Showing 27001 words to 30000 words out of 93195 words
Chapter 10 - Tsaka Mai Wuya Complete Hausa Novel By Janafty .txt
Don ma naji ba shi da Tsami ne na sha da yawa"
Amma ta jinjina kai kafin tace"To ai baki ci komai ba Hasiya?
Cikin Tabbatarwa nace"Na ci wake da mai da yaji Amma"
Amma ta kuramin ido kafin tace"Kin tabbatar? Kin san kina da lulura kuma ki rika wasa da cikin ki"
Dariya na yi kafin nace"Amma kada ki damu a koshe na ke"
Bata kara mgana ba ta fara jan Casbahan da ke hannunta ni kuma na isa ga jakar da nake tara kudin ciniki na Dauko na zube su a tsakar Dakin ina Kirgawa bakina har kunne na ce ma Amma Danwaken ana samu da shi Sosai.
Amma ta gyada kai kafin tace"Sai mu godema Allah"
Sai da na gama kirga kudin na ware na wanda za'a je kasuwa ina cewa"Amma garin Danwaken mu ya kare ga Habi bata nan"
Amma tace"Ki je da kanki mana. Tunda baki da tabbacin yau zata dawo kada ki jirata kuma gobe babu garin a hannu."
Da shawaran Amma na yi amfani sai da nayi wanka sannan na yi shirin Fita. Tunda Amma tace sai anjuma zatayi wanka ni na fara yi tunda fita zan yi, Hijabina na saka har kasa akwai Nikab na Habiba ne shi na ara na saka bana son a samu wata matsala ne.
Amma na gefe tana kallona har na Soke yar wata jaka mai igiya ta Habiba ce na ara saboda saka kudi nayi ma Amma sallama tayi min fatan Dawowa lafiya na fita.
A tsakar gida na ci karo da Maman Boy da maman salihi nasan sun yi da ni Saboda naga suna nunani da baki ban damu ba na fice ina Fad'in"Zan shiga kasuwa"
Da Sauri Maman Boy ta mike tana Fadin"Tsaya Hasiya. Daman ina son Citta da kunafari nawa sun kare"
Dole na Tsaya,Ammh Maman boy sai da tayi min taron mutane sako wajen na mata biyar suka hadamin ga shi kuci kuci hakanan na karb'a bani da Mafita.
Har na kai bakin Titi ba bu wanda yaa ganeni bakina alaikum na shiga kasuwa wajen masu had'a garin Danwake naje na fad'i iya adadin za'a hadamin sai na shiga cikin kasuwa na siyo wayan murhu da gawayi.
Sai na siyo wake da mangyad'a da Borkonu sai kayan maggi da kayam kamshi, sai sakon su maman Boy na jima a kasuwar sannan aka gama Had'amin komai tunda sai da na jira akayi nika. Aka had'amin komai cikin wani karamin Buhu mangyadan ne kawai na rike a hannu kada ya fashe.
A bakin Titin Tsamiya na Sauka Tunda bazai shigo dani ba. Na Dauki Buhuna a saman kaina mangyada kuma yana Hannuna Lokacin Rana tayi Biyu har ta wuce.
Ta layin da zai kai mutun har gidanmu na bi inda masu awara ke layi wajen su biyar suna ta siyan su har da masu Dankali da kosan manja.
Da zan wuce naga matasa a wajen tunda daman wajen zamansu ne. Naji muryan wani Saurayi yana Fad'in"Ke mai awara nan barayin ina ake saida Danwake mai Dad'i da Safe haka?
Na ji sanda wata yarinya tace"Nan dogon gida ana Danwake da Safe mai Dad'i Da wake in mutum na so, sannan mangyada ko manja sai wanda ka zab'a".
Na wuce acikin raina ina jin dadin ko bakomai akwai jin Dad'i a yabi sanar mutum, har na isa gida bakina yaki Rufuwa ina ko sauke kayan saman kaina na fara gayama Amma.
Tayi dariya kafin tace"Hasiya manya.."
Ina Dariya nace"Amma baki ji dadin da naji ba"
Ammh ta yi mirmishi. Sallah nace zan yi sannan na warware kayan na mikama su Maman boy sakon su har sun fara lekowa suna Fadin"Hasiya nace dai baki manta da Sako na ba ko? Tafarnuwa da ungurnu ne ni dai Sakona"
Har sai da nace musu Sai na yi Sallah zan Fito da sakon su na basu, sannan suka shafamin lafiya.
*Littafin TSAKA MAI WUYA paid book ne, iya Book 1 ne free Pay N500 For BOOK 2,3. Regular group or VIP GROUP N1000. Via 0552179550 Jamila Umar gt bank.*
*Shedar biya ta wad'anan lambobin 09069067488 or 08032773332.*
*SPECIAL GROUPS Follow@Jamilaumarjanafty On AREWABOOKS mutanen mu na Niger za su Tuntubi Kausar Aglan nissa +22796562223 Nagode*
*Janafty*
*10/09/2023*
*TSAKA MAI WUYA.*
*Wattpad:Jamilaumar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*
https://chat.whatsapp.com/CPRnRPcAD5K8vEY91Ziz8V
Albishirinku ya yan'uwana An-Nisa! Ina wacce ta dade tana amfani da Sabaya amma bata ganin aikinsa duk kuwa irin shan da take masa ? To share hawayenki tamu Sabayar ingantacce ne wanda muka sake bakin aljihu muka zuzzuba kayan gyaran jiki wanda bana cutarwa ba infact shi wannan hadin 2 in 1 ne…. Hadin SABAAYA da ADUMULMULA, in kina fama da matsalar zubewar Nono to wannan had'i naki ne, in kinaso ki cicciko fatarki tayi kyau ki koma tamkar ‘yar yarinya to ki riki wannan hadi namu… Aikinsa bai tsaya iya nan ba hatta da kara lafiyar garkuwar jiki yanayi da kuma kara ni'ima…kowa na iya shansa, matan aure, Masu shayarwa in kin kusa yaye, 'yan mata, babba da yaro, maza da mata kowa na iya amfani da wannan hadi namu…. Muna maraba da mai siyan daya ko sari.
Abangare guda kuma muna had'a magani ingantacce na ciwon sanyi da yaki jin magani, in aka daure ana amfani dashi ana dacewa bi'izinillahi ta'ala, kai hatta da maganin hawan jini da diabetes duk muna saidawa kuma ana dacewa in sha Allah.
Atuntubemu tanan whatsApp or call 📞 07065481260.. Don Allah don annabi in kin san ba siya zakiyi ba kar kizo ki bata mana lokaci da tambayoyi please kayayyakinmu original 💯ne babu algus
*07*
Shi Sadiq a kan Quantity Surveying ya samu shaidar Degree d'insa na farko.
Ma'ana sani kan harkan shimfid'a Titina da sauran su.
Shiyasa ya ke bautar kasar sa a Dismento Nigeria limited Old Sokoto Road, Samarun Zaria.
Shi kuma Tahir Politcal Sciences ya karanta wato harkan abunda ya shafi Siyasa. Ya na bautar kasar sa ne shima a wata goverment secondary na cikin Samarun zaria.
Yau litini tun bakwai da Rabi ya fita ya bar Tahir a gida ya na faman nuku nukun sa, Sai da ya biya in da ya fara siyan Danwake mai d'an karen Dad'i ya mika karamar kularsa da ya ke zuwa da ita ga yaran da ba'a rabasu da wasa a kofar gida suka shiga suka amso masa.
Dashi ya tafi wajen aikin nasa. ya riga ya saba tunda ya samu Danwaken nan da shi ya ke tafiya wajen yana karyawa har kuma wani Lokacin ya yi ragowa ya dawo da shi gida. Watarana kuma wani wanda suke aiki a wajen shima hidimar kasar ya ke yi suke ci tare.
Karfe biyu saura ya baro kamfanin kamar yadda ya saba adaidaita ya hayo zuwa anguwar Tsamiya aka sauke sa a bakin Titi ya gangaro da kafarsa.
Yasan Tahir na rigashi dawowa tunda makarantar sa ta fi kusa gida. Sannan ba tsayawa ya ke a tashi ba da ya gama Darasinsa ya ke gudowa gida Tahir dan Shiririta ne ba komai ya ke ba ma Muhimmanci ba shi dai wayarsa kamar tafi komai muhimmamci a rayuwarsa.
In kaga ciwon da Tahir bai Dauki waya a hannunsa ba to kila sai dai ciwon Ajali mutun ne mai mu'amala da kafafen yad'a zumunta sosai ba irin Sadiq da waya ko hawa irin kafafen nan ba su dame shi ba, Shi dai barsa da kallon Fina Finan korea da turkish Drama suna nan cike a Laptop dinsa ko Tab dinsa. Sai kuma sanin kan Na'ura mai kwakwala wannan tun yana karami ya iya sarrafata tunda ya taso ya gansu ne shima agidan su.
Dakin a bude Tahir ya barshi Saboda Sabon Iskanci har da su Dage Labule sama a dakin na Fuskantar waje, ga shi cikin Anguwa mai cike da Mutane sai wucewa ake yi ana ganin musu asirin dakin
Ba wannan ya fi bata ma Sadiq rai ba sai ganin yadda Tahir ya yi kaca kaca da Dakin Alhalin kafin fitarsa da Safe sai da ya kimtsa dakin shara ne kad'ai bai yi ba yace sai ya Dawo.
Tun kafin ya shigo ya gimtse fuskarsa Sanye ya ke da Riga da wando,Rigar mai Dogon hannu ce mai ruwan Ash da layi layin blue. Wando kuma jeans ne mai ruwan kasa sai Rufaffen baki takalmin da ke kafarsa bayansa Rataye da Jakar laptop d'insa sai karamar kular da ke hannunsa.
Yana shigowa ba domin sanin Darajan Sallama ba, da ba zai yi ba sai dai yasan Darajanta tunda shi Musulmi ne Murya ba Dad'i yace"Assalamu Alaikum.."
Bai ko jira Tahir dake kwance kan Katifa da ya yi wani da'i da'i ya amsashi ba cikin Fusata yace"Haba Tahir. Haba Tahir meye haka?
Ya fad'a yana kallon Tahir din cikin Takaici.
Tahir da ke kwance daga shi sai dogon wando ko Riga ba bu ajikinsa wayarsa na Hannunsa yana Dannawa ya yi matashi da d'aya hannun na shi Cikin kosawa da irin ka katsemin aikin gabana ya Dago yana kallon Sadiq kafin yace"Miye wai? Kai dai baka raina abun korafi wlh. Zafi ne ya isheni ga shi ba wuta shiyasa na bude kofar na kuma D'age labulen mu samu iskar Duniya ya shigo mana"
Daga haka ya koma ya cigaba da Dannan wayarsa yana ta faman mirmishi. Sadiq ya tsaya kawai ya na kallon Tahir bakinciki ya chuse ranshi. Kai tsaye ya sauke jakar hannunsa tare da kulan ya dago cikin Zaro ido yana nuna Dakin da kallo kafin yace"Au baka san me kayi ba ko Tahir.? Ba ka san ma me ka yi ba ko Tahir?
Tahir Hankalinsa na kan wayarsa yace"Me na yi kuma?
Da muryan ko ajikinsa.
Sai kawai Sadiq ya yi kwallo da Takalmin Tahir da ya cire nan tsakar dakin sai da ya Daki bango ya Dawo Tahir ya Dago yana kallonsa baki Bude kafin yace"Me ya yi zafi Alarammah?
A fusace Sadiq yace"Ban sani ba. na gaji da kazantar ka Tahir na gaji. Kai yaro ne? Komai sai an gayamaka zaka yi? Bakina kullum akan mgana d'aya ne ehe?
Ya karishe fad'a har jijiyon kansa na tashi alamun ranshi ya baci ganin haka yasa Tahir ya ijiye wayarsa nan saman gado ya mike yana fadin"Yi hakuri to. Kasan gajiyan da nayi yau? Daman fa ina da shirin na mike na kwashe na share dakin ne ka shigo"
Ya na fad'a lokaci d'aya ya duka yana kwashe kayansa da ya cire watsar da su anan.
Sadiq sai faman Hararansa ya ke yi kamar idanuwansa za su fad'o kafin yace"mgana d'aya ba zaka Dauka ba Tahir. Shikenan ka cigaba"
Daga haka ya karisa gaban Fridge ya Bude ya Dauko ruwa ya sha anan duka ya shanye ya fita waje ya jefar da Goran sannan ya dawo.
Tahir dai dole ya kwashe duka kayansa ya kimtsa wajen saboda yaga Ran Sadiq ya baci yasan Halinsa haka ya ke ba shi da Saurin fushi ammh kuma ya tsani ya rika maimaita mgana Daya.
Sai ga Tahir har da Shara, sai bayan ya gama ne ya yo alwala ya zo ya yi sallah Lokacin da ya idar Sadiq na kan katifa barayin da yake kwanciya tunda Kafitar tsakiya Dakin suka sakata kowa farko ya ke so ba Lungu ba, sai suka raba Gardama suka sanyata a Tsakiyan Dakin.
Ya na sallame sallan yaga Sadiq da ke danna laptop dinsa har ya sauya kaya zuwa saukkaku na zaman gida. Yanayin kallon kad'ai da ya gani ya sha jinin jikinsa da Sauri yace" kana wani kallo na kamar na yi sabo? Lalurin sallar azahar har sai la'asar ta gabato."
Sadiq kamar ba zai yi mgana ba sai kuma ya jinjina kai kafin yace" kai dai ka sani. Kai ba yaro ba ne in daidai ka aikata ma ai ka sani Tahir ba ruwan Sadiq aciki ni dai tsakani ga Allah na fita hakkin zaman tare"
Daga haka ya cigaba da kallon allon Laptop dinsa shi kuma Tahir ya mike yana Hamma kafin yace"Abokina yunwa na ke ji. Kuma miyar nan fa ta kare ita kenan jiya na yi mana shinkafa da Miya."
Banza da shi Sadiq ya yi ganin haka yasa ya nufi kular da ya shigo da shi ya jawota yana fad'in"Wai miye a kulan nan ne da ko da yaushe ka ke fita da ita kuma ka dawo da ita?
Sai dai me? Ya kasa mgana da ya ga Sauran abunda ke ciki Danwake da wake da Manja an chakud'a an ci an rage kad'an.
Da sauri Tahir ya kauda kansa kafin ya Dago yana kallon Sadiq cikin Jin haushi yace"Haba Sadiq. Tsakani ga Allah abunda ka ke yi yanzu ka kyauta kenan?
Ba tare da Sadiq ya kalleshi ba yace" me na ke yi?
Tahir yace"Gidadanci mana. Eh mana Gidandanci mana ban da haka miye ribarka na zuwa da Danwake wajen aikinka Tsakani ga Allah? maganar gaskiya wannan dabi'ar taka ta katon bagidajen Kauye ne"
Mirmishi Sadiq ya yi kafin yace"To miye bambamcin Tahir? Ai bagidajen kauyen ne ko baka sani ba?
Ya fad'a yana saka kallon wajen Tahir wanda ya rufe kular ya dawo gaban Sadiq ya zauna saman katifa yana Fadin"Danwake a kula kamar wani yaro dan firamari Sadiq? Ina laifin in Danwaken ka ke son kaci ai akwai a Restaurant sai ka shiga ka siya kaci tunda kai dai ka san nasan abinci ko wani Restaurant in kana Ra'ayi zaka ci bai fi karfin aljihun ka ba"
Yadda Tahir ya ke mganar zaka san abun ya mishi ciwo, duk da yasan Waye Sadiq ta wannan bangaran bai taba Tunanin abun na shi ya kara Lalacewa kamar haka ba.
Wai Danwake a kula abun ma ba shi kunya ya ke yi wlh in ya tuna kuma wai ka shiga cikin mutane da shi kamar wani karamin yaro.
Lura da Hakan da Sadiq ya yi shiyasa ya ture Laptop din gabansa ya Fuskancesa kafin yace"Rayuwa ce. Kowa da irin yadda ya ke tafiyar da tasa Rayuwar Tahir. Miye aibu aciki don na siya abunda nake so na tafi da shi wajen aiki na?
Da Sauri Tahir yace"Wlh akwai aibu. Babban aibu ma kuwa. Aikin yara fa ka ke yi? Yaran ma kanana Sadiq. Haba don Allah"
Tahir ya fad'a har yana wani juya Fuska irin yaji kunyan nan. Dariya Sadiq ya yi kafin yace" A wajen ka kenan ya ke aibu ni dai a wajena a daidai na ke kallonsa kasan Hausawa na cewa Daidai wani.."
" Karkatan wani.."
Tahir ya karishe cikin mamaki kawai yana kallon Sadiq. Shi kuma yana yi masa mirmishi sai kawai ya rike Haba yana fad'in"Ikon Allah.. Allah mai mutane kala kala kawai sai aka ganka ka fito da kula ka bud'e ka na cin Danwake da wake da Manja."
Sadiq yace"I sata na yi? ni zan ci kayana ra'ayi na ne. Ban kuma takurama Ra'ayin wasu ba."
Tahir yace"Ni tsaya ma a ina ka ke siyan Danwaken nan ne?
Sadiq ya ce"chan ne wani gida a kasan layin wajen masu awaran nan da Dankali"
Cikin takaici Tahir yace"kai ko a ina kasan gidan? Ko da ya ke in wajen ciye ciye irin wannan ne kai tsuliyan gari ne"
Sadiq yace"Ni fa ranar naje siyan awara a wajen naji wani na tambaya ina ake saida D'anwake mai dad'i? sai wata mai awara ta kwatanta masa gidan kuma ta yabi Danwaken shiyasa nima nake zuwa ina siya. Kuma Alhandulillah akwai dadi ga tsafta"
Tahir ya karkace baki kafin yace"A ina kasan ya na da Tsafta? Hala a waje ne a ke d'anwaken? Ko kasan me yin Danwaken ne?
Sadiq cikin kosawa da Tambayoyin Tahir yace"ba'a waje ba ne acikin gida ne. Ta ya za'ayi na san mai yin Danwake Tunda ba gidan na ke shiga ba"
Tahir ya ce"Uhm sai kaga yadda ake D'anwaken ka raina kanka Sadiq. ba fa kowa ke tsaftace abun sana'arsa ba, barin ma irin gidajen anguwannin nan. Wani abun wlh in kagani kamar kayi Amai.."
"Tahir.. Tahir don Allah.."
Sadiq ya katseshi bayan ya Daga masa hannu Dariya Tahir ya kwashe da shi kafin yace"Wai don nace Amai..Amai..!"
Sadiq ya ce"Daman kazami ne kai. na sani"
Tahir yace"Tabdijam! Ai dama a Shinkafi a ka haife ka zaka fi Dacewa da Katon kauyen Shinkafi ba na Birnin Zamfara ba."
Sadiq ya yi dariya har sai da ta yi Sauti lokaci d'aya kuma ya kimtse fuska ya kurama gefe d'aya ido kamar mai Nazari. Kansa ya jinjina kafin yace"To ai ban yi maka karya ba Tushena kauye ne. Kuma kauyen Shinkafi. Ko ba'a Haife ni achan ba chan aka Haifi Abba. Sannan lokacin da aka haifeni Umma ta fara rashin lafiya ko arba'in d'ina ba'ayi ba Abba ya ce Innani ta tafi da ni da Umma Shinkafi ta na kula da ni, Sannan ina da wata Takwas saboda Laluran Umma Innani ta yayeni babu abunda bata ba ni na ci Saboda inganta lafiyata ba, Tahir ban sha Nonon uwa kamar yadda ka sha ba. Hannun Innani na zauna har na tsawon Shekara Shidda sannan Abba ya karbo ni na dawo zamfara Ka ga kuwa ka daina mamaki in kaga ina cin wani abu akwai sabon haka Tun ina da kuruciya da su na Saba, kuma ni Inanni ta yi min Renon uwa ka sani ko a yanzu ta mini gatan da ko Abba da ke d'anta ba ta yi ma shi ba"
Tahir da ya yi Tagumi yana kallon
Sadiq ya na jinsa ya Sauke ajiyar zuciya kafin yace"Shiyasa ko Hajja na je gida ta rika rawan jikin kawo min abubuwa taga na fara cewa ba na cin kaza sai ta fara fad'a tana fadin kai dai ka cika kircin tsiya shiyasa nake son abokin nan naka Saddiqu yaron nan har mamaki ya ke ba ni ga shi Dan gata gaba da baya ammh a irin Rayuwarsa kamar wanda baisan gata ba komai ci ya ke har kaji ya na fad'in Hajja zogalen nan ki ijiyemin zan ci da Daddare ammh kai sai shigen iyayin banza da Wofi tafi mara wayau shiyasa baka kiba kullum lange lange kamar iska"
Gabadayan su suka kwashe da Dariya Tahir yace"Ina shan gori wajen Hajja komai sai tace Saddiqu ya fi ka Tahir kai kam sai fatan Shiriya."
Sadiq yace"Allah sarki Hajja na yi kewar Dambunta da kwad'en Zogalenta yaushe zamu je Daura?
Tahir yace"Kasan ko kwanaki ta yi ta fama da Zazzabi."
Sadiq ya kallesa kafin yace"Subhanallah yaushe? Shine baka Fad'amin ba?
Tahir yace"Kawu ya ce da Sauki shiyasa kaji ban Fad'a maka ba. Kasan Hajja da kafiya ga shi ta na ciwo ammh taki bari aje asibiti wai ita ta warke."
Sadiq yace"In na ganta Innani na nake gani a tare da ita. Bambamcin kad'an ne ita Hajja ba ruwan