Bala'in tsaruwa sosai,wata mata wacce ba zata wuce shekara 45, amma kyan jikinta zaka dauka ba tafi shekara 30 ba, kana kallonta kasan balarabiya ce, Tana zaune akan makeken kujeran falon Tana shan fruit ganin gudan jinin nata yasa ta tashi da sauri tayi hugging dinshi tare da kamo hannunshi ta zaunar Dashi akan kujera kaman wani yaro karami, shi kuma sai kara shagwabe mata yake, abdul dai dariya yakeyi dan inda sabo ya saba da ganin irin son da Mum ke nuna ma dan nata, shi kuma yaita shagwaba kaman dan jariri, Mum tace son ya abuja cikin hausa tayi maganan amma zaka dauka da larabci takeyi, yace Mum lfya, yunwa nake ji, Mum tace tashi muje dinning sai a sannan ta lura da abdul dake ta dariya Mum tace Abdul Ashe tare kuke ban lura ba, ya aiki? Nan ya amsa da lafiya tare da gaida Mum din sannan Suka nufi dinning Mum ce tayi saving dinsu duka, A Majeed cin abincin yake kaman za'a dauke mai,mum kallonshi take tana tausaya mai domin ita dai matarshi bata da lokacin dafa abinci, sai masu aiki wani tym din kuma yaci takeaway indai abinci zaici cikin natsuwa toh yazo taraba ne, bayan Sun kammala Abdul ya mike tare da fadin mum zan koma abuja yanzu, Mum tace Abdul dare zai maka fa, yace wlh Mum ina da aiki sosai gobe, baby Boy ne yasa muka zo taraba wai anan za ayi meeting, A Majeed ya tamke fuska tare da fadin wlh abdul Ka rainani da yawa, kasan ni boss dinka ne wlh idan ka kara cemin Baby boy saina turaka maiduguri course, dariya abdul yayi sosai tare da fadin Mum bari in tafi, mum tace toh ina zuwa danna wani abu tayi kaman remote saiga wata tafito cikin riga da skirt baki kanta babu dan kwali, mum tace Kawo min bucket na dambun nama daya da cake, tace ok your excellence, ba tayi minti uku ba ta Kawo ita da wata, Mum tace Abdul gashi sai kayi taci Allah ya kiyaye hanya, ya amsa da ameen sannan ya Kalli A Majeed daya wani tamke fuska yace A majeed na wuce yace safe journey, sannan ya fita ,nan Mum da dan nata Suka zauna suna ta fira cikin So da kauna.
Indo dai Tana wajan da take Tana kuka, Abdul dake tafiya yaga kaman yarinyar dazu ce,da kayanta ya zube, kaman zai wuce dan bai tabbatar ba, har yayi gaba ya dawo baya, bayan yayi parking ya fito sai yanzu ya gane itace domin roban yana makale a hannunta, yace baiwar Allah lafiya kuwa, bata bashi amsa ba sai kuka da takeyi kanta na mata ciwo, yace ko kurma ce ke, nawa ne kayan naki, cikin sauri ta dago Tana fada mishi, tausayi yaji ta bashi kudin koh 3k bai kai ba, mota ya koma ya dauko 5k ya bata amsa tayi da sauri ko duba yawan kudin ba tayi ba, ta fara fadin ngd tare da rugawa da gudu dan taje gida yana kiranta amma ina tayi nisa.......
Taku maryam obam😘
💅 TAMBARIN TALAKA 💅
NA
MARYAM ALHASSAN DAN'IYA
🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝
Vote me on wattpat @maryam-obam
WWW.maryamobamnovels.com
25to30
DEDICATED DIS PAGE TO...
MRS DAN MALIKI
UWAR GIDA SARAUTAR MATA💑 ALLAH YA KARA MUKU SON JUNA KEDA OGA
YA TSOLE IDON MAKIYA👏
Murmushi yayi tare da fadin ko bakya son insan gidan kune? Kai ta girgiza alaman a'a, yace ok To muje, tace idan aka ganni dakai za'amin fada, yace ok ina ne gidan, tace dan Allah kar kazo wlh idan inna ta ganka sai anyi min duka, shide mamaki take bashi idan ta kira kalman duka, ganin yanda tayi kaman za tayi kuka yasa yace toh shikenan yanzu a ina zan kuma ganin ki? Tace idan na fito tallah, yace shikenan ki gaida gida, sauri ta farayi kaman zata tashi sama, wani yaro dake wasa a wajan amma yana da wayau yace kai kasan yarinyar can?yaron yace eh, nan ya tambaye shi ina ne gidansu, yaron yace muje in nuna maka, nan sulaiman yace suje, indo Kafin ta shiga gida saida tayi canji a chemist tasai Magani sannan tasha ta boye sauran canjin kar tani yau ma tace tabi wani, bayan ta shiga gida babu kowa a tsakar gidan dakin Tani ta shiga ta ganta a kwance, Tani na ganinta ta tashi tare da mika mata hannu, indo ta bata kudin, kirgawa tayi taga sun cika dai2 Tani tace amma yar nan kina da bakin hali, yau shine kika 'ki zuwa wajan da za'ayi miki juye ki samo min sababbin kudi, ita dai indo shuru tayi bata ce komai ba, nan Tani tayi ta sababi tare da bata wani tuwan dawan daya kwana biyu, amsa tayi dan baci ma za tayi ba dan a koshe take, dakinta ta nufa ta kwanta domin ta huta, maganin da tasha yasa zazzabin ya saketa, ta fara bacci Tani ta shigo taga tuwan a gefe ita kuma tana sharan bacci, Tani tace jar far uba, bacci ma kikeyi fita tayi sai gata da buta ta fara zuba mata Ruwa a jiki da sauri Indo ta tashi cikin tsoro ganin Tani yasa ta tashi tsaye tare da fadin yakuri inna dan Allah, Tani tace dallah rufemin baki shegiya maza fita kije kimin cefane, ta mika mata naira dari gashi ki siyomin wake gwangwani daya, tarugu na goma, albasa na goma farin magi guda daya kuma idan kika dade ni dake ne, kuma wannan tuwan ubanki ne zaici,?tace inna zanci kaina ke ciwo tani ta tabe baki, tare da mika mata kudi, bayan ta amsa ta sakar mata ran kwashi mai zafin gaske fita indo tayi tana hawaye tare da rike kan, kai tsaye inda aka aiketa ta nufa ta siyo komai ta dawo gida, ko zama ba tayi ba ta hada murhu domin daura abincin dare.
A Majeed ne a cikin katon office dinshi, yana danna wayanshi, Abdul ne ya shigo bayan yayi nocking, abdul yace kai A majeed yau wata rana, A Majeed yace mai kake nufi? Abdul yace naga yau ka dawo kuma gaka a Office kaida in kayi tafiya sai kayi kwana biyu baka leko ba, amma yau gaka a office, A Majeed yace kana da sa ido wlh Abdul ni mai ya Kawo ka ma, abdul yace babu komai kawai nazo wajanka ne, so nake muyi magana, A Majeed yace badai a office ba sai ka bari idan nabar office muyi maganan a gida, Abdul sanin halin abokin nashi yasa yace toh ba damuwa tare da tashi ya koma Office dinshi.
Kaman yanda A Majeed yace ma Abdul a gida za suyi maganan hakan ko akayi domin bayan A Majeed ya fito Abdul shima binshi yayi har gidanshi, bayan dukansu sunyi parking A Majeed ya fito, baiko kalli abdul ba yayi ciki, shima abdul din binshi yayi ciki, wani dangareren falo naga abdul ya zauna, irin falon larabawa, falon yayi mugun haduwa da tsari,wata ce ta fito tasa riga gown amma ya tsaya dai2 giwa irin dai kayan da masu aikin turawa ke sawa, ta ajiye ma abdul snack da drink, Abdul ko kallon abun bai yiba, shidai jira yake A Majeed ya fito suyi magana, A Majeed bai fito ba saida ya kwashe wajan 1hr Kafin ya fito cikin bakin jallabiya ba karamin kyau yayi ba, domin ya fito sak balarabe, kallon Abdul yayi tare da fadin ina jinka, abdul yayi ajiyan zuciya tare da fadin kasan ranan da zamu taraba a wajan wani kauye akwai yarinyar da tazo tsallaka titi mu kuma munzo har tayi bar..... Plz ya isa haka abunda kake son fada nake son ji ba labarin wata ba, Abdul yace A Majeed labarin akanta ne domin tana da halaka Dashi, A Majeed yayi tsaki tare da tashi yace idan akan yarinyar da baka santa bane baka ma san inda take ba, zakai min magana so u better change d topic, Coz bazan saurare kaba, Abdul yace A Majeed I know where she is wlh am in love with d girl, A Majeed yace what? Kana nufin kana sonta? Abdul yace haka nake nufi, A Majeed yace kai gaskiya kaban mamaki duk matan dake Nigeria wayayyu, masu class educated ka rasa wacce zaka ce kana So sai mai talla yar kauye, abdul yace A Majeed I luv her and am ready to marry d girl, yarinyar nan za tayi abunda wayayyar Mace ba zata iyayi ba, sannan waye wa da yawa yana sa kauyanci, bani da burin auren macen data waye sosai, nafi son inyi aure a karamin gida, ma'ana gidan da basu da hali, saboda duk abunda na Kawo mata she will appreciate it, amma idan yar babban gida ce tana ganin iyayenta masu kudi ne, komai za tayi ban isa in hana taba, duk munin abun sai dai inna gaji in saketa, sannan ita..... A Majeed yace enough plz ka cikani da surutu am so tired I need to rest, abdul yace ok na tafi, bayan Abdul ya fita A Majeed bedroom dinshi ya nufa tare da kwanciya ya dauki wayanshi ya doka ma Zainab kira, har ya katse bata dauka ba, ya kuma kira shima batai picking ba, tsaki yayi tare da jefar da wayan gefe, domin tun jiya yake kiranta taki dauka ya rasa dalili.
Mlm musa da Tani suna zaune akan tabarma, Mlm musa ya kunna yar Radio dinshi yana ji, suna dan fira jefe2 shida Tani abu na gefe Tana zaune, maganan siyasa ake tayi a Radio din, mlm musa yayi tsaki tare da fadin sai suyi ta maganan sunyi titi da gada, mu ina ruwanmu dasu, mu kawai su bamu abinci, Tani tace aifa kam domin indan talaka akeyi mudai "TAMBARIN TALAKA" RUMBUN SA, yaro ne yayi sallama, bayan Tani ta amsa yace wai ana kiran esha, Tani tace waye kuma asha, kai jeka tambaya wa ake nema, yaron ya fita sai gashi ya kuma dawowa wai indo ake kira, Tani tace wanene yaron yace wani ne a mota, Tani tace kodai Abu akace ka kira? Yaron yace indo akace in kira, tani ta kalli Abu dake zaune tana kumbura fuska tace ke tashi kije hala ke ake nema, tashi abu tayi ta dauko gyalenta duk ya kode amma ita gani take kaman sabo, indo dake d'aki tana jin komai gabanta sai fadi yake domin tunda Yaron yace esha ta gane sulaiman ne, Abu ce ta shigo tana kuka, Tani ta tashi da sauri tana tambaya lafiya? Abu tace tani dan mai gari ne fah, wai kuma wajan indo yazo, harda wani cemin wai sonta yake yi, Tani ta Saki wani uban ashar tare da nufa dakin indo......
Taku maryam obam😘
💅 TAMBARIN TALAKA 💅
NA
MARYAM ALHASSAN DAN'IYA
🌈 KAINUWA WRITERS ASSOCIATION🤝
Vote me on wattpat @maryam-obam
WWW.maryamobamnovels.com
30to35
DEDICATED DIS PAGE TO...
hafsat mamani
(Maman jawaheer)
Ina yinki sosai My darling sis much luv❤
Bude kofar tayi da karfi, indo ta tashi zaune dan tsoro, dakin duhu babu haske, Tani tace ina kike makira, ta kwala ma abu kira tare da fadin kawo min fitila, Abu ta Kawo Mata fitilan tare da haska fuskan indo, Tani tace dan ubanki a ina kika san yaron mai Gari? Indo tace inna ni wlh ban sanshi ba, kawai ya siya wainar rogo ne, Tani tace dan ubanki karya zaki min, indo tace wlh inn..... Tas ta fara marinta tare da dukanta tako ina, ni zaki ma karya, yar iska, dama shine yake lalata ki, shine ya biyoki har gida, Tani dukanta takeyi tako ina, saida ta mata lilis Kafin ta barta, tace wlh idan na sake ganin yazo gidan nan nemanki saina yanka ki yar iska, ta fita fuuuu, zama tayi kusa da mlm musa Tana fadin shima d'an mai garin in banda asara ya rasa wacce zaiso sai wannan makiran yarinyar, kalli Abu yarinya kyakyawa sai dai fari kawai wacan makiran zata nuna mata, mlm musa yace ai yarinyar nan yanda kika san mayya shegia ni dama ta mutu mu huta, Tani tace hmmm yar iskan sai taurin rai inda zata mutun aida nafi kowa murna wlh, Abu tace Tani nifa gskiya ina son yaron mai gari, tani tace