Showing 102001 words to 105000 words out of 130351 words

Chapter 35 - MAHABEER Complete Document by Xayyneb.txt

Xayyneb   

29 Jan 2025

9940

din da ummu hani suke ciki ta shiga filin airport din,, dayake abin na kudi ne nan danan aka shirya mata biza ta shiga sahun fasengeer ko minti biyar bataiba jirgi ya daga bnda kuka babu abinda ta shige cikin qaton hijab dinta tanayi, tana nuno kamar jia ne sukazo garin cikin jirgi ita dashi,, amman gashi yau qaddara ta fiddota,, tun tana kuka mai hawaye har saida taji kukanma kansa ba dadi dole ta haqura takoma yinna zuci, sune basu sauka nigeria ba sai Misalin tara na dare, taxi tasamu ta kwantata masa anguwar nan kuwa nan da nan sai gasu cikin anguwar 'yan majalissu ta bashi kud'insa ta shiga falon gidan tana jaye da trolley tana kukanta marar hawaye sai gunji,
annah ce da momy umaimah ke zaune a falo suna yin hira aiko kamar daga sama suka ga ummu hani ta shigo ta kife kanta anan bakun qofar tana kuka, har bangaje juna annah da momy umaimah suke har suka isa wajenta suna hada baki wajen cewa"ummu??! ke ummu hani lpia miya sameki?? daga dawowarku sai kuka? Inashi mahsbeer din yake kuma neto??!!
gani kawai sukayi ta sulale qasan wajen idanunta a kakkafe ko baqin ba'a gani sai farin,,, bakinta kuwa banda fitar da wani farin kumfa babu abinda yakeyi, zuwa can suka ga ma ta daina yin motsi kwata kwata, jikinta ya saki gaba day'a babu inda ke motsawa tartare da ita sak matatta.....!








*Xexen Fasaha*
f. o. w.
[10/11, 2:49 PM] Xainab Documen: 🌊🌊🌊


*MAHABEER*!!!
🌊🌊🌊
Story and writing
by
Xayyneb πŸ’€πŸ’€


🌊🌊🌊🌊🌊


Fasaha online writers f. o. w.


*🌳impacting valuable knowledge and Entertainment is our concern🌳*.
🌊🌊🌊🌊🌊
πŸ…Ώ4⃣9⃣
🌊🌊🌊
A matuqar razane su annah suka tarairayota jikinsu suna kiran"ummu hani? ke ummu minene ya sameki?,, gaba day'a sun gigice ganin bata sanma sunayi ba kunfan nan dake bakinta yana zubo mata sai qara zubowa yakeyi kuwa, a guje momy umaimah ta rarumo wayarta ta kira dady mua'zzam saraki bai d'aga ba saboda driving yake lakacin, wayarma bai duba ba bare yasan mai kiran nasa,
cikin rawar jiki momy umaimah ta share hawaye dake zubo mata na tsananin tausayin ganin halinda ummu hani ke ciki,, babu b'ata lokaci ta q'ara kiran dady mua'zzam d'in cikin rawar murya take cewa "ka d'aga,, ka d'aga,, dan Allah,, shi kuwa dady mua'zzam jin wani kiran sabo ya sake shigo masa yasashi yin parking gefen hanya,, ganin sunan matar tasa ne shi ya sashi d'ag'awa ah nutse tunkan yace wani abu yajiyo muryarta cikin wani iriyar *tashin hankali* tana cewa 'kayi sauri ka dawo gida nuree gida kam babu lpia ummu hani ta mutu zamu rasa ummu hani nuree mun rasa ta,, sai kawai yajita sake fasa kukan mai cin rai,, fahimta yayi kamar bata a hankalin tama amman dudda haka cikin tsananin mamaki yace "wace ummu hani kuma? suda suna London kuma?? ganin takasa basa wata gamsasshiyar amsa ne ya sashi cewa "okey gani nan tafe daman gida zanyo yanzun,, yana gama fad'in haka ya katse wayar ya tada motr shima hankalin sa a matuqar tashe ya nufi gida mai gadi ya bude masa ya shiga tareda kashe motar cikin sauri kamar zai kifa a qasa ya fad'a falon kusan fasuwa qasa yayi a samansu annah dake zube bakin qofar shigowa sakamakon wani
mugun tuntuben daya gwabza dasu momy umaimah da annah dake zagaye da ummu hani,, momy umaimah na ganinsa ta miqe da sauri ta riqosa tana hawaye tama kasa magana sai nuni datake yi masa da 'yar yatsarta a inda ummu hani take kwancen,
kamo hannunsa tasakeyi ta janyosa suka zuqunna gaban ummu hani,, cikin wani tsananin mamaki yake kallon ummu tunani yake yaushe suka dawo nigeri Alhalin ko yau sunyi waya da mahabeer amman bai fad'a masa ba?,, duban annah yayi yace "annah miya faru ne da ummu hani haka inashi mahabeer din ne to kuma??
dakatar dashi annah tayi tace "a'a d'and'a yandak ka gantan nan muma hakan muka ganta dan haka kuma yanzun ba lokacin tambaya bane d'aukar taneh kawai zamuyi mu kaita asibiti dan haka jeka shiga mota gamu nan fitowa",,
da sauri kuwa yafita yaje gyara parking yana jiran fitowarsu, saida itah annah ta dauko malullubin ta ta miqowa momy umaimah hijab dinta dan sam kasa tashi tayi taje dakin harta dakko ma tana nan duqe gaban ummu tana kuka,, kama ummu sukayi suka fito da ita suka shiga motar sannan suka nufi asibitin,
addu'oe kawai annah ke tofa mata tana lazumi yayinda sam momy ita kam takasa wani iyayin katab'us dan dudta sare take jin kanta ma ita, suna shiga asibiti aka d'auki ummu hani bisa gadon marassa lpia aka kaita wani daki doctor lurwan ne da doctor usman suka duqufa kanta dan su samo su lalubo mta koda numfashinta dayai sama ko qasa ne a tattare da ita,,
tsawon awonni suna haka amman abin yaci tura dole doctor lurwan ya fito ya baro doctor usman ciki,
banda share zufa babu a abunda doctor lurwan ya keyi dan limit din ciwon ummu ya wuce tunanin sa kam,
da sauri si momy umaimah da annah suka qaraso gunsa suna tambayar ko ummu hanin ta farko ne?!,, da qyar ya iya bude bakinsa sannan ya dubi dady mua'zzam yace "alhj kuzo mije office nawa akwai magana,,
binsa sukayi dukknsu bayan sun zauna doctor lurwan yayi shiru kansa a qasa cikin karayar zuciya da klr wani tsinkewar ta dan har a ransa yake kwadayin ummu yanzun inta mutu shiknn burinsa bazai cika ba na ganin ta yarda da muradinsa, sam bai san shi bai san tamayi auren ba knn? yanzu ko ummu hani ta wuce tunanin ka doctor lurwan,
jin muryar momy umaimah tana ce masa "ta mutu ko doctor? dan Allah in ummu hani ta mutu ka fad'a mana mu musulmai ne masu daukar qaddara"!! ta qarashe maganar cikin gursasshen kuka tana kwanciya jikin annah wacce itama tuni zuciyar ta ta kare tana share hawayen fuskarta da mayafinta,,
dady mua'zzam saraki ne yayi qarfin halin cewa "inaji a jikina ummu hani bazata mutu ba dai kuyi haquri,
dan Allah ku daina kukan dubn doctor lurwan yasakeyi sannan yace "muna sauraronka doctor, sauke ajiyar zuciya doctor lurwan yayi sannan yace ''ba mutuwa tayi ba saoda dudda bata numfashi mun aunata mun hango zuciyarta na bugawa sosai fiyeda yanda ake buqatar zuciyar d'an adam ma ta dinga iriyar bugawan, ammn wannan na nuni ne da cewa ita din taga wani abu da yayi matuqar razanar da ita yayi kuma mummunan touching heart nata wanda shine ya jaza mata hakan, amman kuma cikin ikon Allah munyi iya nami qoqarin wajen saisaita mata beatheart din nata ya dawo normal yanzun like others peoples, shiru ya danyi sannan ya hada yatsun hannunsa waje daya yana yamutsasu sannan yace "amman kuma babbab matsalan yanzun shine yanda numfashinta yaqi dawowa shine nace bari na fito naji daga bakinku dan gaskia dole sai an sanya mata abin jawo numfashi na oxygen wato na ainahin iskar da ake shaqa ta ciki wanda shine zai taimaka mata wajen saituwar numfashinta"
shiru doctor yayi yana sauraren su dady din,
dady muazzam yace "babu komi asanya mata din mudai fatanmu Allah shi bata lpia,, haka kuwa akayi doctor lurwan yakoma dakin sukasa mata oxygen din nan a fuska tareda dora mata ledar ruwa suka fito,
dady suka shiga dakin tareda zama gefen gadon suna kallon ummu hani cikeda tsananin tausayi dan sam an kasa mai iya yin wni magana ma cikinsu sai kallon ummu hani sukeyi kwance sambal sai kace ba ummi hani nan tasu ba? Lallaikam mai rai yaji tsoron Allah dan mutum ba' a bakin komi yake ba wajen a Allah,
sai zuwa can annah ta fad'a masa dud abunda ya faru tun daga shigowar itah ummu hani din har kawo yanzun,, momy umaimah tace cikin dasasshiyar muryan ta "ni ina tunanin akwai abinda ya faru tsakaninta da mahabeer fa nuree? inda gashi ita day'a tazo batareda shi ba,, taguminsa dady mua'zzam yajanye tareda sakin wata iriyar qaqqarfan ajiyar zuciya sannan yace "tabbas umaima nima nayi tunanin hakan a raina dan lpia kam babu ynda za'ayi ya turo musu d'iya tun daga qololuwan duniya ace shi yana cen zaman sa abinsa kuma???!! kaiii a'a gskia da akwai sakal ga A'la'marun yaran nan,, numfashi annah taja cikin mutuwar jiki tace "gskia ne wannan,
duban ummu hani tasakeyi sannan tace "kuma ita gata kwance bare tafada mana abinda ke faruwa amman mizai hana ka kira wo shi mahabeer din kaji abunda ya farun harya turo yar mutane gida da dare haka a gigice babu nutsuwa a garetan? dan yana dan banzan shashashan yaro"!
dady mua'zzam yace "Wlh annah tun d'azun nike kiran numbersa sau dai inji ta kan it's not reachable qarshema yanzun bata shiga number kwata kwata annah,,
shiru sukayi dukknsu sukayi suna tunanin anya kuwa lpia to shima din yake kuwa?, dayake asibitin akwai tsaro amman dudda haka annah tace zata kwana wajenta su dady mua'zzam suka wuce gida dan momy umaimah taso itama ta kwana din sai kuma dady mu'azzam yace kodan kalacinsu na safe yakamata suje gida dasafe saita hado breakfast ta kawo musu, amman sam baby manal taqi bin mamarta jikin annah ta lafe danta saba da annah sosai sam bata damu dasaita sha mamanta ba indai tana wajen annah,,
yarinyar tanada wayau sosai,
Koda suka koma gida lokacin day'a saura saida dady mua'zzam ya kirayo abokinsa mr johson yaji ko suna tareda mahabeer din amman sai yaji wayar tasa shima switchoff dole ya haqura ya barwa gobe haka suka kwanta zuciyoyinsu sai saqe saqe suke.
mahabeer kuwa suna komawa gida mikel ya wuce side dinsu shi kuma tundaga waje yake qwalawa ummu hani kiran nasa da cewar "feader na? feader na gani na dawo I'm back kina inane? Ina kika shige,,? Jin shuru yasashi kwanciya nan falon ya fiddo wayarsa yana dannawa danga tunanunsa ko wani abu takeyi a ciki jin shirun yayi yawa yasashi ajiye wayar ya miqe tsaye tareda haura saman dakin yana cewa feader nahhhhhh?? kin boye da yawa fa,, lokacin bada magungunan nan nawa yayi please kizo ,,,jin babu motsin komi a dakin yasashi leqa katifarta nanma bai gnta ba har toliet ya shiga ya dudda ba nan ma yaga wayamm tsaye yayi tareda dafe qugu da hannayensa yace "ah to ina ta shige ne kuma haka? saurin sauqa qasa yayi dan zuciyarsa ta basa wataqil tana kichen ne ma,, turus yayi ganin bata nan nanfa ya fito ya dinga qwalla mata kira shiru kakeji,, zubewa yayi bisa kujera yana tunanin to ina taje haka?,, wayarsa ya fiddo cikin aljihu ya kira number ta taita ringing baiji an d'aga ba,, tsoki yaja ya ce feader kin fiye saka waya silent why aita kira baki sani ba,, zuciyar sa yaji tace kaje side dinsi sera may be ta shiga ne can,, hakan kuwa ya miqe kai tsaye ya nufi bangaren su sera yana shiga kuwa yayi karo da sera zata fito ya danja gefe ya dubeta yace "sera sister na tana cik kuwa??
zuba masa idanun ta sera tayi sannan tace wace "sisteer naka kuma datun d'azun naga naga tabar gidan nan jaye da akwati tana kuka??
wata mummunan faduwa gabnsa ya yanke yayi cikin tsananin mamaki yace "kuka kuma miya faru da ita,, ware hannayenta sera tayi tace i don't know nazata ko kaine ma kai mata wani abun,, a guje mahabeer yabar wajen ya koma cikin gida yana qara kwalla mata kira yaji shiru zubewa yayi qasa ya dafe kansa idanunsa tuni sun fara ja cikin tsananin damuwa yake cewa "ina yarinyar nn ne ta shiga,, kaddai cikin garinan taje wani wuri, kuma tana kukafa akace??!!,, zumbur ya miqe tsaye tareda daukar key din mota dan gani yayi zama kam sam bai gansa ba. cikin birnin London yaita zagawa lungu da saqo ko zaiga umnu hani amman ina har saida akayi magrib da isha'e yana yawon neman ta cikin mota saqo da lungu kuwa.
daqyar yasamu yayi salla sanna ya dasa neman ta amman shiru kakeji,,, wata zuciyar tace toka koma gida my be takoma gida yanzun kaje ka duba,,, ransa a b'ace yace
"kin wahalar dani ummu hani miyasa zakije wani gu bada sani naba?? "!!!!!
qarfe 11 dai dai ya shiga falon gidan ya hau sama nanma shiru bata nan, nnnfa hankalin sa ya qara yin wani mummunan tashi a lokacin ne ya tabbatarwa kansa ummu hani wani abu yasameta a inda taje to ina taje?? wata zuciyar tace masa 6acewa tayi knn,, dafe kansa yayi nan da nn jijiyoyin kansa suka taso rudu rudu idanunsa sunyi jajir yana tunanin inda zai je nmta a qasar nn, zumbur yatashi ya fuce ya higi motarsa ya fuce kai tsaye gidajen television d redio ya nufa yaita bada sanarwa haka yaita yawo a titi kamar marar hankali zautacce,
sai ukun dare sannan ya dawo gida gaba day'a nutsuwa ta kucce masa sam takasa masa,, alwala yaje yayo yaita sallolin nafulfuli tareda kai kukansa ga Allah saida yayi asuba sannan yarigaya da yayanke shawarar bugawa gida ya fad'awa su dady batun kosasa a add'ua nan ya lalubo wayar tasa ya kunnata ko gani bayyayi sosai ma sakamakon wani zafi da idanunsa ke masa wnda damn indai ransa ya b'aci hakan shine alamun kukansa,, yana fara ringing day'a biyu yaji dasyn ya d'aga yana fad'in "Alhamdulilla sojana,, miyake faruwa wai naga ummu hani a gida tazo kuma inata kiran wayarka yaqi shiga?? a razane mahabeer ya miqe tsaye yace "whatttt dady tazo gida fa kace? Eh tazo yanzunnan ma haka asibiti zamuje dan acan ta kwana ba lpia dan haka komi kkyi ka ajiyesa kazo gida yau yau,,, ai baima bari dadyn nasa ya gama maganar ba ya latse wayar nan yahau shiri ko wanka baiba yayi parking kayansu ya hada komi da komi ya bude briefcase dunsa can qasa ya fiddo viza dinsu wanda ya karbo jia ya tsaida drop ko sallama baiwasu mr Joseph ba sai filin jirgi nan aka gama masa komi da komi ya shiga jirgi dud a rude ba'a jimaba jirgi ya d'aga dasu,, qarfe 11:22 suka sauka a airport drop yadauka zuwa anguwarsu basu jimaba suka iso nan ya sallami dan drop din yayi cikin gida kamar zai tashi sama dan sauri yana fad'in ''dady momy ina ummu hani din miya faru da ita dan Allah?!
jin anyi masa mgn daga baya yasa shi saurun juyowa wannan kurtun soja mai gadin gidan nasu shine yashigo falon yake fad'a masa suna asibi yan gidan,, bai tsaya tambayar wane hospital bane dan yasan itane suke zuwa nursing home da gudu ya fito ya figi mota ya fice daga gidan kamar mai tafiya saman iska,, da temakon doctor lurwan ya fado dakinda aka kwantar da ummu din sam shi baiga momy umaima dake zaune nesa kadan da gadon ummu dinba tana karanta littafin hisnul Muslim garkuwar musulmai, yayinda annah take can gefe d'aya tana zaune tana lazumi bayan gama sallar walhar ta datai,, ganin oxygen a hancin umnu hani tuni ya qaraso wajen a gigice ya durqushe gaban gadon yana kyarmar jiki ya dora kansa a gadon yana faman danne xuciyarsa da hannayensa kamar zata fito yekeji dan *tashin hankali*,, dubnta yake kwance kamar gawa wani tsabar tausayin ta ya mamaye masa zuciya ya kifa knsa a cinyoyinta yanata sabbatu yana fad'in "kitashi feader na please ina tsoron ace kada akan lalurar ciwo na ne yasa kika gudo kika barni????!!!! pleassssssss ummu wake up wake... Uppppppppp dan girman Allah ki tashi haka ki ganni nima na ganki zanje in nemo ma kaina magani na samu sauqi sosai,, insha Allah nai alqawarin zame miki gwarzo namiji ba marar lafiya wacce hatta kaisa garasa qarfin gaba dazai hucewa matarsa takaici ba kamar sauran maza ba, kitashi dan alah wlh xn nem mgni in warke ummu miyi rayuwarmu cikin jin dadi harki haifamun yarahh nima...... sambato kawai yake wasu zafafan hawaye yaji sun biyo kuncinsa abinda bai tab'a yiba wato kuka tunda Allan daya kawosa duniya kuwa,, amman wai yau shine yake zubarwa hausa fulani woman hawayen shi??? akan mace qwara daya? !! ta6666 shi kam dai ma bai damuba dan yayi hawayen shide din tsoronsa kada ace umnu hani tagajida lalurarsa ta gudo gida ne ta fadawa su dady dansu rabasu tunano hkn daya qarayi ne ya sashi qara zaucewa da sambatu yana sake fad'in """wlh zanje insamo maganin ummu zuqunnewa yayi a wajen tareda sake danne zuciyarsa datake sake qara masa wani iriyar addababben zafin numfashi kawai yake saki,
momy umaimah da anna kuwa tuni jikinsu yayi sanyi da tsananin tausayin yaran,, wato daman wannan matsalar dayake fad'a ynxun yasa ummu hani din dawowa gida sbd baida lafiyan gaba? abinda kowanensu yake saqawa a ransa knn,
a hankali momy umaimah ta qaraso ta dafa kansa tareda zuqunnawa a gabansa,,, da sauri ya gado kainsa da jajayen idanunsa kamar an watsa masa tasshi a cikinsu, ganin wacce ke gabnsa tana fidda hawaye itama hakan yasashi saurin rarrafawa ya fada jikinta yana cigaba da surutansa da cewa momy.. mo.. momy ummu kitadimin da ita kinga ance in ansanyawa mutum oxygen basu tashi a rayuwa,,, wlh momy zan mutu nima inta mutu momy na plasss kitasar mun ummu hawaye kawai yake bulbulo masa a fuska lokacin,,, rungume kansa momy umaima tayi cikin tausayin kansu tuni suka dinga fiddo hawaye a tare annah ce ta taso daga wajenda tagama sallar ta nufosu itama knn saiga...






*Xexen Fasaha*
f.o.w.
[10/11, 2:49 PM] Xainab Documen: 🌊🌊🌊


*MAHABEER*!!!
🌊🌊🌊
Story and writing
by
Xayyneb πŸ’€πŸ’€


🌊🌊🌊🌊🌊


Fasaha online writers f. o. w.


*🌳impacting valuable knowledge and Entertainment is our concern🌳*.
🌊🌊🌊🌊🌊
πŸ…Ώ5⃣0⃣
🌊🌊🌊
Annah ce ta taso daga wajen data gama sallar tata ta nufosu kenn saiga dady mua'zzam sunzo shida dady Muhammad da momy ni'ima sun shigo tareda sllma, suka zauna bayan sunwa su annah yamai jiki,
jigum sukayi suna kallon ummu dake a kwance ido rufe sai shi mahabeer kuma da keta faman sakin ajiyar zuciya yana jikin momy still,,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login