Showing 33001 words to 36000 words out of 130351 words

Chapter 12 - MAHABEER Complete Document by Xayyneb.txt

Xayyneb   

29 Jan 2025

9965

abinda ya tsana knn kuma raini,, shiyasa kulum annah take fada akan sai yaita faman Kama rai yana dauresa ita batasan natural haka yake ba abin a jininsa ya taso,,, sake daure fuska yayi katamau sannan yasamu damar cewa "annah waimi ke kawo yarinyar nan cikin ahalinmu ne dan Allah?
plsss Anna ku sallameta tabar nan gidan mu kadai mun isa mu bawa ahalinmu farinciki bawai sai wasu sun shigo jikin muba,, "
saida ya qarasa maganar sa taz ya tsaya Yana maida numfashi tareda muzurai kowa binsa yake da ido a wajen ummu kuwa dauke fuskar ta tayi daga gefensa aranta kuwa cewa takeyi "oh ni ummu *daga taimako*?? Sai mutum ya zamemun qaya a karo na 2 da sake haduwa tun asibitin?
kuma shine abin yake ta *bibiya akai*???,,,,
wani dan siririn tsoki taja a can qasan ranta sannan tace "wlh dai dai irin kace ni mlm,,, amman kuma fa a tsakaninmu knn, bazan taba gwada wa su mah hakan ba kuma,,, kaida ka siya taqamar nima zan dinga siyar maka da tawa kalan a 6oye a 6oye bayan idanun mutane,,,
d'an fitinar mutum kawai dakai,,,
tayi maganar tareda murguda bakinta,,,
jitayi annah na cewa masa
"em hemm em hem,,to tsohon kakanmu,,kagama bamu umarnin koko da saura ka qarasa muna sauraran ka sosai sosai????
Marairaice fuskarsa yayi yace haba dan AllAh annah ki gane man yarinyar nan sam batta da..... Miye haka mahabeer na? Cewar momy umaimah ranta adan 6ace,, shiru yayi ya kasa furta komi shi knsa yayi mamakin yanda momy umaima ta nuna rashin jin dadinta akan wannan maganar dayayi akan yarinyar,,, wato harma ta fara shiga tsakanin su da su knn?? rabon dayaga sauyin fuskar momyn tasa shi baima iya tunowa amman gashi lokaci data wannan yarinyar ta janyo masa wacce bai dauketa a bakin komi ba sai irin sune masu fitowa daga garuruwansu suna yawon bara a titi titi rareda kwana a titi hankalin su kwance,,,
gyada kai yayi a hankali yaxee
"yi haquri momy,,,
Momy umaimah tace "ba komi mahabeer na wannan itace wacce zata dan dinga taimakamun a wasu ayyukan na gida mafarin zuwan nata knn,,, momy kina nufin 'yar aiki knn?
"a'a mataimakiya dai,, dan ummu ta wuce yar aiki a wajena,,,
wani abu yayi tunani a ransa na cewar lallai kin kawo kanki yarinya zaki gane bakida kunya,,dan da kanki zakibar gidan nan mu zuba ni dake hmmm,,,,
nan da nan ya dan saki fuskarsa yace ohk momy,,
hakanma yayi ay,,, ni zan wuce side dina momy na warwatsa Yana maganar yana yamutsa fuskarsa kamar dole ne aka sashi yinta,,""
hararsa annah tayi tace qafan gaba ta gaida ta baya dai,,,"" ficewarsa yayi yaqi bata amsa,,
girgiza kai momy umaimah tayi sannan tace
"kai ohh mahabeer na Allah shirya myn kai ka cika fitina wlh,,,"
anna tace"hmm kunsan haka knn ma ashe kuke ta sa masa idanu yana tsulan tsiyarsa a cikin gidan nan,,
Murmushi kawai momy umaimah tayi ta kauda zancen da tace
"yanzu annah nasan dai kinason kunun tsamiya da qosai in kin kai azumi bari naje sai na hada miki ko??"
ganin annah na shirin sake musawa yasa momy umaimah tayi saurin tashi ta kamo hannun ummu suka bar dakin suka koma kichen suka fara harhada kayan dazasu aikin dasu suna gama had'a kunun tsamiyar suka rufe cikin samis sannan momy umaimah ta juyo markadadden qullun qosanta daga cikin blander din data gama markadawa sai qamshin tarugu da albasa yake markadan,, nan ta fara soyashi ummu tana tsamewa dud abin nan momy umaimah daurewa zuciyar ta kawai takeyi dan yanda qamshin qosan ke bugunta jitakeyi kamar zata zazzage 'yan hanjin cikinta ne saboda ynda zuciyar nata ke tashi,,,
''ummu cigaba da soyawa zanje falo in dan kwanta dan kaina ciwo yake mun ga kuma juwa unaji,," cewar momy umaimah tana mai miqawa ummu din tsinken juya qosan da matsaminsa,, kar6a tayi tace
"to mah Allah sawaqa"
"Ameeen ummu,,,"
da sauri ta fice ta koma falo ta kwanta sai a lokacin ne tasamu relief na abinda ta keji amman dudda haka ta sanya hankicef a fuskar ta dan tanajin qamshin qosan na mata gizo a hanci,,
"hyy momy na ykk?,,, Allah sa yaya mahabeer yadawo dai daga office ,
dan yau ko zan kwana momy sai naga yaya,,dan na kwana biyu naje wajen dady shiyasa"
hannat knn takeyin maganar bayan ta ajiye ledar kayan da momyn tata ta aikota ta gwada wa momy umaimah din kalar samfir din kayan business din nasu data ce zata ayko ta ta kawo matasu ta gani,,,




*Xexen Fasaha*
[10/11, 2:46 PM] Xainab Documen: 🌊🌊🌊


*MAHABEER*!!!
🌊🌊🌊


Story and writing
by
Xayyneb 💤💤


🌊🌊🌊🌊🌊


Fasaha online writers f. o. w.


🌊🌊🌊🌊🌊
🅿2⃣6⃣.
🌊🌊🌊
momy umaimah duba kayan ta farayi tana mai bata amsar eh ynxu ya dawo hannat nasan yanzu zai fito nn falo dan ga abincin sa nan bai fito ya ciba"
"tohm momy ina nan kuwa tayi maganar Tana mai qara sake zama ta zuge jikkarta ta fiddo fowder dinta ta qara shafawa tareda wetlips harda gazar,,hannat irin wanda suka amince dinnan nan ne da fante fante a fuska kowane kokaci kwalliyar fuska bata yanke mata kodan taga kwalliyar ne ita ke dan fiddo tan ne oho,,, Murmushin 6oye momy umaimah tayi ta girgiza kai dan tasan dud wannan abin da hannat keyi ne dan mahabeer ne,batasan miyasa har yanzu hannat bata fahimci shi ra'ayinsa yafison natural abu ba na koma miye batareda sirki ba, har a ranta taji tausayin hannat dan tasan ko kadan mahabeer bata gabansa...
wata riga ce da wando na fakistan da gyalensu kalar red and white cottons ne kayan daga cikin wanda take d'agawa taga sunyi masifar burgeta kayan harta raya a ranta zasuyi wa ummu na kyau kayannan dan haka kawai saita fiddasu gefe daya ta ajiye taci gaba da duba sauran suma saida ta qara fidda mata kala 4 sannan.
"kaya sunyi kyau hannat cewar momy umaimah data miqa mata sauran kayan dake cikin ledar tana mai qara cewa "kicewa hajiyar taki ina gaisheta kuma a cigaba da saidasu kan farashi mai rahusa kinji ko??
ita hannat sam hankalinta ma bayya ga momy ynda ya kamata gaba d'aya hankalin ta yana kan qofar dakin mahabeer daga can saman benen,,, lura da hakan da momy tayi yasata tashi ta nufi kichen jin ana kiran sallar magrib....
iskewa tayi ummu ta gama suyan Tana goge saman wajen da dan guntun towel dake hannunta a sanyaye take yin komi babu abinda take da buqatar gani irin taga mommonta da baffanta dan tunda suke bata taba jimawa kamar haka ba batareda tana manne dasu baffanta ba,,,
Jin momy umaimah na magana da cewa "sannu ummu har kin gama ashe ma, juyowa tayi tana dan Murmushi take fad'in "eh mah an gama yanzu kayan zan wanke wanda muka yi aikin dasu,, to sannunki 'yata Allah shi miki albarka"
Ameen take amsawa dashi tana dan qara Murmushi har gefen dimple d'inta dake saman fuskarta na wajen saman tsoka tsokar ceck dinta ya lotsa a wajajen guda biyu dukkansu,,
Momy umaimah tace"amman to kibari kiyi buda baki saiki yi ko?
batason yawan musu musamman ma ita wannan din datake mata qwarjini sosai hakan yasa ta cewa
"to mah shiknn,,, "
"yawwa ummu ta,, to ki zuba kema abinda kike da buqatar ci din sai kije can dakin nan dana kaiki kikayo wanka ki zauna kici abinki inda nasan bazaki yarda ku zauna dining table ba kici kunyar ki dayawa fa ummu,,, momy tayi maganar cikin yar dariya,,,
qara sunne kanta tayi cikin gyalenta tana Murmushi Murmushi mai ban sha'awa
"uhmm ummu knn,
bari na zuba miki naga alamun diban ma nauyi yake miki dubi ynda kikesawa kanki abinci kamar za'a bawa yaron goye hmm,,,
saida ta dibn mata qosai dinnan wanda yaji kayan hadinsa sosai sannan ta zuba mata kunun tsamiyan da chips din da suka had'a shima ta dora mata bisa babban faranti ta miqa mata tace
"yawwa amshi to mmu,,jeki kikai ki dawo,,, fita tayi da plate din a hannu dai dai lokacin da mahabeer ya ke saukowa daga saman sa shima cikin sabon shigar sa ta red jeans da white shirt mai dogon hannu tun kan ya qaraso wajen qamshin turarensa tajiyo ya bugi hancin ta haduwar udanunsa cikin nata yasa tayi saurin dauke idanunta a kansa cikin rawar jikin da batasan lokacin da ya shigeta ba,, sauke idanunta tayi bisa farantin dake hannun nata bataqa dago idanunta ba a haka taci gaba da tafiya ba zato taji yasa gefen qafadarsa ya goge nata da dan qarfi irin ta ingizar nan ta da gan wanda daman da gan gan yayi mata hakan tun daya hangota ya, shiry yin hakan a zuciyarsa,,,
tana shirin wucewa ne bayan tasamu daqyar tasake riqe farantin hannun nata daya kusan kuccewa zuwa qasa shikuma cikin dabara dajin haushin kayan vasu zube ba kamar yanda yaso yasa shi sako mata qafarsa ta tsakan kanin nata qafafun ya tardeta ya ida saurin wucewarsa daga wajen kamar bashi yayi ba ko kallo bata ishe saba dudda irin faduwan da yaji tayi qasa sosai kuma ga alama komi na cikin farantin sun warwatse qasan wajen hakan yasashi sakin wani 6oyayyen Murmushi na jin dad'i a ransa,,
cikin sauri hannat data hango wutowarsa ta miqe ta nufosa tana wani karairaya taja ta tsaya gabsnsa tana shirin kamo hannunsa ta riqe yayi saurin janye hannunsa tareda sake daure fuskarsa yace "masallaci"
daga haka ya kewayeta yabar falon ya fice abinsa,, da kallo ta bisa na ganin ynda yake takunsa na taqama,,
"Wayyo Allah na,, ta furta tareda rungume q'irjinta da hannayen ta, jitakeyi kamar taje da gudu t rungume faffadan bayan sa datake bi da kallo wala Allah kota samu sassaucin abinda takeji daga garesa,,,
dole ta koma ta zauna tana jiran dawowar tasa...
aca kuwa ta gudar hanyar da ummu take zaune turus bayan kayen datasha daga mahabeer,,wani irin takaici ne da baqin ciki suka mamayeta na ganin ynda yai mata,, bin jikinta takeyi da kallo gaba daya ya bata mata jiki da kunun nan harya fillitsa ma a fuskarta har zuwa gefen idanunta da bakinta,,
"Allah ya isarmum mugun mutum"
dafa qugunta tayi dataji yasake riqe mata daman gashi shine silar haifar mata da ciwon qugun tun karon da suka farayi a asibiti gashi yanzu ya sake motso mata shi ta hanyar mai mai da yai mata,,
samu tayi ta miqe tsaye ta hanyar dafa bango da tayi tana ciccije lips dinta daqyar ta samu ta ida miqewar a tsaye,,, still tana dafe da qugun nata da hannayen,,,
ta danyi kamar minti 5 a wajen tana murza wajen sannan taji qugun nata ya saki ya danyi dai dai sai kokacin ne ma ta juya can cikin tsakiyar falon wnda ke zagaye da kujeru harta hango wata budurwa zaune a daya daga cikin kujerun ta bata baya tana dannar wayar dake hannunta,,,
sake cije lebe tayi yaynda ta zuqunna tana faman tattara qosan da chips din tana mayarwa a cikin plate din ta samu ta kaisu daki sannan ta dawo ta koma kitcen din ta iske momy umaima Tana jiran dawowarta wacce ganin ummu din ta jima bata dawo ba gashi lokaci na son qurewa yasa harta fara tunanin ta daure itan ta dauki kayan ta kaiwa annah din dud da bata son jin qamshin qosan nan na rabar ta ko kad'an mafarin knn ma tace ummun ta dawo ta tayata daukan kayan un yaso ita saita dauki samis din kunun,,
ganin shigowar ummu din yasa ta cewa
"yawwa 'yata kin dawo ma knn, to tayani daukan kayan mu kaiwa annah.... sakin baki tayi tana bin jikin ummu din da kallo ganin yanda yayi dagaje dagaje da kunu musamman ma gaban rigar ta,,
"ahh ummu miye ya faru kin zubar da kayanne a hanya??
tuni idanun ummu hani kuwa suka fara shirin sauko da ruwa dan ita dama haka take muddin aka 6ata mata rai kuma akazo ana tanbayarta musabbabin abin tofa kuka take Saki dan saurin kuka ne da ita ita,,
jitayi wani abu mai qululu qululu tattareda daci ya tsaya mata a mata a maqoshinta sannan ta daure da qyar tace "eh mah na fad'i ne qasa bn lura ba,,, tana maganar hawayee na sauko mata shar shar a fuskar ta,,,
"momy umaima tace "kaii sannu daina kuka ummu dan Allah kinji, ko kinji ciwo ne wani wajen na miki zafi yasaki kukan???
girgiza kai ummu tareda tace "a'a mah banji ciwo ba,,
"to Alhamdulilla yanzu jeki ki wanke jikinki zan kawo miki wani kunun a daki,,, juyawa ummu tayi tabar kichen din tana son tace zata gyara wajen da kunun ya zube amman tasan zatace tabarsa ne inta gama za'a gyara.,,
toilet ta shiga ta cire rigar ta daurayeta ta shanya sannan tayo wanka tareda alwala ta fito ta zura kayan ta na d'azun wanda ta cire su. wato baqaqen kayansu na buzaye knn na saqi,,,
ta kabbara sala dan itace tafi tsaya mata arai datayi ta a halin yanzun,, sam sam ita ga al'umman komi bata bari salla ta wuceta kan lokaci...
a falo kuwa momy umaimah ta gama kaiwa annah kayan sannan ta dawo falo ta koma dakinta dan tayo salla itama,,hannat na nan zaune kunnen ta ear pies nema a halin yanzun a ciki,, kida kawai takesha abinta dan ita momy umaimah tayi zaton ma tayi sallar ganin after dress dinta dake jikinta,, har saida akayi ishae sannan mahabeer ya shigo falon shida dady mu'azzam da sauri hannat ta cire ear pies din kunnen nata ta gaisheda dady ya zauna Yana amsawa sannan ya dubi mahabeer dake tsaye gefensa kamar soja yaqi ma zama takaicinsa shine ynda yadawo ya iske hannat har yanzu,, mtsss yaja tsoki a ransa kuwa fadi yake cikin tsabar takauci "mima za'ayi da mace marar class,,??
yasake jan tsoki.
"mtsss"
wannan tsokin kuwa da yayi wannan karon har saida ya fito fili dady mua'zzam yaji shida hannat da momy umaima data fito itama dai dai kokacin,,,
dubnsa dady mua'zzam yayi yace "ah soja na yadai kana tsoki haka babu komi???
shafa sumar kansa yayi yace
"nop dady babu komi bari naje dakin nawa na kawo maka takardar naka dake wajena na cikakken bayanin injinan man da muka shigo dasu a ya ko?,,,"
"ok soja na jeka ina jiran ka to ,,,"
wucewa yayi momy umaimah kuwa tana cewa "nuree ga dinner din ku can kan dining,,
"bari dai ya dawo wifey kinsan Nafison inga inacin abinci tareda my son kanmu zai qara haduwa ne,,,
wani kallon gefen ido umaimah tayi masa ta juya taga hannat tawani zuba musu ido ba ko kunya tana kallonsu,, cikin dabara ta sauya maganar da cewa "oh mu kan namu sai ya rabu dakai ko inda ba za'a ci damu ba,,,? Murmushi dady mua'zzam d'in yayi yace "bance haka ba uwar gida aike tuni kan mu a had'en sa yake ko?,
Yayi maganar yana kashe mata ido,,
da sauri ta juya zata bar wajen ganin yanda nureen nata ke shirin bata kunya a gaban 'yar su,,,
tafara taku kad'an knn da nufin zuwa wajen annah sukaji qarar faduwan abu da q'arfi,,,,,
"washhhh dady na kuzo dan Allah qafana..... ohhhhhuchhhh!! "
Abinda sukaji mahabeer ya furta knn da, qarfi,,, dukknsu suka nufi can inda ya zame din ya fadi a qoqarinsa na hawa sama zuwa dakin sa,,
da sauri dady mua'zzam ya roqosa shida momy umaimah suna fad'in "kai mahabeer lpia kuwa?? Miya faru,,,??
cikin ciccije lips dinsa yake cewa da qyar yana dafe qafar tasa da hannunsa
"dady... daddy.... wohhhh washh!!,,, dady naji na taka wani abu ne anan wnda ya zameni na fad'i ina tunanin ma na karya qafa na... auchhh dady yasake sakin wata qarar dan tsabar zafi.... "momy na zafi,,"" ya fadi hakan yana mai nishi najin azabar zafin da qafar tasa keyi masa,,, jin qafar hannat na zamewa itama wajen a irin tsugunnin da tayi taji tana shirin zameta ya sata shafa hannun ta a q'asan tiles din wajen ta sunsuna nan da nan tace "laahhh wlh momy kunu ne a qasan wajen shine ya kadasa ma inaga,,,"
har had'a baki sukeyi wajen cewa"kunu dai???
tomi zai kawo kunu nan kuma a hanya?????",,,,,,,,




*Xexen Fasaha*
[10/11, 2:46 PM] Xainab Documen: 🌊🌊🌊


*MAHABEER*!!!
🌊🌊🌊


Story and writing
by
Xayyneb 💤💤


🌊🌊🌊🌊🌊


Fasaha online writers f. o. w.


🌊🌊🌊🌊🌊
🅿2⃣7⃣.
🌊🌊🌊
"ya salamullahi"
Abinda momy umaimah tace knn tana mai dafe kanta da hannunta daya, sannan ta dago ta dubi dady mua'zzam d'in dake cewa "miya faru kuma yana maganar ne yana qara janyo mahabeer din cikin jikinsa yana qara mammatsa masa qafan tasa da hannayen sa yana cigaba da tofa masa addu'oen da sikazo cikin bakinsa a lokacin,,,
sauke ajiyar zuciya momy umaimah tayi tace"matsala aka samu ba shakka kunun ummu ne daya zube anan lokacin da zataje dakin ta dashi nasan ta manta batai moping din wajen ba shiyasa har tsautsayi yakawo mahabeer wajen hakan ta faru,,,,,. "waimi ke faruwa ne anan da kukazo kukayi dafifi haka??,,
cewar annan data qaraso wajen itama,,, kame baki tayi ganin mahabeer kwance shame shame a qasan wajen hannayensa saman qafarsa Yana wash wash,,, "kaikuma dakake wani wash wash kamar wata mai naquda miye ya faru ne em??? Annah ta tambayesa tana mai duqowa wajen itama,,,
sam kasa bata amsa yayi shi ta kansa ma yake a lokacin,,, momy umaimah ce ta fad'a mata yanda abin ya faru,,,,
anna tace "to sai kuma miye em? Ynxu dn Allah mikina kai kamar ba namiji ba? daga wannan 'yar faduwan sai kuma ka bi ka susuce???
idanunsa ya dago dasuka canza launi dan wahala da qyar ya bude baki yace"washhh wlh annah dan bakiji yadda nikeji bane cikin qafar nan nawa zunga kawai takemun kuma wlh saita san ta zubda kunu a wajen nan na taka,,,!!"
ya qarashe maganar tareda qoqarin miqewa tsaye qafar ta sake girdesa dan takawar dayai mata ba dai dai ba nan da nan kuwa ya sake zaman 'yan bori a wajen da qarfi,,, wata sabuwar auchhhh din ya sake saki dan zafin zaman ba qaramin shigar sa yayi ba,,,
sannu dady mua'zzam da hannat suketa binsa dashi zuwa wannan karan lips din mahabeer kuwa ba qaramin sake yin ja sukayi ba saboda tsabar taunar su da haqoransa da yakeyi batare da sanin saba, jin zafin zugin qafar nasa yakeyi har can cikin qwalwar kansa na

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login