Showing 39001 words to 42000 words out of 69834 words

Chapter 14 - ABIN CIKIN RUHINA BY MISS BB.txt

Miss Bb   

10 Jul 2024

8270

su,to Amman yanzu abun nata gaba yake wata sa,in in tazo saitace zatayiwa Ameer girki ni naje nahuta,to hutunme garan bawani surfe ko nik'a nikeba,aisune dai za,ace kana gajiya aikin gidane kamar ko taushe yan share share da goge goge,saifa sanwar da gyaran dakuna.
Hankalinta ya gaza kwanciya da halin data bullu dashi,gashi bata tafiya har sai yadawo taringa jansa da hira kenan har sai yabiye mata,.
Karshe tace shine xai maidata gida idan suka fita Ameer shida dawowa kuma,saidai nafarka tsakar dare inganshi........wata ranar zan jiyosa yana wanka karfe daya ko biyu,babu kyau zargi amman tabbas ina zarginsu shida ita,kasancewar nasan halinsu suduka,Raihana ba tun yanzu take bin maza ba,........shikuma rauni garai indai kan mace ne nan take tana iya jawo hankalinsa kanta,hatsabibiyace ta kin karawa idan ta saka abu gaba babu ubanda ya isa ya hanata,ba gaban iyayenta takeba hannun kakarta take kuma bata son laifin jikar tata,salma bata da natsuwa cikin kwanakin,da yadda suke da Ameer abun gwanin sha,awa Amman yanzu ko kallon dakinta baiyi balle yace zaishiga,yafi sati uku rabin daya kusanceni.
Abincina yadaina ci killum kuma da sassafe za fita office,bai dawowa sai taltainin dare..........wannan abun ke azabtar da ita duk ta kara lalacewa,tashiga tashin hankali marar misaltuwa,tarasa waye zata kira yayi mata soving wannan problem din...........ta tuna yar uwarta khairat,irin abubuwan dasuka shirya mata itada raihanan,gashinan to yanzu ta juyo kanta.kuka ta fashe dashi tana nadamar abunda tayi,wai itace har gaban malamin tsubbu takai yar uwarta wadda suka sha nono guda suka rayu tare,suke son junansu kamar rai da ajali,Amman tabiye shawarar qawa ta kaita ta baro,ta rabata da wanda takeso itama kuma yar uwar tata bata samai ba.
Wannan kadai ya isheta ishara ga ta bata ma iyayenta rai,Allah bazai barta ba......haka take ta kukanta kamar idonta zai fito.


*wannan kenan*


***********


Amarya khairat sun d'age kasashen turai,kafin sutai ya zaga da ita dangi ta gaida iyayensa,da nata duk inda sukaje sai sambarka banda gidan yar uwar dadysa yayar dadysu,ko ruwa wannan comon ba abasu ba ba asake bi takan su ba,shi dr yasan dalili nice ban saniba,shiyasa bamu wani jima ba muka baro gidan koda yaga fuskata ta canja ya kama jana da labarin ban dariya har saida na saki fuskata..........gaskiya babu laifi dr ya iya love saidai bansan meyasa baya nuna man shi kan gadoba,duk yadda nake sha,awar sex to daya tun karoni yafara abunda yake zanji yafita raina,because baya wasanni dani shidai kawai yajishi yashige shine muradinsa,nikuma bana so bansan kuma tayadda zan nuna masa ba,inajin kunya gaskiya gashi da dadewar bala,i tun inashan kukan har nazo na hakura na dai kukan,saboda nidai ban tabajin wani dandano ba ckin harkar,kullum sai bakar azaba gabana yaringa wata irin zafi saina kwana na yini yana zafi.
Na rasa yazanyi Husna kurun muke wannan maganar,don yah meenah bata barina ma ina dauko maganar balle ta fahimceni,maah da Annie kunyarsu nakeji matuka bazan iya dizcousing wannan issue din dasuba,dole nabar abun matsayin kalar tawa rayuwar kenan ni bazan tab'a jin dadin Aureba har abadan.


Munje gida sallama yace nayi masu kwana biyu,wayyo dadi jinai kamar yajefani aljannah.......da Abbu yace aa saida yaga ina kuka sannan ya kyaleni.


Inajikin maah bana matsawa ko ina don nayi missing nata sosai,Anty shida tana dubai itada yah jahid,yah meenah ce kurun musha hirar mu tunda har yanzu hutu muke,sai mun dawo daga yawon honeymoon sannan hutun yake karewa.
Dadaddare dakin maah zan kwana ta nata bani labarin abunda yafaru bannan,har tazo kan *ABIN CIKIN RUHINA* tace,
"Umminki nata cewa tunda kika gama makaranta secondary bakijeba har kikai aure,ince maki idan kun samu lokaci keda dr kuje kugaidata,dama kuma Abbi dinsu imran baida lafy kinga idan kuka tai wannan yawon sai ku biya kudubashi,babu dadi tana sonki kina gudunta."


Shiru nai ina tuna wasu abubuwa dasuka wuce ba wai banson ummina ba,inasonta sosai saidai dole yanzu matsayina na matar aure matar wani naguji abunda zai tada man feeling din wani cikin raina,hakika ban taba mancewa dashiba amman me ina ciresa da karfin bala,i saboda gudun jefa rayuwata halaka,ai halakace kana auren wani zuciyarka tana tunanin wani,bazaka taba samun kwanciyar hankali ba ga tarin zunubai kuma,dannewa nai kawai bance mata aa bazamu ba nace,
"Allah ya kaimu lokacin maah,insha Allah zanje wajen ummi ko yini muyi mata."
Hararata tayi tace"aa karma kuje kawai,yinin banza yaushe har kuka gama gaisawa na lura bason zuwa kikeba."
Hkr nabata nace"sorry maah kwana nawa kike son nayi mata to."


Ganin zata tashi taji haushi yasa nai saurin rikota ina dariya,naita lallashinta harta sauko tace"ina laifin kiyi mata sati guda."
Maimakon nayi gardama sai nace "to insha Allah,kilan ma mu tadda Anty shida can ko."
Tace "Aa inajin jibi zata dawo don katsina zata ta anso ko me,kinsan ta samu aiki,shahid ma ya samu shiyasa za,a hade bikinsu dana meenah lokaci guda."
Farinciki ya kamani nace"abu yai kyau wlh naji dadi Allah yasa Alkairi,,,,,nan mukai ta tattauna maganar har mukai bacci.


Washe gari Abbu saboda ni baije office ba muka zauna mukaita hira kamar anyi shekara ba,a haduba.
Kwatsam saiga salma wurjan wurjan,da ganin idonta ma kuka tasha,na mance daduk abunda yafaru na rungumeta ina matsar kwallah,haba itama saita kama kukan,mukaitayi daker mukai shiru zubewa tai gaban maah tarike kafafunta tana kuka tace
"Kiyi man rai maah kiya fe man,wallahi nayi danasani,ban kyautata maki ba wlh sharrin zuciyane dana qawa kiyi hkr ke mahaifiyata ce kiyafe man......"sai kuka kowa tabashi tausayi wajen Amman banga hakan ga Abbu ba,shan mur yayi matuka maah dagota tayi tana lallaashi
"Daina kuka salma ai hannunka baya rubewa ya yanke kayar,duk abunda kikai mun yafe kinjiko daina kukan haka,ai mungode Allah ma dakika gane gaskiya."


Cikin dakakkar murya Abbu yace" mekikazo yi gidan yanzu,bacin sanda kika barshi kina farinciki har bakinson zuwa neman Albarka mu da muka haifeki."
Rarrafawa tayi wajensa tana kuka take bashi hkr kuka fake sosai,Aman Abbu ya rude idon sa yace baisan wannan ba tatashi tatai gidanta tunda ta nuna bata ra,ayin wannan.
Saida Annie ta saka baki sannan ya kyaleta yana tambayarta lafiya tashigi gidan haka kamar wadda aka koro.
Ta na kuka take basu labarin Raihanna"tun wancan lokacin ashe neman juna suke ban saniba,sai dana gansu da idona agidana na nuna bacin raina shine tasashi ya yi man dukan tsiiya,saida na kwanta asibiti bacinan kuma ta dawo gidan da zama wai ai tunda aure zasuyi,nanda sati biyu.............kuka yaci karfinta takasa karasawa gaba daya munshiga tashin hankali,wace irin rayuwace wannan salma keyi Ameer din zaiyi haka,duka auren kwanan sa nawa dazai wannan lalacewar anyi gudun duniya yayi wata uku.
Salati da sallallami kawai ketashi falo,salma najikin yah meenah kukan kurun take.


Abbu yace"shine kika taho."
Tace"Aa don nace ban yarda ta zauna man giba ina kallonsu suna abunda bai dace ba shine tasashi ya dakan yace ina taho gida sai yaneman."
"Lahaula walla quwwata illa billah,naga abunda ya isan bai ishi ubangijinaba ni saudah,shi ameerun yayi mai wannan tozarcin lallai yacima dan iska."


"Kanaji Abbukhair,bazaka ce komiba gaskiya ka kirashi yazo kadauki mataki mummuna kanshi,taya zai kamata yaringa duka kuma duka yaushe akai auren har da zaice zai karo mata kishiya,kishiyarma qawarta wadda tasan ta tasan komi kanta,gaskiya kayi wani abu."
Tashi yayi yace"ga dakuna nan sai wanda ta zab'a ni banda lokacin saurarensa yanzu tukun."yan gama fada yafice ya barmu.


Wannan rana batazo mana dadadi ba,kwana mukai mu uku muna tattauna maganar,nida ita da yah meenah,nasha kuka don har yanzu ina son yar uwata tausayinta ya kamani,sainaga ni ai ba komi bane tunda bana fusantar irin wannan rayuwar,
Bamu samu bacci ba sari gaf da asuba gashi jirgin karfe tara zamubi muwuce (US) dama na hado kayana tass,daker na tashi nai salla sannan nafita ina taya maah girkin safe.


"Kinga dai abunda yafari da yar uwarki,to kadan daga cikin cin amana kenan dakuma sab'ama iyaye kidauki darasi kanta,ina maitabbatar maki bama gamawa akaiba,ba fata naked mata ba amman tabbas duk wanda yasai rariya ya San zata zubar da ruwa,don haka kisan wacce kike ciki duk da nasan duk aure yana da kalubale,haka yake kuma nasan kina taki matsalar,ina sane ban tambayekiba don nima inson ki koyi rike sirrin gidanki,komuma zamuji dadi iyayenki,kicigaba da hkr kowa shine yake zaunar dashi gidan mijinsa tare da iyalinsa,babu wani waje yanzu da zakije kizauna da yafiye dakin mijinki,don haka kikara hkr kinajina."
Jinjina kai nai ina cewa"hakane maah insha Allah zanyi duk yadda kikace amman ina tausayin salma,kisa baki Abbu yakirashi adaidaita komi."


"Karkidamu ni kaina bazanso zamanta gidanba zanyi duk yadda zanyi komi yadaidai ta,amman kinsan wancen auren saiyayishi,bafa mutuncine dashiba dan iskan yarone na bugawa jarida shafin farko."
Dariya nai tace"wallahi kuwa,kuma karkiyi mamakin idan shima baga bokan ta kai shiba,saboda ai kinji tace farko lafiya lau suke."
"Hakane ma ah babu tantama wlh,amman kisata Addua nima innaje saudiyya zan akata,kiyi mata nasiha kikara kwatanta mata maah nasan zata gane."


"Shikenan kije kishirya lokaci na tafiya,kardai ki manta da zuwa wajen umminki."
Dariya nai knacewa "insha Allah maah."


Karfe takes da rabi dr yazo nan yayi break,yanata jan yah meenah wai ta kusan tsufa agida........gardai ayi bikin itama tatare gidanta tana cinyewa su abbu abinci,dariya ta kamayi harda salmar aka rakamu airport duk sai naji kewarsu......rungume juna mukai muna share kwallah,aka kiramu muka shige.
Sai birnin london ta alkhairin Abbu.


#mrs bb ce 😉💕💕😘😘
💕💕💕💕💕💕💕
🌹
*ABIN CIKIN RUHINA*


Writing by mrs bb
Mom muhseen.


Wattpad name
Humaira7531.


DEDUCATED TO ZAUREN MRS BB.


*_ABOUL-NASSER (ALFAH) COMING SOON INSHA ALLAH._*
FATAN ZAKU JIRAYE SA NAN BADA JIMA WABA INSHA ALLAH.😉🌹🌹


GODIYATA BATA DA IYAKA GAREKU FANS BANSON HAKA KUKE SONABA,ALLAH YABAR MUNKU LOV U ALL.
😘😘😘💕💕💕🌹🌹


Not edited.


38&39.


Waje na samu na zauna inajin kafafuna baza su iya daukata no ba,banson had'uwarmu banso ko kadan,shiyasa tun farko naso bujirewa maah badan banson zuwa wajen ummin ba,saidon gudun irin hakan jikina rawa yake saboda wata irin yunwa da nakeji.........youghout ko ice cream kurun nake son sha don sune kayan shana bana iya cin komi har gara cake amman ban dashi saifa kayan zak'i.
Wayata na sake dauka in kira ummin in roketa taturo man yah imran din...........saidai wata tsaleliyar mota data shigo ta shagaltar dani,farace k'al tayi masifar yin kyau dagani new modan ce.
Fasa kiran nai na zuba ma motar ido inson ganin waye ciki,zuwa wani lokaci na hango wani mutun yana nufo inda nake,hankalina yatashi ainun.
Tashi nai na fara neman guduwa don wallah mutumen ma ni tsoro yakeban,gashi dai gabjeje kuma baki kamar dai dan africa.
Ganin zan ruga mai yakara sauri nima na kara nawa saurin ina jin kamar zan saki fitsari,,,,,nayi wata irin zufa addua kurun nake ina rokon Allah ya tai makeni.........jinai na karo da mutun dagowar da zan ashe mutumen nan ne wata kara na fasa na ina kwasa wa aguje........ninai kurun anfizogoni anjefa cikin mota.......duk na gigice jikina tsuma kurun yake.......figar motar akai kamar zamu tashi sama muka bar fikin jirgin.


Saida mukai nisa sannan na dawo cikin hayya cina na tuna ban kwaso akutunana ba,cikin tashin hankalii nace.
"Driver wait na manto jakunkuna na filin jirgin don Allah kamai dani na dauko."


Kamar daga sama naji muryannan da ko doguwar suma nai zan ganeta,saidai wannan ta shabanban da wadda na sani watannin baya,,,,wanan kamar an kara mata suger muryar jinake har sino take fitarwa don tsananin sanyi da zak'i.


"Uban waye drivernki."


Shiru nai don tabbatar da shine naji zafi zagin,rabon da azagan harna manta dama shine keda sana,ar zagin to tunda yatai ban sakejin wandanyace don ubanki ko dan uwarkiba..........shiru nai na hkr nasan dai nayi asara don duk kayana dana siyo nawa dana tsarabar da zan koma dasu suna can cikin jakunkunan,.......har mukaje bakina bai sake maganaba illa skakar kamshin dake gauraye da motar danake inajin dadinsa,tunda nafara laulayi bayan kamshin turaten Dr babu wani turare da yadauki hankalina irin wannan danake shak'a, bazan iya tantance nashine ba ko na motar ba.......zanso insani.........idona rufe yake banma kallonsa balle har nasaka ma raina wani abu tafiya ce maidan nisa mukai kafin muka isa,rabona da Dubai tun na gama primary nazo nai hutun wata biyu daganan sai fa yau,duk garin ya canza man ansake samun cigaba ta ko ina........har naso inzama bakyauya duk da dai naje knda yafi nan din kyau datsari.........


"Kina iya fitowa."
Yafice yabarni tsaye bin bayansa nai da kallo mamaki ya cikani,kayana nagani zube ya fiddo daga but koyaushe aka saka su oho.
Ummi da Mimi da sadam suka iso suna man oyoyo sai na manta da bacin raina na rungume ummi ina murna nima,mimi da sadam suka kwaso mun kayana muka k'arasa ciki.


***********
Zuwaa dabai wani canjin yana yine gareni,tunda ummi tagane inda ciki ta shagwab'ani,sai abunda nace inso zanci,tunda Allah yasa yah Areef ya ajiyeni ranar dana zo ban sake ganin saba, sai bayan kwana biyu shima kuma a daining muka had'u na gaidashi ko kallona baiba bakke ya ansa,raina yayi babu dadi ai tunanina yanzu babu sauran takun sak'a,sai yasaki ranshi muyi zumunci,Amman duk wannan bobbotan ban san ko nameye bah........har mimi tasan banji dadi ba ina daki mun gama waya da Dr yace daya gama abunda yake zai iso mukoma.
"Nazo ma dad I yya inba yar da hkr."
Harara na banka mata na juya ina danna wayata waje ta samu tana cewa,
"Bari Kik dalilin jin haushinki da yake,duk baki son sani."
Yinai kamar banson me take cewa ba amman kuma nan kunnena na saurarenta.
"Tunda yah yadawo daga bikinku kwance yake khairat,aikin da yazo yi saidai wani yake ashi shi,yafi wata asibiti anrasa gano kanshi.....yau sauki gobe ciwo,duk ya tashi hankulan mu Abbi kanshi kamar ya zauce akan ciwonsa,ummi kam wani sa in kuka take mashi akan ya tausaya masu yayi hkr da kaddara ita tasan duk dan bai sameki bane,to kanshi farau rashin masoyiya......wasu ma iyayensu suke rasawa duniya gaba daya sukuma hkr balleshi don kawai baisamu wacce yake so ba,to ita dayake tana jin maganar iyayanta kuma ta yarda da kaddara mai kyau da marar kyau ai gashi can tana zaune gidan mijinta lafiya lau bata dorama kanta wannan masifar ba,saikai kana namiji kakasa jurewa.
Banga anfanin kasancewarka namijiba Areef.
tunda har baka iya sadaukar da soyayyarka ga waninka,to ko kaki ko kaso khairat dai ta haramta gareka,kuma har abadan bazaka sameta ba,don ina mata fatan kasancewa da mijinta har karshen rayuwarta,don kuwa mijinta yafika sonta idan zaka tashi ka fuskanci gabanka to idan kuma nan zakai ta kwanciya bismillah ga wajenan iyaka abincine in daho inba kanwarka ta kawo maka, da kaci da karka ci uwarsu daya ubansu daya,wahalalle kawai."


"Gaban yah jahid lokacin ya biyo shi shima zaiyyi wani aiki nan,ina gefe nima duk ummi take fadar wadannan maganganun,koda na kalli fuskar yah wallahi khairat kuka yake amman babu sati saidai hawaye dake zuba,fita nai inbasu waje don naga yah jahid yana son magana dashi.........dama ummi tana gama fadan ta tafice rai b'ace.
Ina jikin k'ofar naji yah jahid yana lalashinsa,yana cewa,
"Areef ya kamata ka tashi hakanan,duk abunda ummi ta fad'a gaskiyane kaifa namijine kaine yadace ace kana yin juriyar da khairat keyi,barifa kaji itama fa badan tan soba,bata da yadda ta iya ne dasu Abbu........"karya take jahid bata sona shi take so.ya katseshi da fadar haka.
Murmushi yayi yace"kishinka bazai barka kayarda da haka ba,amman kasani itama tana cikin irin wannan halin,tadai fika juriya ne."
Wannan maganar ta sake har zuka yaya yace"shikenan aina an fad'a hakaan nai aka alkawarin baza sake kwaniya aka rashinta ba,ama abu guda da zakai mun shine kasanar dasu kar wanda ya sake anbata mun sunan ta gabana,,,,idan ba haka ba zasu neman su rasa,naji ma ni duk natsaneta wallahi banson maganinta yanzu,.....


Tun daga lokacin yah yadawo kamar bai taba ciwo ba arayuwa,saidai lokaci lokaci zaisha mgani saboda ciwon zuciyarsa.......ranar da kikazo dana sanar dashi ummi tace yaje yadauko ki kinga yadda ya har zuko man kamar zai makeni,aguje nabar wajen nai zaton bazai jeba sai muka ga yadawo tare dake.......tun daga ranar baya zama gia saidai gida uncle jabir (kanen su maah ne shine autansu shima baitab'a haihuwa ba)kinji haushinki da yakeji ."
Tsaki naja nace"ya dade baiji haushina ba angaya mashi ni tashi nake, ni ko tunashi banyi kimaji in gaya maki."
Dariya tayi tana cewa"eh gaskiya ne naga alama. haba mata wazaki maida shashasha kawaidai kina waskewa ne saboda kina da aure nima kuma zanso kina yin hakan,yadda yake shareki baya ansa gaisuwarki kema kibar gaidashin,hakan zai bashi haushi,saboda ke duk yazama dan bala,i wlh."
Dariya nai nace"dama shine wlh dama fitinannene ne,saidai kice karuwa yayi ninan nizan gaya maki masifarshi wlh.
Gyara kwanciya nai ina sake cewa"inyayi hkr na kusan tafiya don ma ummin tace saina k'ara sati wlh da da dr yazo zanbi mijina inkoma."
"To masu miji muma dai ai mun kusan yin auren adaina mana gori harda goruba."
Dariya nai mata mukahau wata hirar.


*******


Yau mukai da Dr zaizo ya ganni jibi mu koma ban ma gaya mashi cewar ummi ta kara man kwanaki ba ,sai yazo inyi maganar gabanta don daker zai yarda amman idan tasa baki zai barni.
Don nima ba son zaman nake ba don duk nima naji yasire man kamar yadda yace ya tsaeni yanzu,harma ni zaice ya tsana lallai ma koda yake kodacan ai haka yake nuna wa,ni baitab'a nuna man alamar yana sona ba inba ranar da zai bar garin ba.


Ummi bata nan tun safe ta fita tace sai yamma zata dawo,bata son dr yazo bata nan kar ya daukeni yace zaigudu dani bamuyi bankwana ba daroya duk mukai nida mimi.
Yah imran ne yakaita
Nida mimi muka shiga kitchen muna hada ma Dr abunda zaici idan yazo,kasamcewar mimi badai iya girkiba don du itatyi wasu abubuwan,ina dai taya tane.........juice kurun na had'a na kai frig din karamin falonsu.
Harda wani sweet cake tayi mashi,tace sairayinta Abukhalipa yana masifar sonsa wani irin cake ne yasha cream asamanshi,tace a frig take sashI sai yazo ma take fiddoshi don karyayi melting.....naji dadin sa sosai don saida naci miyauna kamar yayi tsartuwa.nasan kuma Dr zaiso shi duk na k'agu ya iso na yi kewarsa sosai.
Shima ga frig din na kaishi sanan nawuce nayi wanka,yanu banson yin kwalliya don ko kadan bansonta, saboda cikin anan doguwar rigace mai kama da jallabiya Dr ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login