Showing 27001 words to 30000 words out of 130351 words

Chapter 10 - MAHABEER Complete Document by Xayyneb.txt

Xayyneb   

29 Jan 2025

9973

ita "sorry matas close your chapter,,
"ai dole kace abar mgnr inda na ta6o maka maganar aure wacce baka so ko?
kai nifa wlh bari kaji inka fi qarfin d'anda da maima toni baka fi qarfi naba,, wlh rass inka cikani nida kaina zan iya aurar dakai ga wacce naso a cikin dangi na had'aku aure,,,
baisan sanda kalmr "iyeeeeee ta66666,,," ta fito daga bakin saba ba shiri,,,
"oh kanaga bn iyawa knn ko?
Gimmm yayi da fuskar nan kuwa tasa yana magana da cewa "no Anna i'm not say fa,,, amman dai aurar dani annah kamar wata mace?????
dai dai nan suka shigo cikin gidan annah tayi fitarta daga motan ko qala bata sake ce masa ba,,, zamansa yayi a mota yana gunguninsa da cewa"ka jimin fa wannan old woman d'in dan Allah,,, ita komi aure aure??
tsut yaja tsoki siriri ganin wayarsa na lighting ne na plash yasashi duba me kiran nasa,,, bleesing ce yagani,,, daga wayar yayi yayi shiru yayinda yake danna dayar wayar dake hsnnunsa yana type,,,,
Jiyayi tana fad'in "halo halo hello my??
You are hear me???
"a daqile yace "yeah,,
Murmushi na ajiyar zuciya ta sauke tace "huhhhh my pleasure ,,morning my,,,, hope all well my,,, ???
"5n"
Ohkk my yaushe zanzo hospital d'in ganin mommy na ban san a sallameku kafin nan?
Wach d'in hannun sa ya kalla yaga 7:22 sadda ya dan ta6e lips dinsa yace
Kibarshi at a 9 o'clock,,,,"www thakns my innazo saina kiraka ka shigar danid cikk dan ban san room d'in ba,,
"better,,,,,,
,,, ,, till you come,,,,
hang up yayi na wayar sannan ya kashe motar ya kwantar da seat yai kwanciyar sa a motar batareda yabi annah ciki ba,, dan baisan mgnr da zata qara daddago masa ba,, ear pies dinsa yasa a kunne Yana jin music idanunsa a lumshe,,, yana nan har annah tagama shirya breakfast dun ta fito dashi ta shiga motar yatashi ya ja motar suka koma asibitin,,, suna shiga room d'in suka tadda har mommy umaima din ma ta farka ma.
Mahabeer gefenta ya koma ya zauna yana fad'in "momy ya qarfin jikin?.
Murmushi tayi tace
"jiki Alhamdulilla yy sauqi mahabeer na,, Annah kuwa ta fara bude kayan breakfast d'in ta hadawa momy tea ta miqa mata ta fara kur6a sannan ta cika mata plate da chips,, jin qamshin chips din ne yasa momy umaimah taji zuciyar ta wani motsa mata kokaci daya,, nan da nan kuwa ta fara kakarin amai tana alama da hannunta alamun annah ta rufe chips d'in batta son jin qamshin sa,,,
cikin tausayinta annah ta rufe dan tagane nufinta,,,
sannu suke mata kawai,,, zuwa lokacin ta daina qoqarin aman nata ta koma ta jingina da pillow tana maida numfashi a hankali,,,,
tea dinma mahabeer ta miqawa dan jitake bashi take buqata ba,,,
mua'zzam nema da annah sukaci chips d'in mahabeer shi ruwan tea dinma kawai yasha dan yanada qyami na launin mashaqar iska na asibiti shi,,,
Mua'zzam saraki nr sukaji yana amsa wayar tasa da cewa "eh room dinne freand kamar yanda nace makan,,, eh ku shigo kawai ina ciki,, yana kashe wayar sukaji anturo qofar,, idanunsu naga qofar dukknsu dan dubn mai shigowar,,,,
Alhaji Muhammad ne a gaba sai ni'ima matarsa na biye dashi a baya,,,,,,,



Fasaha online writers f.o.w. 📘🖊


*Xexen Fasaha*✍🏻
[10/11, 2:46 PM] Xainab Documen: 🌊🌊🌊


*MAHABEER*!!!
🌊🌊🌊


Story and writing
by
Xayyneb 💤💤


🌊🌊🌊🌊🌊


Fasaha online writers f. o. w.


*Kyautar wane gareki pg d'in nan my mom sadeeq.... (hawwas) Allah barmun ke cikin cigaba da kasantuwa tare a zumunce har muddin rai Aminnn*
🌊🌊🌊🌊🌊
🅿2⃣2⃣.
🌊🌊🌊
Rungume juna sukayi Alhj Muhammad da mua'zzam sarakin suka zauna a kan kujerar wajen bayan gaisheda annah da sukayi sukayiwa momy ya jiki ta amsa musu cikin kulawa da murmushi,,, zama tmomy ni'ima tayi kusada Momy umaima suka riqe hannun juna cikin murmushi da maganar yaushe gamo,,,
Mua'zzam saraki yace
"haj Muhammad ashe madam ta dawo nigeria???
dubn ni'ima alhj Muhammad yayi yaga hankalin ta gaba daya ya tafi ga kallon saurayin d'an abokin nasa kamar ynda shima yayi gamdakatar da hakan tun farkon ganinsa dashi,, amman ya danganta hakan ne kawai da jinin yaron ne burge jama'a da cikar qwarjininsa,,,
Murmushi yayi ya maida kallon nasa ga mua'zzam sarakin yana mai cewa"eh da safen nan ta sauka jia dama dana kar6i keys d'in gidan tun jia aka gama shirya komi na gidan shiyasa anan ma ta sauka bayan daukosu air port da nayi da qannen mamanta 2 wnda muka kaisu airport ynxu suka wuce mukuma muka yo nan ganin patient,,
"Allah sarki an gode ay Muhammad da ni'ima Allah bar zumunci dai"
cewar annah,, ciki girmamawa dady Muhammad yace
"annah ai godia tame ce waku,,,
sake dubn ni'ima alhj Muhammad yayi yaga still rabin hankalin ta naga mahabeer jitakeji a a lokacin ita wani irin qaqqarfan abu na mata yawo a ckn jinin jikinta gameda shi yaron nan take,, wnda batasan miye shi ainahin abin ba sam sam,,
Alhj Muhammad da dai yaga tayi zurfi sosai hakan yasa shi katse tunanin nata da cewa, "ni'ima ta?,,,
ahankali ta sauke idanunta kansa batace komi ba taji yaci gaba da fad'in "shine yaron da nike ce miki babban d'an hj mua'zzam nawa,,, kuma mai sunan yaronmu *mahabeer*,,,"
jitakeyi kamar ta saka kuka ni'ima na ambato mata tsohon mikin da yayi na ambato sunn danta tilo daya data rasa a duniya, bata sani ba shin yana raye koko ya mutu bata sani ba,,, qoqarin danne damuwarta tayi dan tayiwa mijin nata alqawalin daina zubda qwalla hakanan kan mahabeer suci gaba da roqan Ubangiji Allah ya bayyana masu shi zai fi,, kuma basu fidda ran sake samun wani d'an ba a duniyar nan ta maliki yaumiddin indai ana kwana ana tashi...
murmushin qarfin hali ta saki tareda yafito mahabeer da shima idanunsa suka sauka kanta lokacin yana murmushi wanda shi kansa baisan dalilin murmushin nasa ba, yadaiji matar qawar momyn tasa ta burgesa har a cikin jininsa yaji sonta kwatan kwacin irin wanda yakewa momynsa umaimah kuwa,,,,
har kusa da ita yaje ya zauna shima hsnnunsa ta kamo ta riqe da hannayen ta biyu cikin dubnsa da murmushi tace
"ina son mai sunan nan naka d'ana,, kozaka riqeni a matsayin momynka nima ka riqa dan d'ebemun kewar yaro na mai sunan ka????
Kallon ta mahabeer yakeyi fuskarsa a sake sosai yana murmushi yace
"eh momy na"
dariya annah tayi cikin son tsokanar sa tace "kayya dai ni'ima,, bakiyi dacen yaro ba dai nikega,,,
dubnta mahabeer yayi fuskarsa a tur6une jin annah na shirin kwafsa masa a zuciyarsa addua yake Allah sa kada annah ta fad'i abinda zai sashi yaji kunya a gaban wadannan mutanen,,,
murmushi ni'ima tayi tace
"komi yasa haka annah?????
Annah ta 6alli goronta ta tauna sannan taci gaba da cewa"ah to inma zaki barwa iyayensa abinsu suda suka saba da halayensa su ci gaba da jura,,
Kamar yai kuka ganin momy ni'ima tayi sakayau tana kallonsa dan son jin qarin bayani daga garesa,,,
kauda kansa yayi ya maido dubnsa ga su Dady mua'zzam da suke can gefe suna ma firarsu kan tafiyen alhazawan bana.....
dubm annah yayi sosai yace "to annah basai ki fad'a mata abinda nike yin ba,,, yayi maganar a raunane harda langwabe kansa yana dan muri muri da idanunsa,,,
"yanzu kuwa zataji,,,
Hannunta annah ta daura bisa kunnen mahabeer ta riqe tace "Kingansa nan ni'ima kunnen qashi ne da dan nan naku yakai munzalin da za'ace ya ajiye nasa iyalin shima amma sam ya q'iya babu abinda ya sa a gabansa face fad'in rai da shegen muskilanci wannan wannan da kikeji da gani ba qaramin dan ban haushi bane ja'irin mutum kawai tazuru,,
Qarashe maganar tayi tare murde masa kunnen sa,, sannan ta saki.
wata 'yar siririyar qara ya saki sannan ya dafe kunnen nasa dake masa zafi zafi na matsa da yasha daga hannun annah yana fad'in kai annah kinawa wifey na kishin ta ganni da kunne 2 ko sai daya?
Annah tace "eh qwamma in cire kunnen naka ko wannan liqaqqiyar yarinyar nan taka ka rage farashi a kn idanunta,, murmushi yayi su momy umaima da momy ni'ima dariya suke musu kawai dan sun fahimci salon nasu wasan na jika da kaka ne suke ta6awa.
Momy umaima ta bude baki knn da nufin yin magana taga shigowar ummi hani wacce tun tashin su yau ta je ta wanke kwanikn abinci acan baya inda ta saba wanki sannan ta jira har lokacin da masu kawo kalacin suka kawo ta sauka ta siyo musu suka sha,, sannan doctor lurwan yayi musu bayanin cewa zuwa gobe insha Allah ne zaa basu sallama,,, dayake dan iska ne har gefenta ya matso inda take ya yi mata magana qasa qasa da cewar yana nan kan bakansa fa shi ita kawai yake jira,,, ganin bai samu fuska bane kwata kwata tayi kamar bada ita yake ba saima matsawa da tayi wajen mommon ta tana mata gyaran gashin ta daya sauko saman katifar gadon da take akai,, ganin babu sarki sai Allah yasa shi ficewa yabar wajen nasu,,
bayan fitarsu ne baffanta da ita bintey d'in taji suna tattauna kan batun sallamr nasu da doctor d'in ya ce gobe gashi basu da taqamaiman masauki bare akai ga batun neman aiki,, ita kanta abin ya dameta hakan yasa ta tashi ta fito nan harabar wajen tana tafiya wanda ita kanta bata sanin mike mata dad'i a lokacin,, tunani kawai ya mamaye zuciyar ta na yanda zasu samu mafita itada iyayen nata,,
dai dai room d'in su momy umaima d'in ta tsaya tajima Tana tunanin ta shiga gaisheda mutanen kirkin nan kamar ynda tai musu alqawalin leqosu ana gaisawa koko??
girgiza kai tayi ta dan ja da baya tana girgiza kai alamun a'a. sam ita battason shsshigewa irin mutanen nan masu abin hannunsu tana gudun akirata kwadayayyiya a rayuwarta ita,, bata son wulaqanci bata jurarsa akan abinda tasan ba tanada gskia akan sa,,,
Harta juya ta fara tafiya taji wani 6angare na zuciyar ta na cewa ''a'a ummu hani ai ba duka mutane aka taru aka zama daya ba,,, bare ma su wadannan mutanen masu karrama dan adam dudda suna da arziqi amman su babu ruwansu ga alama kowa nasu ne,, kije ai har ga Allah ba akan nufin wani abu bane zaki shiga dan dai kawai gaisawan ne kamar yanda kika maganta musu,, batason rashin cika alqawali shiyasa knn ta shiga room d'in cikin qwarin gwiwarta,,,
sallamr da tayi ne yasa suma sauran wato su dady mua'zzam Duknsu waiwayowa da hankalinsu gareta, inka dauke momy umaima da dama itace ta fara ganin nata tun farkon shigowar nata room d'in,,,,




Fasaha online writers f.o.w. 📘🖊


*Xexen Fasaha*✍🏻
[10/11, 2:46 PM] Xainab Documen: 🌊🌊🌊


*MAHABEER*!!!
🌊🌊🌊


Story and writing
by
Xayyneb 💤💤


🌊🌊🌊🌊🌊


Fasaha online writers f. o. w.


🌊🌊🌊🌊🌊
🅿2⃣3⃣.
🌊🌊🌊
dukkansu suka amsa mata sallamr nata, ganin ynda take ra6e ra6e ne na rashin sabo da jama'a haka,, ganin haka da takeyi ne yasa mua'zzam saraki cewa"ah matso kusa da momyn taki mana 'yata kinga ta qagara ki matso wajen nata inda har ta miqe zaune,,,
yayi maganar fuskar sa sake a cike da annuri,,,
matsowa tayi kanta na sunkuye still ta qara gyara zaman mayafinta a kanta dan jin ynda gashin kanta mai santsin gaske da yawa yana shirin zamesa,,,
gaisar da kowa tayi cikin dakin sannan ta qaraso wajen momy umaima tana shirin zama qasa momy umaima tayi saurin riqo hannunta cikin murmushi tace "aa zauna kusa da yayanki 'yata,, ita sai lokacin ma ta dan dago fuskar ta danjin wani qamshin turare wanda yake mata gizo da kamar tasan mamallakinsa,,, a hankali ta juyo gefen inda takejin qamshin turaren ta sauke idanunta kansa wanda mahabeer yayi mutuwar zaune yana kallon yarinyar dan tun shigowar ta yagane ta,, mamaki ne cunkushe a zuciyarsa gameda yarinyar daman su momyn sa sun san tane koko???
a hankali suka zame idanunsu daga cikin na juna zuciyar kowanen su na bugawa d'al d'al d'al,,,, batareda sanin haqiqanin abinda yajaza musu hakan ba a iyakacin tunanin su a lokacin,,,
ba qaramin girgiza ummu hani tayi ba na ganin wannan mutumin dan zafi anan dama sune iyayensa ashe???? Amman kuwa indai haka ne tohm albasa batayo halin ruwa ba,,,,
annah da taketa kallon yarinyar tun shigowar ta wajen takega kamar tasan ta amman ta rasa inda tasan ta,,, saida ta qara kallonta sosai yanzun data zauna sai lokacin tace"ahoooo yarinyar kirki kece Ashe? cikin kunya da d'ari d'ari ummu hani ta d'ago ta dubi annah dan itama sai yanzun ta ganta,,
Murmushi tayi tace
"hmmm'''
annah ina wuni,,
Annah tace fa?? cewar mahabeer a zuciyarsa,,, knn ma har tasan suna ce mata annah??? baisan cewa ba a yarensu dud wacce ta take a matsayin munzalin uwa ba toda haka suke kiranta,,, mafarin knn Ummu ta furta sunn kai tsaye da sigar girmamawa kamar yanda ta saba ita ga kowa,,,
Jiyayi annah tace "lpia lau yarinyar kirki,,, haba sai tunani nake inda nasan na ta6a ganinki ashe silar wancen tuzurun mijin nawa ne,, tayi maganar tana mai nuna mahabeer,,satar kallonsa ummu hani tayi a lokacin taga yawani had'e rai kamar yasha mad'aci girar nan tasa baqa sidik mai kyawun gaske harta kusan gamewa da juna,, idanunsu na qara sauka ana juna lokacin a karo na 2 knn a shigowar ta ya wani watso mata harara a qasan idanunsa yanda bakowa ne zai fahimci hakan ba face wacce akaiwa,,ganin hakan yasa ta mayar masa da yatsina fuskarta da irin kallon nan daya tsana tai masa irinsa wato irin na kai kuma fa yadai????
Momy ni'ima cikin murmushi tace "hjy umaima wannan buzuwar fa 'yan uwa ne??
nan momy umaimah ta fad'a musu tun farkon ganinta da ummu hani harya kawo yanzun,,, nan dakin kowa yaita tofa albarkacin bakinsa ga zancen,,, mahabeer kuwa kya6e lips dinsa yayi lokaci daya kuma kiran bleesing dinsa ya shigo wayar bai daga ba ya miqe yacewa momy umaimah zaije waje ya dawo yanzun,,,
Momy ni'ima cikin murmushi tace "to saika dawo,,,,itama abinda momy umaimah tace masa knn sannan ya fice,,
sai jan ta da fira annah take dasu momy umaimah na ganin ta saki jiki dasu amman inaaaa har lokacin gimm take komi nata a sanyaye haka take gudanar dashi,,,
su dady mua'zzam dama su tuni sukaci gaba da firarsu anan Alhj Muhammad yake cewa dady mua'zzam "yanzu abinda ya rage mun na samo haj mua'zzam shine mai gadi na gidan namu sai kuma dai wacce zata dinga share mana gida haka da wanke wanke,,,""
girgiza kai dady mua'zzam yayi yace "eh hakanma nada kyau ay zan samo maka ta hnyar bada cigiya insha Allah yau zuwa gobe,,,,
dayake su momy umaimah sun danyi shiru a lokacin shiyasa hakan yabasu damar jin abinda mua'zzam sarakin ke tattauna shida alhj Muhammad a lokacin ciki kuwa harda ummu hani d'in wacce yatsunta ke cikin na juna tana matsawa dud dai saboda qin sakin jikinta har lokacin,,,,,,,








Kudan tasta fanss ba cj
*Xexen Fasaha*✍🏻
[10/11, 2:46 PM] Xainab Documen: 🌊🌊🌊


*MAHABEER*!!!
🌊🌊🌊


Story and writing
by
Xayyneb 💤💤


🌊🌊🌊🌊🌊


Fasaha online writers f. o. w.


🌊🌊🌊🌊🌊
🅿2⃣4⃣.
🌊🌊🌊
Maganar Anna ce ta katse ta daga tunanin ta data keyi jitayi tace"eh hakan ma nada kyau sabida mataimaki dad'i ne dashi,,,
sauke 6oyayyen ajiyar zuciya ummu hani tayi tirq'ashiii... wanna shine ake cewa ga qoshi ga kuma kwana yunwa,,, abinda itada iyayen ta suke burin samu kenan aikatau amman kuma gashi taji ana cigiyar masu yi tayi shiru,, anya kuwa in taci gaba da shirun nan nata bataso kan taba kuma batai butulci ga Allah ba daya basu komi a sauqaqe batareda shan wuya ba,,,? babban muhimmin abinma ciwon mamanta,, yanzu dud inya sake tasowa mata yaya zatayi knn da rayuwarta???
kada ki bari damar nan datazo miki ummu hani ta kucce miki ki bude baki kiwa bayin Allahn nn jawabi dan samawa mamanki mafita da babanki dakuma ke kanki d'in nan dasamawa mamanki lpia kokwa koma gida kan lokaci,,,,,. hannunta da momy umaima ta riqo ne yasata sauke ajiyar zuciya tareda d'agowa da fararen idanunta ta saukesu a kanta wannan karon cike da qwarin gwiwa,,,,
"mikike tunani haka 'yata??
momy umaima tayo mata wannan tambayar cikeda dan nuna kulawarta a kanta,,, a matsayin ta na wacce tazo wajenta taganta a cikin wannan hali haka,,,. dan Murmushi tayi tareda Dan satar kallon momy ni'ima datake zuge zip d'in jikkarta jin wayarta na ringing.....
sauke ajiyar zuciya ummu hani tasa keyi a karo na 2 sannan ta maida gaba dayan hankalinta ga momy umaima cikin dan rawa rawan muryarta tafara da cewa
"t.. to.. za...zan ma su baffa ...na maganar aikin d kuke mgn akai... daman dai muma munzo garin nan ne neman inda zamu samu aikin yi sai kuma wannan hatsarin ya ritsa damu harya kaimu da zuwa nan asibitin kuma gashi cikin yardan Allah munji kuna cigiyan wanda zasuyi muku aiki nasan baffa na inyaji hakan zaiyi musu aikin shida momma na a gidan,,,""
tana kaiwa nan tayi shiru kanta na qasa dan sauraran amsar tata,,
Kafin momy umaima tace wani annah tace
"ayya kaga ikon Allah,,, Allah sarki to shiknn Muhammadu kaji ko?,,"
tayiwa alhj Muhammad magana ya matso sosai dan girmamawa yace "na'am annah" tace
"ga shi ana ta maganar nemo masu aiki wa gidan naka da kace kanaso ynxu, to gashi wannan yarinya.....ta danyi shiru sannan ta dubi ummu hani tace "ammm yama sunanki 'yar nan??? ta tambayi ummu hani,,,
cikin girmamawa tace "ummu hani sunana"
Yawwa to kaji Muhammad ummu tace iyayenta suna neman irin aikin da kace kanaso za'ai maka kaga shiknn ma abu yazo a sauqi ko,,, "eh hakane annah masha Allah yanzu zamuje in mun tashi daga nan can wajen iyayen nata dan mu qara maganar sosai da sosai domin jin ta bakinsu suma kuma koko? ,,
"eh hakane kam gaskia,,," cewar dady mua'zzam saraki,,,
duban ummu hani momy umaima tayi cikin Murmushi dan har a zuciyarta taji dad'i na zata kasance kusa kusa da wannan yarinyar wacce gaba daya tagama shiga ranta, taji dad'in ita da bama ta samu gurbin aiki wajen ni'ima ba sai su iyayen nata da suka samun,, hakan yasa ta dubi mua'zzam saraki tace "yawwa nuree nikuma saina dauki ita ummu d'in tana tayani dan wani abun wanda ba'a rasa ba a cikin gida koya kagani,,,?
"bakomi wifey na indai hakan yayi miki to nima yayimun,,,"
cewar dady mua'zzam da yayi maganar cikin sakin fuskarsa wanda ga alama annah ma taji dad'in fad'in haka d'in

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login