Showing 54001 words to 57000 words out of 69834 words
mashi duk abunda nai,shine zata ce haka.
"Badake nake maganaba saudah karna sake jin bakinki."
Ta banko man harara nasadda kai ina cigaba da kukana.
"Bakiban ansa ba ta Alkairi."
Ina sharben majina nafara magana cikin rawar murya.
"Abbu maah ce..........sai kuka ya kubceman na tayin sa ina jan numfashi bai hananiba don daman kukan shine nakeyi nasamu sauki,
Saida nagaji nayi shiru nacigaba da cewa,
"Abbu bansan menayi mata ba,tun ranar da yah yatafi take daureman abu kadan taita hanta rata,kuma taki fitowa fili ta gaya man laifin danayi mata,inma don yah Areef ne wlh tallahi Abbu bana kulashi,ban shiga sabgarsa,shine yake damuna saboda ita ko maganar arziki bamuyi dashi.inbanda gaisuwa amman shine tace haka,wlh niban karya dokarkiba........na karashe ina kukana."
Ajiyar zuciya Abbu ya sauke yana kallonta cikin kallon tuhuma alamun ransa ya baci,
"Kin kyau ta saudah,yanzu da kanki zaki jefa wannan baiwar Allah kuka kijefata cikin kunci da damuwa,bacin wadda take ciki.shin kokin mance lalurarta ne saboda wani dalili can naki nabanza zaki ta kura ta,shin haramunne don ta so Areef,koko shi haramunne don y sota.kinsan dalilin ubangiji daya d'auke mijinta,kikasan hikimarsa nayi imanin saboda khairat rabon Areef ce shiyasa ya dauke mijinta,don shi yasameta.
Kifita sabgar Allah kifita lamarin ubangiji,kebaki isa kihana ba haka baki isa kisaba,don sai Allah yanuna maki ikonsa,babu ruwanki daga yau namaki hani da shiga tsakaninsu."
Maah cikin b'acin rai tace"yallab'ai ni ban isa shiga tsakaninsu ba,akwai abunda ya tunzurani har nake mata haka don tasama ranta babu ita babushi"
Wani kallo yayi mata yace"mekike nufi inajinki."
"Tun ranar dasukai hayaniya ita dashi Areef din,yaya ranta ya b'aci don tazo har d'aki ta sameni,cewa wai me khairat take nufi tana nufin har gobe tana kan bakata na son Areef,to ingar gad'eta don anriga angama komi kan batun auresa,kuma babu mai hana wannan auren na Areef,don tunda zulfa,a taga areef a UK take ma sonsa,kasancewar mahaifiyarta tasan ummin,sai tayi mta waya kancewar aikuwa yarta taga Areef ta haukace kanshi,babu wani jayayya tace insha Allah saiya aureta,mafarin taita taimakawa wajen ganin khairat bata auri Areef ba tun wancen karon.
Saboda taja mashi kunne kuma nima ta kalailameni da kalamanta har nayarda da ita.to shinefa ta sake jaddadaman cewar mai hana aurensa da zulfa,a sai Allah inmata magana ta rike jawarcinta.........wannan abun shine yafi komi yiman ciwo yallabai,ashe har yaya hafsa zata ki jinina saboda wani abun duniya,ciki daya muka fito amman ta ki diyata da d'anta,taya kake ganin zanji dadi hawaye suka cika idonta tab........sharewa tayi yayinda nima nawa kukan ya k'aru tace"wlh zanyi farincikin aurensu domin dukansu nice na renesu nasan halin kowa,amman taya kake tunanin zan yarda khairat ta cigaba da nacewa kan haka,dole tasa nayi mata haka badan komiba,kayi hkr banyi nufin b'ata ranka ba."
Rarrafowa nai na rike kafafunta ina kuka sosai nace"maah kiyi hkr don Allah kiyi hkr wlh tallahi zan goyi bayanki,nima na janye daga kan maganarsa,dama kuma ba kulasa nakeba bazan taba aurensa ba,inacin mutuwa mai tonan asiri taya zan kasance haka,,,,,,nacigaba da kukana.
Shiru yayi yana auna maganganun da ta gaya mashi,tabbas baiga laifinta ba domin kuwa ba neman kai suke da khairat ba,abune na gida wnda idan akayi kowa ziyyi farinciki,amman tunda hakane abarshi ahakan........
"Ta Alkairina,kinji duk bayanan mahaifiyarki,don haka banda abun cewa daya wuce kiyi hkr kibar komi hannun Allah,insha Allah zai kawo maki wani wnda zakiyi farinciki fiyeda tunaninki,fatana kiyi man Alkawarin kiyaue dokokin Allah,kifita sabgarsa tunda daman kince baki kulasa,to atai ahaka inso samuna ne kitai waje ki idasa karatunki."
"Aa abbu zanso in zauna kusada ku,nai maka alkawarin kiyaye duk abunda kace."
"Masha Allah haka akeso,Allah yayi maki Albarka."
Nace"Ameen Abbu ngd,maah kiyi hkr kiyafe man don Allah banajin dadin yadda kike man kihi hkr pls."
"Babu komi ya wuce kidai kiyaye,don zamu sab'a inhar nasake ganin wata hudda ta hadaki dashi,kina iya tafiya."
Natashi na dawo cikin gida ina wondering halin ummi,lallai mutun ba abun yarda bane,taban mamaki banyi tunanin haka daga gareta ba.
*********
Shirye shiryen biki ake bakama hannun yaro,don ankai lefen yah shahid gidan su husna,ankuma anshi na yah meenah itada yah harun,dayake bayan da wowarmu daga dubai ya koma saboda aikinsa,amman tare zasu dawo da yah Areef.
Hidima ta nake kamar babu wani abu cikin raina,nan kuwa karkaso ka bincika karfin haline kurin da juriya.
Shima ankai nashi lefen amman saboda basusan darajar mutane ba suka wulakanta y'ankai lefen,har kuka maah tayi saboda yadda aka anshi kayan cikin renuwa da wulakanci,wai ai yarsu tafi karfin wannan yame yamen.
KO zinari babu balle gwal,saikace ba yar minister kudiba,,,,,,,bayan akwati goma sha biyu haka aka cika da kaya,wanda maah saida ta cika akwati bakwai biyar ne kurin ummi tayi mashi,ita kanta ummin ta tsargu sabida yadda taga maah tayi masifar canza mata,ba kamar da suka dawo daga kai lefen taje har falonsu ta sameta tace.
"Munkai lefe yaya hafsa,ankuma wulakanta mu kamar yadda kikazata an watsamana kudin tukuici a fuska,ance gashinan suba mata lauta bane da arzikinsu idan da munsan bamuda arxikin yi mata lefen,da munfad'a bazasuji komi ba don sun ranta mana,ummi ta kadu dajin irin abunda yafaru,tana kermar murya tace"wlh saudah bansan haka sukeba..........kinsani yah hafsa,wlh kinsani aibatun yau kike tare da hajiya safara,un ba,i think tun bakiyi aureba.shine kike son ansar yarsu matsayin surikarki gidan da ba,asan drajarmu ba ba,sa kimrmuba basusa mutunci da karamciba,no problem gashinan ayi mugani,amman kisani bazan sake shiga cikin wannan hidimarba wlh tallahi kau."
Ta juya ta fito tabarota.
Jikin ummi yayi masifar sanyi sosai,don kuwa maah tayi buris da lamarinta,duk zafin ummi da fadanta ta koma kamar ruwa yacita,maah kuwa tayi fushi sosai abunka ga wanda bai saba irin wannan fushinba.......gidan duk yazama babu dadi wajen annie kurun nakejin dadi,duk da maah din ta sauko tabar fushin dani,amman kodayaushe bata da walwala don Abunda ummi yayi mata yayi bala,in daure mata kai.
Airah tayi wayau sosai don watanta uku yanzu,dariya kamar gonar auduga wadda kuwa halin mahaifinfa,tana girma kyanta yana karuwa.
Tuni muka gama wanka Annie ce kegyarani kamar wata amarya,har kunya nakeji tace aiba dole saika tashi aureba,dole kazama cikin kulawa don kowane lokaci mijin na iya zuwa.
Jinta kurin nake don ni bawani aure dazan sake,rainon diyata ya isan da karatuna,don tuni nakoma yanzu ma IT muke nan wani private ne,wani lokacin gida nake barin Airah,don bata barina aiki idan anyi sallar azahar indawo inbata nono tasha,naba yah meenah ita don sun kammala nasu tuni,don ma tanashan priso tayi wata irin kiba gwanin sha,awa kyanta sai sake bayyana yake kowa yaganta yayita santi,gata da shiga rai,kuma bata rigima sai idan yunwa takeji ko kuma bacci.
Tunda ya tafi na sauke layin sayasanni dashi,don ma karya kirani balle wani sakonsa na banza,bawai har cikin zuciyata inajin dadin abunda nake ba,banda wani solution daya wuce haka,babu anfanin inta saurarensa inasaka kaina cikin shaukinsa,soyayyarsa mai girmace cikin zuciyata inhar inajin muryarsa,bazan iya control din mind dinaba shiyasa mafi a,ala in nisanceshi.
Agajiye na dawo yau Airah naga nina taita mik'o hannnu,hararata nai ina cewa"acici ko hutawa baki barina inyi to kwalelenki yarinya,nai mata gwalo."
Kamar tasan menake cewa ta fashe da kuka,dariya nai zanruga mimi ta rikeni,
Annie face"wlh bakishiga saikin bata,muguwa kibar yarinyar tun safe yau ko dawowar dakike bakiyi ba,shine kuma bazaki bata hakkinta bakini tsoran Allah."
Dariya nai ina harararta itako sai miko hannu take,
Ansarta nai mimi nacewa"Allah zai saka maki babynah."
Yinai kamar zan maketa taisaurin matsaw.
Saida nabata sannan na mikata ga mimin nashige ciki,don tafi yarda dasu itada yah meenah da Annie.ko salma bata son taje wajenta.
Wanka nashiga najiyo wayata nata ihu bafitoba saida nagama,lokaci kuma ta tsinke kaya nasa nayi sallar la,asar ina sallamewa aka sake kira.
Dauko wayar nai babu suna aman da alamun daga wajene,harga Allah ban tunanin shi bane na d'auka nace.
"Assalamu alaikum."
Shirune yabiyo baya nasake maimaita sallamar,
Sai sannan akai magana cewa,
"Baki tausayina khairat...........daskarewa nai inda nake don kuwa tunin duniya na gane shi......so nake na yanke wayar amman hannuna ya kasa,zuciyata dokawa take kurin inajiyo numfashinsa ahankali kamar wanda baida lafiya......jinai yace"pls dr ka sallameni wlh nagaji da asibitinnan haka."
Silalewa nai bakin gado nazauna kasa,inajin kwallah na cika idona......cikin rawar murya nace"yah .......bak....bakada lfy ne."
Mrs bb ce
Mom muhseen.
0934722970.
Share it plss
[7/7, 6:36 PM] Mom Muhseen: 💕💕💕💕💕💕💕
🌹
*ABIN CIKIN RUHINA*
Writing by mrs bb
Mom muhseen.
Wattpad name
Humaira7531.
DEDUCATED TO ZAUREN MRS BB.
48.
Hawaye share share fuskata kamar ankunna famfo,numfashi ya sauke baice mun komi ba duk hankalina inyayi dubu yatashi,
"Don Allah kayi mgn bakada lfy ne,meyasa baka sanar agidaba plsss kadawo gida hakanan,anan babu mai kulawa dakai........"
"Idan ma nadawo karaman wani ciwon zakuyi,no need for that Zan zauna anan inmutu kinga kowa yahuta."
Kuka nake sosai nace"Aa yah kabar cewa zaka mutu,don Allah kadawo gida akula dakai sosai insha Allah yadda kake tunanin abun bazai faruba."
Lumshe idonsa yayi yanajin wutar kaunarta na sake ruruwa cikin zuciyarsa,dafe xuciyar yayi yace cikin low voice dinsa,datai sanyi kamar kankara.
"Kina so indawo."
Ina share kwallah na silale kasa na kwanta ina kuka k'asa k'asa daker na fizgo maganar nace,
"Eh"
Sassanyar ajiyar xuciya yaja yace"ki ansa man abunda zan tambayeki."
Numfashi kurun nake ja saboda yadda nakejin kaina,banson meyasa zuciyta take man haka ba,inhar akanshine bana iya dogon fushi duk yadda nake son nisanta kaina,dana ganshi ko naji muryarsa dandanan zuciyata zata koma kamar ruwa.............daker nace "uhh"
Shiru yayi tsayin lokaci banda numfashinsa bakajin komi,lumshe idona nai ina sairaren yadda yake sauka cikin kunnena,hawaye na silaloman inajin sabbin feelings akansa..... ..........
*"sweetheart!"*
Jinai duk tsikar dake jikina tana tashi,muryarsa tana ratsa duk wani lungu da sako na jikina still hawayen basu bar zuba ba,na kasa ansa kiransa saidai ajiyar zuciya da fizgar numfashi nake..............jinai ya sake cewa.
*"sweetheart are u on d line!!!"*
Wayyo Allahna duk'unk'unewa nai waje guda ina shashsheka,jikina yayi masifar canzawa kadaddabe wayar nayi ina murtsike-murtsike.............bakina yana rawa nasake cewa "uh"
Numfashi ya fesar wanda yasani runtse idona ina jan numfashi,iskar dakin jinake taimun kad'an.
*"did you love me?"*
Cikin wani irin yanayi na cire wayar daga kunnena na kasheta duka nai switching dinta off.
Wurgata nai kan gado nazauna nadunga gurzar kuka kamar Allah ya aikoni,can lungun bayan gado nashige kamar wata mage,nai mamakin yadda har na shige wajen.
Sosai nake kuka don uku biyu ya hayeman,ga haushin kaina da tsanar halina nara shin zuciya da banayi akansa,ga soyayyarsa kaunarsa shauk'insa sunmun taron dangi,ga gargad'in maah yana amsa kuwwa cikin kunnena kamar yanxu take yiman shi,,,,,,,shin yazanyi da raina ina akeson insaka rayuwata ne wai,yazanyi.........yazanyi ya akeson inyi.............ne.........na fashe da wani irin kuka mai tab'a zuciya......kamar wata zararra nikad'ai naketa magana ta.........waini na dorama kaina ne ehy,Meyasa har yanxu nakaa samun farin ciki dorarre,wannan masifa ta isan nagaji nagaji nagaji...........mimice tashigo da Airah nata kuka rage sautin nawa nai inajan ajiyar zuciya......."subhanallahi,khairat lafiya kukan me kike kinga yada fuskar ki takoma?ansarta bata tasha garin rarrafe ta k'umeka da table."
Ansarta nai na ciro nonon nabata ina tsane fuskata da kallabina,zama tai gefen gadona tana cewa"komi yayi zafi maganinsa Allah,kibar dorama kanki damuwa karta zo ta haifar maki da wani abun nada ban."
Cikin kunan rai nace"mimi wallahi zuciyata ta fara gajiya da daukar k'unci,inajin kirjina yana mun nauyi,narasa ta inda zan kama duk inda naje babu sauki,yanzu yayanku yakirani baida lfy banyi niyar saurarensa ba amman wlh mimi jin muryarsa duk ya ruguza man komi,tabbas duk wani kwane kwane da nuk'u nuk'u nawa,insonsa banda wani burin daya wuce mallakarsa,amman mimi akwai katanga tsakanina dashi,katangar mai tsayice bazamu iya ganin juna ba sai ankaudata,kinsan komi ya faru kinsan kuma sharad'in maah gareni,cewar muddin nacigaba da kulashi inta kamani inkuka da kaina.karma intunanin zata saurareni,shikuma ya huraman wuta yace bazai dawo ba saidai ciwon ya kasheshi acan,niban tab'a ganin bala,in *SO* irin namu ba taurin kai ya hanashi ya furtayana sona kuma bazai iya cewa yafasa wannan aurenba,shin ki fad'i man yazanyi.............duk yadda nakai ga sonsa da kaunar kasancewa dashi wlh mimi abun yafi karfina,bazan iyaba..........nafashe da kuka.
Iyakar tausayi khairat tabawa mimi don ita kanta saida taji hawaye sun zubo mata,wai meyasa ummi tacika son ranta,yanzu ko tausayi basu bata,shi yanacan rai hannun Allah ita gatanan bak'in ciki zai kassarata cikin d'aki duk wannan bai isa yakai ta dakayar da auren ba,Dady baida wata damuwa inhar tace abarshi zaiyi mirna,don shima baso yake ba miye aibun khairat duk wanda yaganta idam ba yaga Airah bazaice iyace uwarta ba,don babu abundan ya canza daga gareta.
Lallashina mimi keyi tana ban hkr tare da karfafaman guiwa,dayin addua hakanan naji koba komi nafadi damuwata nasamu relif.
Biki yataho yau yah imran ya iso kowa yayi mamakin rashin ganin Areef,wanda ni nasan daman bazai biyo shidinba,tunda shima yagaji taurin kai irin na uwatai.
Ita ummin aitasan bai lafiya amman sabkda karma ace afasa auren yasa bata sanar da dadynsu ba,saida yah imran d'in yadawo yake gaya masu cewar ai yana can satinsa biyu kwance bakda lfy,yace kua bazai dawo ba har sai idan na amunce aurensa..........kowa yashiga shock jin cewa. Baida lfy kuma serous serious sick ne.
Dadyn su yaita fada yana cewa audaman Areef nason khairat baitab'a saniba,nan maah ta bashi labarin komi yadda ya faru abaya,da kuma abunda ya faru cikin wannan kwanakin..........kamar zai ari baki yaketa banbami ummi tayi sukuti kai k'asa,ansar no din dayake anfani da ita yayi wajen imran yashiga kiransa.......saida yakira sau uku sannan ya dauka baibari yace komi ba yahau fad'a,
"Don ubanka karka bari jirgin karfe goma ya taso baka biyoshiba jibi,ashe kai sakaran banza ne loton banza,da wofi kana sonta baka tab'a gaya man ba,kabiyewa sakarar uwarka to karfe biyu na rana ina tsumayinka gidannan dolon banza,har kake kwance sharaf kan mace maimakon katsaya kai fighting love d'inka katsaya dolanci."
Lumshe idonsa yai yanjin abunda mahaifinsa ke cewa,kokadan zagin bai damunsa wani dadi ma yaji yana kwarara cikin ransa,yau zaiga ABIN CIKIN RUHINSA ganinta ma kadai ya isa ya kwantar da gobarar dake ci cikin zuciyata.
Daker ya lalubo kalmar cewa"insha Allah dady kafinan ma zan iso zan biyo jirgin Abudabi zaisauka abuja karfe daya."
Tsakiyaja yakashe wayar yana cigaba da fada Abbu da dadyn yah meena keta bashi hkr,nidai daman anafara maganar nabar wajen naga yada za,ai atursasani kuma yanxu don wallahi duk da nake jawara babu wanda zai sani auren mai mata.
Yau biki saura sati daya duk munyo dinkunan mu anko kala biyar,less guda biyu atamfa daya sai material da shadda kamfala gizner..........inda naji dadi ummin su dr tazo tatai da Airah,sana waje aikina IT anbani hutun sati biyu,nasaki jikina munata shige da fice gyaran jiki muke zuwa nida amaren,hada salma don itama maah tace taje aimata ai kwatsam tana iya koma gidan mijinta,wanda har yau baizoba babu kuma wanda yasake bi takanshi ma balle yadamu,dukda ita dole tadamu tuna tana sonsa.
Dawowar mukenan daga gidan k'unshi,nida su mimi,yah meenah.anty shida can itadasu kawayenta suke hidimarsu,bama nan gida suka zaunaba sunacan gidan wata kawarta.
Husna kuwa tanan amman b'angaren Annie,anshirya event dinner da kamu sai bridal shower.
Inkagannni zakai tunanin nima ina cikin amaren,sabkda yadda na murje nakoma wata yar 18 yr harabar gidan cike da motocin bakin biki,saidai zagaye mukai tacan baya,don akwai hanyoyi dayawa cikin gidan,dariya muke saboda mimi datai sabon saurayi wani kamar almajiri,sai dariya muke mata.
Ita kuwa sai fad'a tana cewa"wai kinga hakoransa wlh kalarsu kalar yellow din shaddarsa yar dubu biyar,shiko kunya ma baijiba wai nagankine miyauna yaguda,don uwarsa kamar yaga tsire ko balango."
Dariya kurun nake harda rik'e ciki jinai kawai nabanki mutun, cikin sauri nad'ago idonsa cikin nau..........mimi tace"laaa yah yaushe ka iso,sannu da zuwa."
Kai kawai yad'aga mata suma duk suka gaidashi suka shige,bansan tsayuwar uban da nakeba, naja dogon tsaki narab'ashi zan wuce,wata irin fizga yamun yajinginani da bango.......idonsa har ya kad'a yayi jaa.
"Rainin har yakai haka,nizaki kallah kiyiwa tsaki."
Banyarda nasake kallonsa ba naketa kokowar kwayar kaina,
"Kasakan man hannu zakajiman ciwo fah."
Yatsansa yasa ya d'illi bakina "bazan sakiba kin rainani ko,bama ki mjrnan nadawo kodan ..........saikuma yayi shiru na dallabmai harara nafizge hannuna saida nakai kofa nace"meya hana kazauna can har mala,ika azara,ilu yasameka." Rugawa nai ahuje ina nishi don karya kamoni don yadda yanade hannun riga inya kamani bazanji dadi ba.
Dariya yayi yana jin wani dadi cikin ransa atleast dai yaganta kuma zaita ganinta har agama biki,wsta xuciyar tace to in angamafa kaida kayi aure............tsaki yaja ya wuce don yana da baki waje zaije ya kama masu hotel.
Yaune za,ai bridal shower,kawayenmu duk sunzo anata hidima da shirin fita ,don duk anan zasu shirya ni busy ma nake saboda yah imran ya sani aikin take away na bak'insa,inacan dakina nida mimi tana tayani,waya uke da ummin dr taa ban lbrn Airah,sai dariya nake tace ai gobe daren biki tare zasu zo,mungama wayar na ajiye ganin munkusa gamawa nace ma mimi.
"Bari nayi wanka sandda zan fito kingama saina shiryasu cikin wannan babbar ledar,don waccen bata daukewa kema saiki je kiyi arfe biyar zasu zo daukar amarensu,muda bamuda mazan kinga saimukai kanmu."
Dariya tayi yace"karki damu Muma very soon zamu shige daga ciki tsaki naja ina cire kayana nadaura towel,nace"saidai ke ko,tunda naga wannan hamdanan agaske yake.nafad'a ina dariya ita tasan wanda nake nufi aikiwa tab'ata fuska.
"Wlh inajin nauyinki oum Airah,kodan arzikin haihuwar babyna dakikai."
Dariya nai nace "sorry mu k'anwa nadaina nima d'anawa naibari nashiga saina fito."
Wankan nashiga nayi kasancewar ina da dadewar wanka nakusa awa sannan na wanke jikina dayake da shawer nayi kaina yajike nasaka towel din dana shiga dashi natsane kaina,nadan bud'e k'ofar namik'o hannuna nace,
"Mimi akwai towel din Sweetie nanan kan net dinta banshi indauro wannan yajike wlh,........mik'omun akai na ansa na daura ko cinyata bai rufeba don daker ma ya rutsai,mistakenly na duka tsaf zai kunce fitowa nai ina cewa"yaudai ban jimaba karkiyiman complan plsss.....................ido hudu mukai dashi yana zaune kan stool din miroow.........idonsa ker kaina baki na rufe ina zaro ido,,,,,,,,,,,,
_*ABDOUL-NASSER (ALFAH) COMING SOON INSHA ALLAH LABARI DAYA SHA BANBAN DA SAURA,KARKIBARI ABAKI LBR*_
Mrs Bb ce
Mom muhssen.
[7/8, 2:10 PM] Mom Muhseen: 💕💕💕💕💕💕💕
🌹
*ABIN CIKIN RUHINA*
Writing by mrs bb
Mom muhseen.
Wattpad name
Humaira7531.
DEDUCATED TO ZAUREN MRS BB.
49.
"Haba don Allah wannan badai dai bane,yazaka shigo babu neman izni."
Ganin