Showing 15001 words to 18000 words out of 130351 words

Chapter 6 - MAHABEER Complete Document by Xayyneb.txt

Xayyneb   

29 Jan 2025

9942

qarfe 8:00 pm ne muazzam saraki ne zaune a babban falon gidan sa na q'asa yana kallon labaran duniya a tashar
N. T A. wnda lazeem ne kullum kan ya kwanta barci sai ya tsaya ya kalla sannan,,,
labaran da ake haskowane na wannan dinbin mutanen dake kwance a gadon asibiti hakan ba q'aramin tausayi ya basa ba,,
Zai san abinyi wasu insha Allah kuwa nan da cikin satinnan dan mutanen na buqatar a temaka masu matuqa,,,
Shi in zaiyi temako sam bayya jiran zuwan government gaba gadi yakeyin komi nasa, kirkinsa ne har ya jawo hankulan jama'a gaba daya knsa da nufin yai musu shugabnci dan sunsan zasuyi dace da shugaba adali ne shiyasa.
da yawa yawan mutane sukaso wannan za6en ya fito takaran presdent amman yace a'a shi baida burin siyasa tun usuli,,
dukiyarsa yasan har ya mutu bazata ta6a q'arewa ba har jikokinsa kuwa. dudda kuwa maq'udan kud'aden dayake fiddawa kusan kullum sbd mabuq'ata bayin Allah,,
mommy umaimah ce ta iso wajen hannunta d'auke da fresh milk ta miq'a masa tareda fad'in "gashi nuree ina zuwa,,, da sauri ta nufi toilet ta kusan minti 10 a bakin sink tana q'aqaran amai,,, saida q'yal 2 ta samu wani d'an hikkin nan ya fito amman kuma sai taji hakan yai mata dad'i data samu tayi aman.
wanda damn haka take yinsa kusan kullum a 6oye dud dare a irin wannan lokacin kuma,,, bakinta ta wanke sannan ta dawo ta zauna a falon, sam bata nuna masa wani alamun ciwo ne a tattare da itaba lpia lau suka fara firansu jifa jifa suna kallon tv,,, annah ce ta fito daga d'akinta tana d'an dogara sandarta harta iso wajensu ta samu waje a q'asa tayi zamanta,,mommy umaimah ta dawo kusa da ita ta zauna tace "annah mikeson ci in kawo miki kema yanzun?
Annah ta girgiza kai tareda 6allar farin goranta tace "inahh a'a umaimah abinda nake sha'awar ci sam gidan nan baku dashi ay,
Dady muazzam saraki yayi dariya yace "miyeshi annah ta? ki fad'esa yanxun ko ina ne zanje da kaina na samo miki shi uwata,
Momy umaimah cikin dariya tace "eh hakane nuree nice ma 'yar rakiya kam,,,
annah zatayi magana knn saiga mahabeer ya shigo falon yana cika yan batsewa uwa zai fashe,,
kai tsaye kuwa saman cinyr annah ya d'ora kansa ya kwanta rigingine,,,
da kallo suka bisa dukansu.
kamin wani yai magana acikinsu phone d'insa ta d'auki ruri ganin yanda ya zaro phone dinsa a fusace ne tareda kiran sunn mukhtar yana faman masefe shi mukhatar d'in a cikin wayar akan wata maganarsu wacce suka kasa gane samanta bare qasanta,,,, tsoki yaja kawai tareda rufe wayar gaba dayanta ya mayar a jeans dinsa,,,
tunani yakeyi a zuciyarsa gidan wa mukhtar yakai wannan iyayen kud'in samada naira miliyan 10 a wata d'aya daga sabbin ma'aikatarsa wacce ya bud'e ya d'ora shi mukhtar d'in akan komi danshi abin zai masa yawa ga nasa gana dadynsa,, shi bama fidda kud'in ne ya basa haushi ba, a'a yasan kud'in babu inda zasu sai wajen 'yan iskan 'yan matansa yai musu facaka dasu,,
runtse idanunsa yayi dn shi sam ya rasa wannan irin halin bunsuranci irin na abokin nasa a rayuwa?
shi indan tashine bazama ka bata kokacinka ba wajen kallon wata abar yarinya hausa fulani ba, wnda babu kome a tattare dasu sai tarin fitina dasaka headache wa mutum.
gani yayi dady mu'azzam d'in ya miq'o masa hannu nan shima yayi q'oqarin danne takaicin muktar ya miqawa dadyn hannunsa suka had'a kamar ynda suka saba sannan dadyn yace
"yadai my son naganka in feeling sad?
Waya ta6omin mazajena ne em????
"wlh kuwa dad mukhatar ne ya 6atamun rai,,,
But,, but,, bakomi yanxu munyi settling ma,
Mommy umaimah tace "to mikuma ya had'oku yanxun?
sai kace dai ba d'azun nan kuka fita ku 3 lami lafia ba kuma harda basher?
Shuru yayi baice komiba, annah tace "angona ka ajiye komi a gabnka yanzu kaje ka samo min yad'iya da q'uli q'uli dan shi kad'ai nake da muradin ci yanzun"
har had'a baki momy umaimah takeyi itada dady muazzam wajen cewa "annah yad'iya fa?
da daren nan kuma?
"eh shi nakeda buqata ko babu ne?
kansuyi mgn mahabeer ya miq'e zaune yana fidda coat dinsa ya rage laktip din jikinsa sannan yace "miye yad'iya kuma annah?
"tambayi iyayen ka inkai baka santaba su ai sun sani,
bari naje na samo miki shi annah cewar mu'azzam d'in yanamai riq'o hannun mahabeer yace muje my son,,
dubnsa mahabeer yayi yace "amman dady ina zamu sami wannan abun ynxun?
"kadai taso muje inmunje wajen zaka gani,
dole yamiqe annah na masa konkomin shima wataran matarsa zata iya yimasa hkn komin dare wato tashi nakama kn abunda takeso, taqara da fadin cewa "kuma wlh angona dole kaje komin dare"
Shuru yayi baice komiba yabi dadyn kawai ammsn a zucuyarsa yana fad'in "nooo annah kin fad'a dai ne kawai inajin ko blessing bazan mata wannan bautar ba bare wata cen daban kuma,,,,
[10/11, 2:45 PM] Xainab Documen: 🌊🌊🌊


*MAHABEER*!!!
🌊🌊🌊
Story and writing
by
XayynebπŸ’€πŸ’€


🌊🌊🌊🌊🌊
Fasaha online writers f.o.w.


🌊🌊🌊🌊🌊
πŸ…Ώ1⃣3⃣
🌊🌊🌊
*A* mman a zucuyarsa yana fad'in "nooo annah,,
kin fad'a dai ne kawai, inajin ko bleesing bazan mata wannan bautar ba bare wata cen daban kuma,,,
shine yayi driving dinsu dady muazzam na masa kwatancen inda zasu samowa annah yad'iyan, a haka har suka isa wajen kuwa.
shi abinma ya basa mamaki sosai ynda yaga jama'a wajen a sosai kamar da rana anata siyen ganye kala kala Hadda tuwo na kowane irin tsiron hatsi kakeso tofa akwaisa wajen,,
a haka suka siyo suka dawo gida.
dakinsa ya shige ya rage kayan jikinsa ya wuce toilet ya watsa ruwa sannan ya fito ya shirya yayi kwanciyarsa tareda jawo wayarsa, wacce tun shigowar sa dakin yaji qarar shigowar messege a phone d'in sai ynxu ya bude ya karanta,,
tsoki yaja tareda yamutse d'aurarriyar fuskarsa na ganin saqon daga hannat ne,,,
yarasa gane mike damun 'yan matan yanzu wai ma dai?
qiri qiri ba kunya zasu fad'a maka suna sonka kamar dai yanda itan ta rubuto masa yanzun fa.
yanajin babu yarinyar da sauran mutuncinta zaiyi saura a ransa muddun yaga ta furtawa wani hakan da bakinta bare mashi kankat kenn.
kwanciyar sa yayi haknali kwance ba damuwar komi a ransa kota kan wayar ma bai qara biba,,,.
Washe gari asabar dady mu'azzam saraki ya sauko daga samansa a shirye cikin shigarsa ta girma. haka itama momy umaima take a shirye wanda daka gnta kaga cewan eh yess matar manya ce itan ba kwano kwano tundaga suturar jikinta da sauran ma kayan jikinta, fuskar nan tata a sake tk ga fara'a, mata mai tsabar mutunta jama'a komin talaucinka kuwa zata tsaya ta saurareka bawai dole sai irinsu ba,, wato masu hali? nooo,, ita kowa nata ne,,,
tana gefen mijinta
a tare suna saukowa suna fira suna dariya abinsu gwanin sha'awa.
a haka har suka shiga dakin annah.
suka gaisheta.
anan ne kuma shi dady mu'azzam sarakin ke fadawa annah inda yakeson zuwa dan temakawa mutanen da matsalar ta samesu ata bngaren rasa muhallai dakuma lpia, kamar dai yanda suka saban,,,
annah tace ''ayya Allah sarki,, Allah dai shi yi maka albarka ya qara bude na alheri,,
kaje kana tare da sa'a cikin rayuwa insha Allah"
"ameeen ameen annah 2, sai mun dawo to,
"annah ko zamuje ne tare dake kema dai yau?,
a cewar mommy umaima tana murmushi.
girgiza kai annah tayi tace "a'a kuje kudai,
dai Allan mai doku lpia ni zan sanya lalle ne a zunguru na,
dan ga hannayena shauran lallen ya kusa ficewa shiyasa,
tun fa wanda kika daura mun ne wancen zuwan,,,
Umaimah tayi saurin dawowa ta zauna tace "kawo na sanya miki to annah in yaso ni saina zauna nuree sai suje tareda da mahabeer ko?,
annah tace a'a baza'ayi haka ba, inda dai kun saba zuwa ku ukun dud ranar weekend to yanzun ma kuwa hakan zakuje,
kutafi ba komi ni zan sanya da kaina Allah shiyi albarka dai, umaimah kema Allah kawo miki rabon ki a duniya, dan har abadan bazan bar yi miki addu'a ba kema na ganin rabonki a duniya nan a,,,,,,,
Shiru annah tayi ganin shigowar mahabeer cikin dakin a shigarsa da yafiyi ta qananun kaya,, wannan karon farar rigace yasa da farin wando jeans,
a saman rigar ya dora wata iriyar baqar riga mai dogon hannu iya zuw wajen belt dinsa baqi, sai ya nannad'e hannayen rigar duka, wanda hakan yabawa kwantaccen baqin gashin hannayen sa fitowa shar a farar fatar jikinsa gwanin sha'awa, ga black watch dinsa nan qirar diamon sai daukan ido yakeyi wnda bayyana kud'in sa 6ata lokaci ne a wajen fad'a ma, hakama cover shoes dinsa da farar sock nasa.
tako ina mahabeer baida makusa, a tsaye yake q'arfaffan namijin gaske,,,
amman kunnen sa yaso ya dauko masa mgnr da annah tayi ta qarshe,, wnda tacewa mommy tasa ta samu rabonta? to shi dai a iya saninsa basu nemi wani abu suka rasa ba a rayuwa, tako ina Allah ya fad'ada musu gashi har suna bayarwa suma amman har ace momy na nemn wani abun kuma ta rasa a live ? to miye shi abun?
d'aga kafafarsa yayi tareda dan d'age gira d'an kasa gano amsar da zuciyar sa keda buqatar sani amman bata sani ba, share zancen yayi kawai yana mai q'ara gyara blueetooth d'in kunnen sa a tym d'in daya ida shigowa tsakiyan dakin duka.
sai yaga suma sun da sha jininsun kuma sunyi shuru da mgnr da sukeyi kafin ya shigo suna kallonsa da murmushi kamar basune suke mgnn samun rabo ba ynxun.
bayan ya isa wajen su dady mu'azzam d'in ya miq'a masa hannu shima dadyn ya miq'a masa suka jinjina a tare sannan ya d'an kwanto a smn jikin dady d'in yace "morning dady,, hope you wake well dady ?,,,
dan bubbuga bayan sa dadyn yayi yace
"I'm fine my lovely son,ina fatan kaima ka tashi lpia?
Yeah iam 5n like yhu my dady"
rabuwa yayi da jikin dadyn yaje kan cinyar momy umaimah ya daura kansa yana fadin "morning sweet momy?,,
dafa kansa tayi tana qoqarin boye fuskarta daga garesa dan perfume d'in daya sanya tanajin kamar yanason sata amayar da abinda taci dudda dadin qamshinsa kuwa.
cikin dabara ta amsa gaisuwar tasa tareda tashi tsaye tace zataje dauko jakarta data mnto ta a saman bed nata.
da sauri ta fice shikuma ya maida kansa a cinyar annah yana fad'in
"yadai matar kin farka lpia kema dai ko?,
Harararsa annah tayi tace " to da ban tashi ba daka ganni?
kaini wannan auren ma inajin fasashi zanyi ace mutum kullum fuskar mijinka gim a d'aure sai kayi sa'a sannan zai sakar maka ita?
Inaaaa bada niba to,,
qara langwa6e kansa yayi yace
"ohhhh kaga wannan tshohuwar?
to ai fara'ar zuwa takeyi ko annah ta?
ya fad'a hakan tareda watsa hannayensa yana ta6e pink lips dinsa alamun hakan ko a jikinsa.
tace "kai tafi can ni bani waje,, sai kaita zama ay har sai sakin fuskar yazo ya isheka sannan ka saketan inda ba tare kk da kayan kaba daman,,
wani irin murmushi yasaki yana mai qara gyara kwanciyar kansa a cinyar annah batareda yace komi ba.
dariya kawai dady mu'azzam ke musu yana fad'in
"ah mudai annah/'yan bada haquri ne dn wannan auren kam naku mutu ka raba keda mahabeer dinki annah, hmm wanda dmn sabo da shine muka samu ake jimawa mamu anan ba'a koma gida katsina ba,,. mahabeer yace "yesss dady na,,, da sannu ma saina maido muku da ita nan duka,,,
a lokacin mommy umaimah ta dawo d'akin tana cewa "dakuwa munji dadi mahabeer na muddin kuwa kai mana wannan qoqarin.
dariya sukayi dukansu yayinda mahabeer yayi wani 6oyayyen murmushi kawai abinsa shi,,,.
a haka suka fito nan haraban gidan suka shiga mota dady mua'zzam na gefe yayinda mahabeer ke tuqa motar mommy umaimah na baya tana amsa wayar hajiyar hannat akan kayan datace taje london ta siyo ko za'a kawo matasu ynxun tagani ,,,
anan momy umaimah take fad'a mata zasuje anguwa ne ynxun bata nan,
acan bangaren hajiyar hannat d'in ke cewa to shiknn inta dawo zata aiko mata hannat ta gwada mata kalar sampur d'in kayan ahaka sukayi bankwana.
saida motarsu ta hau titi sannan mahaber ya dubi dadyn nasa yace
"to dady yau ina zamu fara zuwa ne? muazzam saraki ya dago daga duba daily trust dinsa dayakeyi yanamai qara gyara zaman gilashin fuskarsa yace "yau dai inaga mufara zuwa can nursing home
(wato barau dukko hospital)
ta yanki cikin gari son"
"to dady"
daga haka yayi shuru bai sake cewa komi ba ya maida kansa ga tuqin sosai,,, saima qara wa motar speed da yayi suka dauki hanyar asibitin ,,,,,,
[10/11, 2:45 PM] Xainab Documen: 🌊🌊🌊


*MAHABEER*!!!
🌊🌊🌊
Story and writing
by
XayynebπŸ’€πŸ’€


🌊🌊🌊🌊🌊
Fasaha online writers f.o.w.


🌊🌊🌊🌊🌊
πŸ…Ώ1⃣4⃣
🌊🌊🌊
basu d'auki wani dogon tafiya ba sosai suka iso *barau dikko hospital* d'in,
sun firfito dukkansu a motan knn sukaji daga bayansu ta gefen titin ana musu horn alamun su tsaya,
su a lokacin ma suna qoqarin shiga a cikin asibitin dan tsayawa mu'azzam saraki yayi kadan yayinda mahabeer da momy umaimah sukayi gefe,
a bazace kuma cikin tsabar mamaki mu'azzam ya qarasa kusa da alhajin daya fito cikin motar wacce ake musu horn a cikinta.
suka rungume juna cikin fara'a.
mutumin yace "haj mu'azzam saraki kuyi mana afuwa mun san mun muku lefi dan shekaru da yawa bamu wai wayeku ba,
sai alokacin mu'azzam saraki ya samu qarfin gwiwar yin magana yace
"wlh kuwa kai dai haj Muhammad ka mancemu kawai zakace a rayuwa, sai kace ba tare mukayi childhood namu ba,?
sannan ga karatun mu da muka yisa a tare tun daga primary har kuma zuwa secondry?
amman ka 6oye lokaci daya kwata kwata har nagaji da try number ka wlh haj Muhammad,
saifa danaje can gidanka nake tambayar masu gadin nan suke fada mun baku qasar, sunce second madam dinka hjy ni'ima ne keba lpia?.
Alhj Muhammad yace "eh wlh kuwa, kasan tun shekarun baya din nan da Allah yabamu rabon haihuwar a duniya bayan dogon lokacin da muka shafe muna neman ta, sai kuma bayan Allah ya bamun ne muka neme jinjirin nan dare daya wlh muka rasa shi, tofa tun lokacin haj mu'azzam ni'ima bata qara lpia ba kullum ciwo sabo yake komawa takai ta kawo wlh sam ni'ima bata iya cin abinci ynda ya kamata, nan da nan ciwo ya rufeta ko numfashinta baya fita ynda ya dace, asibiti mun je 2 amman aka kasa gano taqamaiman matsalan nata dole muka je mecca can wajen danginta anan muka samu wani qwararren doctor ya fara dorata kan magun guna, cikin ikon Allah ta fara dangana ta hnyar adduo'e da muke xuwa munayi mata dare da rana cikin ka'aba.
tofa bayan dan lokaci jikin ya dawo normal sai kuma taqi ta biyoni gida nijeria, wai ita nan wajen iyayenta zata zauna,, wlh haj mu'azzam a hakan ta kafe kan dole na qyaleta dan nasan hakan bai rasa nasaba da rashin jinjirin nata wanda har kwanan gobe bata daina kuka kan 6atar saba,
Haka na haqura a dud tsawon shekaru nan ina zarya tsakanin mecca da nan gida nijeria nan wajen hjy laria inyi mata wata daya itama kuma can inmata wata dayan,
Shiyasa lokaci yaimun qaranci kwata kwata wlh haj mu'azzam ga kuma business komi yai mun yawa a lokacin,
ana haka kuma ita mahaifiyar ni'ima Allah yai mata rasuwa ko wata ba'a qulla ba ynzun haka da rasuwar nata, mafarin knn shi mahaifin nata ya sameta a wajen kakarta bayan an gama makokin mamar tata yanata mata fada akan ta daure dai ta haqura ta dawo nan nijeria d'in kusa da mijinta zifi sauqi har a wajensa shima.
nan suma dangin nata suka yita lallashenta harta haqura amman da sharadin cewa wannan gidan namu bazta kuma zaman saba saboda yana tuno mata da d'an jinjirin yaronta, dan acikinsa tayi renon cikinta a wajaje daban daban na gidan dan haka sai dai asamo mata wani gidan bashiba tofa kaji yanda alamurran suka kasance haj mu'azzam.
girgiza kai muazzam saraki yayi yace Allah sarki Allah jiqanta zanje in mata gaisuwa insha Allah, kuma Allah shi bayyana muku yaronku a dud inda yake, dan wlh 6atan d'a babu dad'i har ma gwamma ace maka yau Allah ya kar6i abinsa akan 6atan nasa,
idanuwan alhj Muhammad har sun fara sauyawa a 6oye ya sanya hankicerf ya goge qwalla daga idanunsa na mikin tuno dansa da yayi? Shin yana raye?
to inyana raye cikin wane kalar mutane yake yin rayuwa? ya tashi a musulmi ne ko kuma kiristan?
yaci abinci ko bai ciba?
Yana cikin matsi na wahala koko yana hali na farin ciki da wadata,?
yana cen yana rayuwa da mutanen daya tabbatar sune haqiqanin iyayensa basu ba?
Allah sarki abinda ya fada knn a fili tareda wani murmushi mai cin rai,
dafasa alhj muazzam saraki yayi yace bakomi haj Muhammad insha Allah komin daren dadewa Allah zai nuna mana shi, karage yawan ddamuwa dan Allah saboda itama ciwone damuwar, addu'ar nan da mukeyi akai mu qara zage dantse insha Allah gskia zatayi halinta.
"hakane haj muazzam ngd sosai da kulawanka"
Muazzam saraki yace bakomi hj Muhammad,,
kuma zancen mgnr gida d kk kamance da gidana na kusa dani ba kowa a cikinsa ne?
kuma kaga ai zaiyi girman gidanka nakega ko?
kadawo ciki kawai na bakashi halak malak abokina,,,
kallonsa Alhj Muhammad yk yana mamakin tsagwaran kirki irinna alhj mu'azzam saraki a duniyar nn?
dudda yasan shima yanada dukiya kamar tasa amman har baiji qyashin bashi kyautar gida ba haka ba batareda ko asin shi ba? lallaikam shiko a rayuwa yayi sa'ar aboki nagari managarci wanda yasan ko bayan ransa bazai mance da lamarin ahalinsa ba zai riqesu amana kamar yanda zaiwa nasa.
cikin tsabar farin ciki ya fara fad'in "nagode nagode haj muazzam saraki Allah shi bar zumunci a tsakani,
"haba haba dan Allah kuma haj Muhammad ai babu zancen godia a tsakaninmu kama daina dan Allah abokina''
dariya sukayi dukkansu sannan mu'azzam sarakin yasake cewa"haj Muhammad muje ga family na cen kazo ku gaisa ko?
tare suka isa har wajen nan suka gaisa da mommy umaimah nan momyy umaimah take tambayarsa qawar tata ni'ima ta 6ata 6a kwana aru
aru?
"takusan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login