Showing 21001 words to 24000 words out of 130351 words

Chapter 8 - MAHABEER Complete Document by Xayyneb.txt

Xayyneb   

29 Jan 2025

9945

ynda yk dnbaisan ta ynda zai tuqa monon ba ya kawo ba,
shi sam baida ra'ayin kan wata magana ta dinga had'asa da matan hausawa dinnan dan yatsani rainin hakali shi a rayiwar sa sam,
amman ganin tsayuwar bazatai masa ba yasa ya daure ya sauke kad'an daga cikin fad'in ran nasa dan tunowa da momyn tasa nacen na jiransa ya kai mata ruwan tasha,,
da wani irin sautin takun tafiyarsa na qaqqarfan namiji ya qara qwaqqwaran taku guda 5 sai gashi a bayanta still ya sake tsayawa hannayensa a wannan karon sanye cikin aljihun jeans d'insa kamar dai d'azun,
Wannan karon kuma bata juyaba yi tayi kamar batasan yana wajen ba dan ta shaida mutum ne ynxu ba Aljan ba sabida ganin datai masa in short time,
a yatsine ya fara maganar tasa da cewa
"ke! ,,ina buqatar ruwa a cikin ta nan wajajen tayaya zan iya samun su?,,,
ummu hani tajisa sarai amman jin yanda yake maganar tasa cikin nuna isa da son ai masa abin kan dole ynda yake so yasa tayi kamar bata jishiba,
ahankali taji ya sake maimaitawa nan ma tayi burus dashi saima qara saurin qarasa linke rigar baffanta datayi ta miqe tsaye ta dauki sauran kayan tana shirin wucewa abinta batareda ta qara dubn gefen da yake bama sam.
shikuwa ganin tana shirin tafiya gashi kuma baisan yaya zaiyi ba indai ta tafi tabarsa awajen kan dole yasa ya d'an sassauko da muryar tasa qasa yace "mamana keson ruwan ne,, kuma ma bata lpia shiyasa please ki taimaka baiwar Allah!,,,,
jin ya ambaci mamarsa ce keson ruwan bata lpia da kuma temakon da yace yasa taja ta tsaya cak a wajen,,,




Fasaha Online writers f.o.w. 📘🖊
[10/11, 2:45 PM] Xainab Documen: 🌊🌊🌊


*MAHABEER*!!!
🌊🌊🌊


Story and writing
by
Xayyneb 💤💤


🌊🌊🌊🌊🌊


Fasaha online writers f. o. w.


Please nayi d'n kure pls wurin sa dedicated a last pg saida na send snn na lura d fatan zaku min fahimta mai kyau dan d'an Adam ajizi ne.


Hmmm qawata ta kaina Raheenat Mahmoud, (heenat ) wannan shafin kena baiwa shi a zunzurutun kyautarwa gareki ,
🌊🌊🌊🌊🌊
🅿1⃣7⃣.
🌊🌊🌊
*A* hankali ta juyo baya batare da ta sake kallon sa ba harta iso gabansa ta bud'e bokitin kayan data linke ta fiddo wata faran roba ta swean water wacce ke da ruwan mono d'in a cikin ta, ta d'ibesu ne da nufin koda sunyi buq'atar shan ruwan basai ta dawo d'iba ba, dayake roban ruwan guda 3 ne saita miq'a masa d'ayan fuskarta na kallon gefe,
hannu yasa ya kar6a yana wani tatta6e lips yace ''sune ruwan zartsin knn a ciki?,,
duqawa tayi ta sungumi kayanta tayi tafiyarta ta barsa tsaye a wajen yana mai bin bayanta da kallo cikin raini da harara, wani d'an siririn tsoki yaja tareda d'aga kafad'a yace
"may be kurma ce ma inaga, koma dai miye ita inda dai na samarwa momy na abinda takeso to ba damuwa na bace wnn.""
shima baro wajen yayi ya koma room d'in da momyn tasa ke a ciki ya taradda ita zaune kamar yanda ya barta, ruwan ya miq'a mata yace "take it momy ga ruwan,
Kar6a tayi ta fara sha jin dad'in ruwan da ta dingayi ne cikin bakinta yasa saida tasha kusan fin rabin ruwan goran sannan ta dure robar q'asa ta ajiye tareda kallon mahabeer cikin murmushi tace "yanda kake farantamun da komi nakeso mahabeer na kaima Allah shi dad'ada maka yaima za6in mata ta gari kaji ko mahabeer na?
''ameeen momy ya fad'i maganar yana mai q'ara fad'in har yanzu dady bai dawo ba mom,,,,, maganar tasa ta katse a dai dai lokacin da yaga shigowar annah itada dadyn nasa,,
tsananin farin ciki ne kwance kawai a fuskar annah lokcn tundaga nesa harta qaraso wajen da mommy umaimah take ta zaune, zama tayi samn kujeran wajen tana fad'in "kai labari mai dad'i naji umaimah daga bakin sa kai Alhamdulilla masha Allah,
Allah kuma ya inganta kai kai masha Allah,,,
murmushi kawai mommy umaimah takeyi kanta sunkuye dan kunyar annah ma taji ita,, shikuwa mahabeer sai amsawa yakeyi da fad'in cewa
"ameeen tsohuwa,,
juyowa annah tayi tace "ah kaga yaro da kana bayana ma ashe?
Sunno fuskarsa yayi yana karkashe mata idanuwa ya d'ora fuskar a kafad'an ta yace "ashe mace na mancewa da mijinta annah daman?
ture fuskar tasa tayi tareda fad'in "yaro tun wuri jeka nemo matarka,,, wata 'yar siririyar dariya ya saki qasan lips d'insa sannan yace aini tuni na fidda second wifey ta annah,,.
cikin farin ciki annah ke kallonsa da iyayen nasa dan aduniya ynxu basuda burin suga mahabeer ya fiddo musu matar da har zai ganta da kansa yace yana son ta zai aura,,
har had'a baki mua'zzam saraki yakeyi shida annah wajen cewa
"a ina take yarinyar to,,
ware arms d'insa yayi yace
"a bayyane take fa, kuma kunsanta tuni,
6oyayyen tsoki mommy umaimah tayi ita d'aya ta gane wacce yake nufi cikin takaicin abin,,,
"bleesing towmy ce fa kunsanta ai inda tana zuwa gaisheku sosai,,, habawa tuni annah tahau tattafa hannayenta tana yin fad'a,, da fad'in lai'lahaillalla Muhammad rasulillah s.a.w.,,, yanzun dan Allah yaron nan har yanzu kana tare da wannan kafirar yarinyan?
fisabilillahe ina abin so yake ga wannan mai gashin dokin?,,
Maimakon kaje ka nemo arewa hausa Fulani masu kunya saika buge da nemn kitistan,?
"haba first wifey,, kigane man,, sufa hausan nan sam basu iya soyayyar bane fa, kuma ga raini nikuma,, i hate disdain wlh annah natsani a rainani sukuma na kula hakan ne halayensu yawanci,,
Oh kenan mu da muke hausawa dud mun raina kowa da kowa knn shiyasa muka haifeka har gashi kaima kazo ka renamun kana fad'a mana magana inda kasha nonon marainan ko?
Zama yayi a kusa da kujerar ta ya kamo hannunta yana fad'in "haba my first wifey ki gane man nifa ba haka nake nufi ba daku,, kuma cewa nayi mafi yawancin su ai ba cewa nayi duka bafa,
yana maganar ne yana mai nuna alamun a tausaya wa maganar tasa a fahimceta sosai sosai,
amshe hannunta annah tayi tace "kaini rabu dani kuma bazamu ta6a yarda ka auro mana arna maqiya Allah ba ka hada mana a cikin zuriya ba dasu, ko mahaifinka dake d'aurema q'ugu da d'amara bai isa ya q'etare magana taba har ya amince ka aurota bare kai,,"' "haba first wifey nasan wasa kk ay,
Hararsa tayi tace "koba wasa ba? Zakaga wasa ko ganin idonka shashashan yaro kawai ka girma bakasan ka girma ba,
Shiru mahabeer yayi dan yaga yau annar tasa ya ta6ota da yawa dan haka bai sake cewa komi ba ya tashi a gabanta Ya koma gefen momyn tasa yana danna wayarsa fuskarsa a cur6une.
har a cikin zuciyar mommy umaimah taji dad'in wankesa da annah tayi kan wannan bleesing d'in datake manne masa kamar mayya.
In baccin ma abin mahabeer ga mata nan jamfa a gari kyawawa amman har kace baka son hausa sai yare?
girgiza kai tayi tareda fad'in
"Allah shirya"
annah kuwa sawa tayi yazo ya maidata gida dan kawowa umaimah abinda zataci,
haka mahabeer ya miqe yana cika yana batsewa kallonsa annah tayi tace "oho dai saika gama,, magana ce kuma na fad'a kajini da kyaun gaske, kuma zanga mai canzamin ita a gidan,."
baiyi magana ba ya fito waje fuuuu ransa a bace iyayen suka bisa da dariyar gwabzawar tasu da annarsa,,
annah ta biyo bayansa tana fad'in "kafi jirgi tashi,,,"
jiyayi yayi karo da mutum harya kai ga shi wanda ya bugen ya kaiga yin baya ya fad'i a wajen,,,
"Washhhhh Allah na q'uguna zafi baffa zafi!!! ",,
Abinda ummu hani tace knn a fili cikin lokacin da take murza qugun nata saboda tureran da yayi by mistakly,,,,
ta fito ne dan siyo musu abinci anan waje taga mai abincin batakai ga kawowa ba mafarin knn ta dawo da nufin anjima ta koma ta siyo musun inta fito.
sarai ya gane yarinyar data temaka masa da ruwa ce a d'azun, amman dayake a cikin fushi yake shiyasa yaji ita kanta ta qara bashi haushin,,
yayi wani dogon tsoki ya wuce a wajen,,,
anna da taga komi ya faru a wajen tayi saurin q'arasawa gaban Ummu hani ta zuqu'nna tanai mata "sannu yar nan kinji,
dubn mahabeer annah tayi daya kusan shigewa a wajen tace "kai mahabeer zo dawo nan nace,,,
cikin sake d'aurewar fuskarsa ya dawo wajen kamar ya fashe yakeji,
"bakaga abinda kaiwa yarinyar mutane bane zaka wuce?
dubnta yayi yace "anna to minayi kuma?
ita face ta shigo mun hanya ay bn sani ba,,,
d'aga masa hannu annah tayi tareda fad'in cewa "dalla ni yimun shiru,,kama mun ita ta miq'e tsaye, mutum sai zafin zuciya,,
Ummu hani jin ance ya kamata ta miq'e yasa ta tattaro sauran qarfinta tayi wani iriyar miqewa a bazace har gyaton mayafinta data rufe rabin fuskar ta dashi ya fad'i gefensa qasa.
da yake data koma can wajen su baffa ta cire nikabin datasa d'azun wajen wanki shine dazata fito ynxu ta lullubo fuskar tata kawai dantaga ba jimawa zatayi a wajen ba,
daga annah harshi uban cijiyar babu wnda fuskarsa batayi arba da tsabar tsantsar kyawun gaske daga yarinyar ba kamar ba mutum ba,, musamma fararen idanunta farare tas dasu dasuka q'ara q'awata fara tas d'in fuskar tata.
"masha Allah tabaraka ahsanal khaliqin," abinda annah tace knn,
"sannu kinji 'yar nan?,,
ummu hani cikin sanyi sanyin muryarta wacce na kusa da itane kawai zasuji maganar tata cikin yaren hausar tata kadan kad'an ta dubi annah tace "bakomi mah,,
har a zuciyar annah taji yarinyar ta burgeta sam batada saurin fushi ynzu da watace ynda aka bugeta dinn ta fad'i taji jiki masifa zatai tayi ammn ita bata nuna hkn ba,
"To 'yar nan mukeda godia kinji,
ummu hani batace komi ba tayima annah sai anjima ta juya baya inda mahabeer yake tsaye wanda tun ganin fuskar yarinyar da yayi a d'azun yaji kamar wani abi na son matsawa tunaninsa a lokacin sai kuma wani abu mai qarfi yaji yaqiba abin dakeson matsawa zuciyar tasa daman hkn a lokacin, babban abinda yabasa mamaki shine jin yarinyar na magana wato shi ta mayar d'an iska knn a d'azun ta koma masa bebiya dayana mata magana?
take yaji matan hausawan sun qara siriye masa a fannin,
shi dama wannan rainin hankalin yayi hate kuma gashi tun ba akai ko inaba yarinyar ta fara nuna masa shi daga had'uwa a rana daya?
to inaga an zauna dindin din kuma?
Karaf idanunsu suka shige cikin na juna gani yayi tanai masa wani kallo wanda ya rasa gane ma'anarsa amman yafi kama da kallon mugu take masa shi ga fahimtarsa.
Bai q'ara tsinkewa ba saida yaga ta bisa da wata iriyar 6oyayyar harara ta duq'a ta d'auki mayafinta ta q'ara kallonsa tace *"amakson"!!!.* (maqiyi)
tana fad'in haka ta rufe jikinta da gadon mayafin har zuwa rabin fuskarta kamar farko harta shige room d'insu yana binta da kallo cikin rasa gane mi kalmar *amakson* d'in take nufi datace masa????,
duban annah yayi yace "annah kinji mi waccen yarinyar take ce mun kuwa?
"Eh naji taimun daidai kuma,
kuma abinda ta fad'a dai dai ne dan inba amakson d'inka ba babu wnda zai nemi illataka yaq'etare ya barka batareda ya waiwayeka ba,,,
Shuru yayi shi sai lokacin ma ya tuna annah bafulatanace kuma tasan yare da dama,,, ganin ta wucewarta yasa yabita da sauri yana fad'in "tsaya annah dan Allah,!!
Annah tace bazan tsayaba nida kake fushi dani kuma, sam shi yama mnce da wani fushi da yake da ita a halin yanzu burinsa ta fad'a masa mi waccen marar kunyar yarinyar tace masa da yarensu ne dan yasan dai yanda take masa wannan kallon ba wai wani abun arziq'i bane ta furta masa daga cikin wannan tatsitsin bakin nata ba,,,,,,






Fasaha online writers f.o.w.📘🖊




*Xexen Fasaha*✍🏻
[10/11, 2:46 PM] Xainab Documen: 🌊🌊🌊


*MAHABEER*!!!
🌊🌊🌊


Story and writing
by
Xayyneb 💤💤


🌊🌊🌊🌊🌊


Fasaha online writers f. o. w.


🌊🌊🌊🌊🌊
🅿1⃣8⃣
🌊🌊🌊
Annah ko sauraran shima bata qarayi ba ta bude motar ta shiga shima ya shiga ya zauna batareda ya qara tambayar ta amsar kalmar ba shima suka dauki hanyar gida,,,,
Ummu hani kuwa wata irin azababbiyar faduwar gaba ne ke cigaba da addabarta tun ganin da ta fara yimasa a karo na farko da kuma yanzu, waje ta samu ta tsaya ta runtse idanunta tareda maida numfashi, tabbas wannan fuskar tasa itace take gani a cikin addababben mafarkin nan nata dud inta kwanta, to mi hakan ke nufi kuma?
jitayi muryan baffanta a kusa da ita da sauri ta bude idanunta kuwa ta waresu a kansa tace "baffa na'am yakace?
mike damunki ne haka ummu hani?
Inaita miki mgn shiru tun d'azun bakiji ba,
"yi haquri baffa naje siyen abincin ne naga mai kawowan bata iso ba shine na dawo na tsaya anan d'in dannasan tana kusa da zuwa ynxun bn son in koma gunku ne babu abincin shiyasa ma qarin tsayuwa na anan d'in"
cikin son 'yar tasa yace"bakomi Allah shi miki albarka zo muje ki zauna kiji maganar da likita yayi mun a gameda binciken da yayiwa mamanki jia gameda ciwon nata, ya fad'i maganar jikinsa a matuqar sanyaye hakama fuskarsa.
zama tayi kusa da mamarta ta riqo hannunta taga har lokacin maman na barci anan baffa yace" ummu kikita yai mun bayani cewan ciwon mamanki na zuciya ne wnda yana buqatar ai masa aiki dan sanuwar lafiyan nata, har ya qara da cewa in har kuma aka barta a cikin wannan halin muddin ciwon ya qara tasowa da zafi kamar wancen karon tofa zuciyarta zata iya kumbura harya kaita ga fashewa kinji abinda likitan yace,,,,
tuni idanuwan ummu hani sukayi narai narai suka kawo qwalla baffa ya dora da cewa "babban damuwa na ummu shine ynda likitan yace kudin aikin naira dubu d'ari 600 da 50,,, ki gaya mana ummu hani a ina zamu samu wannan maqudan kudi ko jakar kudinmu da kikace mun ta fad'i kudin dake cikinta bazasu kai dubu dari 150 ba bare,,,
Gashi hadda number kawunki dud a ciki bare mu kirasa yasan halinda ake ciki
hawayen datake riqo ne suka zuraro mata a saman fuskarta ta qara damtse hannun maman nata tace"baffa yanzu shiknn zan rasa momma na ynzu?
girgza kai yayi yace zata rayu insha Allah da rayuwar Ubangiji Allah,, yanzu dai kinga wannan kudin dubu dari 200 wanda bawan Allahn nan dayazo ya raba mana gasu nan zamu adana su in yaso saimu san yanda zamu bullowa lamarin,,, share hawayen fuskar nata tayi tace "baffa kada mu koma gida saboda duka dabbobin naka ba wasu yawa ne dasu ba kabari mu zauna a nan garin ni zan shiga cikin gari neman aiki in har nasamu na samu gidan aikin koda shara da wnke wnke ne zanyi zan tara kudin da zaiwa mommo na aiki ta warke baffa,,,!!"
"a'a ummu hani,,,
ni ya kamata inje in nemi wannan aikin bake ba, cewar baffan nata.
yanzu mu bari kamar yanda likitan yace idan ta ida warwarewa zai sallamemu nan da kwana 2 kinga saimu shiga cikin garin dan samun aikin,,,
shiru tayi bata sake cewa komi ba tana roqon Allah yasa su dace d'in dan lpiar mahaifiyarta itace babban burunta a duniyar nan,,,
ji sukayi binte ta fara tari da sauri ta matsa ta zauna gefenta tace
"momma sannu kin tashi, ya jikin qarfin?
yunqurawa binten tayi ta tashi daga kwancen da take ta zauna tace"yawwa ummu jiki yayi sauqi kam,,, baffa yace to masha Allah,,, Allah qara sauqi,, amin inji su.
sallan la'asar sukayi sannan ummu hani tace "baffa zanje nasan yanzu mai abincin ta zo saina siyo mana ko?
dato saita dawo suka amsa mata harta wuce daga wajen,, ta inda sukayi karo da wannan mutumin mai d'aurarriyar zuciya da fuska a cewarta tanan ta biyo taga wajen ba kowa kamar basu ta6a tsayuwa wajen ba,, can ta yi nisa da tafiyarta ta kusan sauka daga benen qasan taji magana daga bayanta ance
"wait madam ummu hani man,,,
juyowa tayi ganin waye ne kusa da ita yasa ta sake daure fuskarta tana shirin jawo mayafin nata dan rufe fuskar nata kamar ynda ta saban yayi saurin cewa "why d reason da zaisa kirufe min wannan kyakkyawar face d'in naki wacce nake mafarkin mallaka akoda yaushe?,,,,
doctor lurwan ya fadi hakan yana mai matsowa gareta,,, da sauri ta matsa gefensa can tace "plss karkace zaka tsaidani doctor ina sauri ne,,
tayi maganar tana mai yin tafiyarta,,, da sauri yasha gabanta yace
"ki saurareni plss ummu hani zamu tattaunane gameda kudin da zaku bada aiwa mamanki aiki,,,,,,,
jin abinda yace ne yasa ta dago fararen tasss d'in idanunta ta dubesa dasu,,, tuni Doctor lurwan yaji wani irin faduwan gaba ya sargafesa wani irin kyau ne tattare da yarinyar mai qwarjini da tafiyar da kowane irin d'a namiji komin taurin kansa kuwa,,,
,m..hhhh wani murmushi ya saki tareda lashe gefen bakinsa yana wani irin wasu abubuwa irin na 'yan duniya wanda suka saba latsa 'yan matan da suka sakar musu jiki barkatai,,,,
saida ya waiga yaga ba Mutane tanan 6angaren da suke tsayen sai can daga nesa dasu sannan yace
"amm in har kin yarda zaki auren xan ma mamanki aikin nan a kyauta,,
da sauri ta dubesa dudda ba tantance maza tayiba kuma ba shiga har karsu take ba amman wannan daga ganinsa cikakken d'an duniya ne shi saboda kodaga yanayin iriyar kallon dayake jifanta dashi musamman akan red lips dinta da mamanninta dudda jikinta a rufe yake amman bai hanashi yi mata kallon qurillan,,,
Muryan sa taji yana fad'in "koya kikace ne madam ummu?
a zuciyarsa kuwa rayawa yake waiii naganni makwanci daya da wannan zuqeqiyar babyn carkwai mazaqwai knn,, dan daga ganinta zata bada show ata kowane 6angare jiyake har tsigar jikinsa ma tashi take a lokcn.
"aa kabarsa mun gode da kulawa zamuje mu nemo kudin mu kawo,,
tana fad'in haka tayi gaba stiil yasake shan gabanta yace
"haba ki tsaya mana ummu kin gane koda baki shirya auren bane yanxun why not muyi auren titi na wucin gadi,,, em? yana maganar ne hankalinsa a tashe kamar ya kamota jikinsa yakeji,, dan ya lura sam yarinyar bata san iriyar harkan da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login