Showing 15001 words to 18000 words out of 88726 words
Chapter 6 - AUREN BAUTA(1 to End) complete By Maman Walid And Walida Mrs Aliyu.txt
ta fafutuka, Har yanzu a wannan halin suke inda sabit ya biya musu ummara suka kama hanyar ƙasa don su roƙi haihuwa
Ita badia sam abin be damun ta dama can ita ba child person bace ita ba mace bace me son yara ba don haka abin ko a ƙarƙashi takalmin ƙafarta wai rashin haihuwarta sam be dame ta ba
👩🏽🍳 *menu of d day*👩🏽🍳
*cornflakes crispy cake, miyar gyaɗa with tuwon shinkafa, coconut drink*
*cornflakes crispy cake*
*ingredients*
-corn flakes
-chocolate bar
-butter
-sprinkles (ko wane iri)
-marshmelow (optional)
-vanillah extract
-salt
*method*
1) ki narka chocolate da butter ko a micro wave ko a kan wuta amma pls kar a sakar masa wuta
2) idan sun narke sai ki juye su a roba sannan sai ki zuba vanilla da ɗan gishiri kaɗan
3) ki rugurguza cornflakes ɗinki da hannu ƙanana sannan sai ki zuba ki juya sai kasance kamar tuwo ne, irin zasu cure ne waje ɗaya amma duk da haka cornflakes ɗin zai kasance da ƙarfin sa
4)sai ki ɗauko cupcake case ɗin ki ki dinga ɗiban haɗin nan kina sawa kina ajiyewa, idan kin gama sai ki bi kowanne da marshmelow sannan ki watsa sprinkles ki saka a fridge domin yin sanyi sai aci
*tuwon shinkafa served with migar gyaɗa*
*ingredients*
- farar shinkafa ta tuwo
-gyaɗa
-tomatoes
-attaruhu
-albasa
-tafarnuwa
-citta
-wuyan rago
-curry
-alayyahu
-thyme
-maggi & salt
*method*
1) ki haɗa naman,maggi, gishiri, albasa, tafarnuwa sai ruwa a cikin tukunya ki dora ki barshi yaita dahuwa
2) soya gyaɗa sama sama ta yadda ɓawon gyaɗar zai fita, sai ki surfa ki cire ɓawon sai ki daka ko kiyi blending, ki haɗa tomatoes da attaruhu kiyi blending shima
3) idan naman ya ɗauko dahuwa sai ki zuba kayan miyar ki da soyayyan man da kike so amma kaɗan kasancewar gyaɗar itama zata fitar da nata man
3) idan sun ɗan tafasa sai ki dama dakakkiyar gyaɗar ki da ruwa ki zuba, ki ƙara ruwa iya irin ƙaurin da kike son miyar sannan ki ƙara maggi in baiji ba ki rufe ya ci gaba da dahuwa
4) idan ya dahu kin tabbatar da komai ya dahu, sai ki ɗauko alayyahun ki ki wanke sannan ki yanka sai ki zuba a miyar ki gare mata wuta ki bashi minti 1 sai ki sauke
5) ki wanke shinkafar tuwon ki ki jiƙa ta
6) ki zuba ruwa a tukunya wanda zai ishi shinkafar sannan sai ki rufe, idan ruwan ya tafasa sai ki tace jikakkiyar shinkafar ki ki zuba ki rufe don ya dahu
7) idan shinkafaɗ ta ɗauko tsotsewa sai ki rage mata wuta ya koma low saboda ta ƙarasa tsotsewa a hankali,
8) idan bayan ta tsotse sai kika ji bata dahu ba sai ki ƙara mata ruwan zafi amma karki taɓa ta ki barta haka akan low heat har ta shanye ruwan sai a tuƙa a kuma rufewa akan low heat ɗin
9) idan ta turara sai ki kwashe
*P S* ki sani dahuwar shinkafa ko ta ci ce ko ta tuwo ce ta fi son wuta kaɗan kaɗan da ta ɗauko dahu
*coconut and banana milk shake*
*ingredients*
-ruwan kwakwa
-ayaba
-ice cream ko madara
-sugar
-ƙanƙara
*method*
1) bayan ki markaɗa kwakwar ki kin tace ruwan to ruwan kwakwar shi zamuyi amfani da shi
2) ki yanka ayaba ƙanana ki haɗa da ruwan kwakwa ice cream ko madara sai sugar sai ƙanƙara sai kiyi blending ɗin su
3) idan suka marƙadu sai ki juye a cup ko jug sai ki ƙara yanka ayaba a kai ayi serving
👩🏽🍳 *Bon appetit*👩🏽🍳
*ASMA'UN SABIT*
[10/05 09:50] YAYA HAYAT: [4/17, 2:24 AM] 🥦: 🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦🥦
*A̺͆U̺͆R̺͆E̺͆N̺͆ B̺͆A̺͆U̺͆T̺͆A̺͆*
🍷🍽🥛
👩🏽🍳~(t̸h̸e̸ a̸m̸a̸z̸i̸n̸g̸ c̸o̸o̸k̸)~👩🏽🍳
🍳🍜🥘🍲🍛🍝🥗🌯🍛🍢🥠
ʙʏ ᴍᴍɴ ᴡᴀʟɪᴅ ᴀɴᴅ ᴡᴀʟɪᴅᴀ (ᴍʀs ᴀʟɪʏᴜ)
P⃗a⃗g⃗e⃗ 8🌹
Mummy tana zaune rannan da yamma sai ga hjy munnira sam mummy bata kawo komai ba, suka zauna suka gaisa sai hjy munnira tace
"hjy takakkiya nayi, wallahi iyayen asmau sunce a dawo da ita lkcn aure yayi"
Mummy ji tayi kamar hjy munnira ta soke ta ita sam bata taɓa kawo wa cewar wai asmau zatai aure ba, ta gama sakankan cewa kaji san kai
Gyara zaman ta tayi don wannan magana ce da a za yi ta sosai asmau zata tafi bayan sun gama sakin jiki da girkin ta ai da sake
"hjy munnira ya baki taɓa min wannan maganar ba sai yau" inji mummy
"yo hjy sai na gaya miki ai kema kinsan mace ce kuma wataran dole ne tayi aure ko ba haka ba" shiru mummy tayi don kuwa zancen hjy munnira gaskiya ne
Tattaunawa suka shiga yi inda daga ƙarshe aka yanke hukunci mummy zata neman mata miji a cikin ma'aikatan gidan tunda ko taje can ma sai Allah ya haɗa ta mijin
A haka sukai sallama akan idan mummy ta samo mata mijin zata kira hjy munnira
Mummy ta tara ma'aikatan ta maza sannan ta musu albishirin akwai yarinyar da take son aurar wa cikin su ko akwai me so
"kar ku damu sadaki da kayan aure duk ni zanyi"
Kusan mutane biyar suka amsa suna so amma tunda mummy ta ambaci sunan asmau sai kowa ya janye
Mummy ba yadda batai da ma'aikatan ba amma kowa sai ya ƙi, kowa sai ya dinga kawo uzurinsa
"wa zai auri wata asmau ga baƙi ga rashin fara'a" inji driver, babu yadda mummy batai ba amma fafur suka ƙi haka ta sallame su suka watse
Duk wannan abun da ake yi asmau bata san wainar da ake toyawa ba, hankalin mummy ne ya kuma tashi don duk yadda ta ɗauki abun ba haka yake ba
Shawara ce ta faɗo mata sai ta tara ƴaƴan ta ko akwai wanda zai auri asmaun in yaso sai ta zauna amatsayin cook ɗin daga baya idan ta girma ta mallaki hankalin ta a san yadda za a yi
Bayan duK sun taru amma banda sabit wanda yake ƙasa me tsarki shida matar sa, mummy ta gabatar musu da maganar da kuma hukuncin da ta yanke na ɗaya daga cikin su ya aure ta in yaso daga baya a san abin yi amma yanzu wannan shine kawai shawara
Shiru sukai kowannen su na jimamiba wanda yake son auren asmau, da babban ɗanta tafa ra
"isma'il me kake tunani"
"gaskiya mummy bazan aure ta ba saboda kwananan zan sake aure ƴar meduguri ce magabata kawai zan gabatar a fara shirye shirye"
Ako koma kan na biyu sulaiman shima ya kawo uzurinsa, mummy tana kallon muktar ɗan ta na uku yace
"gaskiya bazan iya ba matana sun iya girki"
Tooooo faaaa abu ya taru ya haɗar wa mummy
"yanzu duk cikin ku babu wanda zai auri yarinyar nan na wani ɗan lkc haka kune son yarinyar nan ta tafi, a banza a wofi" ta faɗa ranta a ɓace
Kowannen su ɗauke kansa yayi mummy ta dinga faɗa kamar ta ari baki dukkan su suka tsuke baki can sai sulaiman yace
"mummy ai mu mun matan mu sun iya girki, ɗan autan ki ne matar sa bata iya girki ba kuma yarinyar nan kamar saboda su take zaune me zai hana ki aura masa ita"
Dukkan su suka amsa da haka ne kam shi kaɗai ne ma mata ɗaya
mummy shiru tayi tasan halin sabit da rigimar sa zata iya lanƙwas kowanne su amma banda shi,
"kun san halin sabit zan iya lanƙwasa ku amma banda sabit taurin kansa yafi komai"
"mummy ba sai ayi auren ba kafin ya dawo sai dai kawai ya dawo ya tarar da amarya" muktar ya faɗa yana d ariyar mugunta don ba ƙaramin rigima za a sha da sabit ba idan ya dawo ya tarar da ya angwance 💑
Babu yadda mummy ta iya haka ta ɗauki shawarar ƴaƴan ta dole ne ta aurawa sabit asmau kafin ya dawo in yaso idan ya dawo ayi duk waccd ayi da shi ita dai ta riga ta gama
Bata ɓata lkc ba taje ta faɗawa mijinta batun auren sabit ɗin da asmau amma bata faɗa masa dalilin auren ba
Dady sai yace
" to shikenan dama gobe zani kano ɗaurin aure sai kawai mu ƙarasa can garin su yarinyar sai a ɗaura mata tunda kince ya dawo kike son ayi"
Mummy sai taji daɗin yadda sam dadyn be yi tambayoyi akan auren ba
Aka gama shirye shiryen auren duk mutanen gidan suka dunguma sai kano auren sabit da asmau har da asmaun wacce sai a mota sannan mummy tai mata bayanin auren
Da yake da ƙuruciya a tattatare da ita sai ta yadda, lfy suka isa kano suka sauka a hotel ɗin tahir guest palace suka kwana
Kashegari suka kama hanyar azore, kasancewar ba a san da zuwan su ba don haka suna isa suka sauka a gidan me garin na fulanin
Suka gabatar da abinda ya abinda ya kawo su sam me garin be gane asmau ba sai da tayi bayani sannan ya gano ta
Nan da nan yasa aka kira kawun na tan ya zo shima aka gabatar masa da maganar auren
Mummg tayi mamaki da taji cewar basu suka tura hjy munnira ba da maganar auren suka ce musu su rabon da hjy munnira ma ta bada kuɗin aikin yarinyar har sun manta
Ko kaɗan dady be ji daɗin wannan abun ba yarinya tana aiki amma sam iyayen ta basa samun ladan aikin ta, sai da ya biya su kuɗi a madadin na aikatau ɗin ta sannan suka kuma gabatar da aurawa ɗan su asmau
Babu wani ja'inja wan mahaifin asmau ya yadda inda atake a ka ɗaura auren sabit da asmau akan sadaki mafi ƙanƙanta
Baffa wan mahaifin asmau shi aka ba sadaki amatsayin sa na uban ta, daga nan daddy ya shiga rabon kuɗi
Mutanen gari sai turuwa suke suna ƙara ƙaruwa kamar sallah ana cewa ai asamau ta je binni ta haɗu da me kuɗi
Baffan ya so su kwana amma sai suka kawo masa uzurin zasu koma ne kasancewar kashegari ake sa ran tasowar ango sabit 😂
Amma sai da suka ƙarasa gidan baffan suka ga gidan sannan suka kama hanyar kano inda suka sauke daddy a kano sannan suka kama hanyar abuja
Mummy kamar ta zuba ruwa a ƙasa ta sha ganin ta mallaki asmau yanzu asmau ta zama mallakin ta, kuma babu abinda zai raba ta da ita
```ni kuwa mmn walid nace anya kuwa sabit zai yadda ya zauna da baƙar mace amatsayin matar sa mutumin da baya son baƙi```
******************
Cikin hukuncin Allah sabit da badia suka dawo gida lfy sai da mummy ta kwaɓi dukkan ƴaƴan ta akan kar wanda ya faɗa masa maganar auren
Don haka ko daya sauka sam be sani ba hidimar sa kawai ya ci gaba tare da kwasar girkin wacce a yanzu take a matsayin matar sa
Itama mummyn ko da suka dawo bata ce asmaun ta bar inda take ba tunda auren ai kamar suna ne, don kawai asmaun ta zauna a nan wajen su
Sai da suka huta suka nutsu sannan mummy ta kira shi da matar sa badia da kuma asmau dukkan su ta tara su a falo
Sabit da badia da mummy suna zaune a kan kujera inda asmau take zaune a ƙasan carpet fuskan nan tata sam ba annuri don kuwa tasan kiran menene
Sai bayan da kowa ya nutsa sannan mummy tace
"sabit bayan ka tafi matsala ta taso ta yadda dole ne a aurar da asmau don haka sai nai mata aure"
Kallon mummy yayi
"yo mummy ina ruwana da auren ta ai aiki aka ɗauke ta kuma ake biyan ta idan zata iya aikin da auren to idan kuma baza ta iya ba ta ƙara gaba ai ba ita kaɗai ce ta iya girki ba sai mu nemi wata"
"ai kai ne mijin" tsab sabit yaji abinda mummy tace amma sai yake jin kamar kunne sa ne yake masa kuwwa
"mummy me kinace" bata maimaita ba face idƙ da ta zuba masa
"kamar naji kince nine mijin wannan abun koo" ya faɗa yana nuna asmau
"ashe kaji kuma wallahi da wasa ka sake ka furta mata kalmar saki wallahi sai nayi mugun ɓata maka wallahi sai kaga ɓacin raina tunda auren ka da asmau babu wanda zai taimaka sai kai
Tunda de duk ƴan uwanka kowannen su yana da mace biyu kuma acikin biyun akwai wacce ta iya girki amma kai kana zaune da ɗaya ɗayar ma wacce bata san darajar aure ba balle wani miji"
Faɗa mummy ta dinga yi ta inda take shiga ba tanan take fita ba tsab ta san halin sabit in tak masa lako lako sai ya watsa mata ƙasa a ido gwanda tai masa ta ruwan zafi in yaso duk a dafe a tare
Sabit shiru kawai yayi yana saureran mummy wannan shine wai a dake ka a hana ka kuka, ita kuwa badia tana zaune a gefe ta cika tayi fam kamar zata fashe wannan shine ga mari ga tsinka jaka
Ga kishiya ga kuma kushen ta da mummy take yi wai bata iya girki ba
"amma mummy duk a gidan nan a rasa wanda za a haɗa da wannan halittar sai ni" ya faɗa ran shi a ɓace kalmar nan ta daki asmau sosai wai halitta
Ɗagowa tayi ta maka masa harara sai kace ita cewa tayi tana son sa ai ko maza sun ƙare a duniya ya rage daga ita sai sabit baza ta so shi don ta fahimci ɗan renin hankali ne
"mummy kin san tsari na na mace ɗaya sannan kinsan ni ba me son mu'amala ne da baƙin abu ba balle wai ace matata ce baƙa" ya faɗi kalmar ```matata``` kamar wanda yake da kashi a baki
"gaskiya mummy da sake ya za ayi in shigo in kalli wannan baƙin abun a ɓangare na ai wannan ma sai ta saka ni in ta firgita cikin dare, in matsala bata sa zuciya ta bugawa ba wannan halittar zai sakani" ya faɗa yana ƙara nuna asmau cikin tsana
Asmau iya ƙulewa ta ƙule ƙarshe ita tunda take ba a taɓa ci mata mutunci ba kamar yadda sabit yai mata *shin wai baƙi muni ne* ta tambayi kanta
shiyasa fa ita tunda taji da wannan ɗan rainin hankalin za a haɗa ta dashi shi taji sam bata san abun amma kasanceqar bata da mafita yasa ta yadda da lamarin
Sabit ya cigaba da kushe asmau kamar ba gobe inda mummy ta tsaya ta barshi ya gama faɗin abinda yake son faɗa sai daya zage ta tas sannan yai shiru yana huci
"to in banda abin auta ai na faɗa maka dalilin auren ko ba haka ba, kuma ba wani da zai haɗa ka da asmau tana can boys quaters tana aikin ta kai kuma kana ɓangaren ta me zai haɗa ka da ita, da matar ka ta iya girki shi kenan sai in raba auren itama taje ta auri wani"
Jin cewar akwai lkcn da auren zai yi expire ne kuma ga yadda tsarin auren yake na asmaun baza ta dinga zuwa ɓangaren sabit ɗin ba ya sa shi kwantar da hankalin sa
Ya kakkafa asmaun doka na in ta ganshi ta canza hanya don baya son yana cin karo da mummunar fuskar ta sannan kar ya sake ya ga ƙafarta a ɓangaren sa duk aka gama maganar kowa ga san matsayin sa sannan mummy ta sallami kowa
Sam badia ba haka ta so ba taso ace sabit ya bijirewa mummy amma sai taga saɓanin hakan
Ko da suka koma ɓangaren su sai faɗa, wai dama ƙila ya so auren ne shi yasa ana faɗa masa ya hau borin ƙarya in da da gaskene ai da sai ya saki asmau
Yai mata bayani yai mata rantsuwa amma ina sam ta ki yarda kawai sai ya share ta yayi wucewar sa ɗakin sa shima yaje yaji da abinda ya dame shi
[4/17, 4:50 PM] 🥦: 👩🏽🍳 *menu of d day*👩🏽🍳
*brown rice served with liver and egg sauce, Apple milkshake*
*brown rice*
*ingredients*
-shinkafa
-man gyaɗa
-maggi
-curry
-green beans
-carrot
-peas
-attaruhu
-albasa
-tafarnuwa
*method*
1) ki wanke shinkafar ki tas sai ki shanya ta don ta bushe, idan ta bushe sai ki ɗauko tukunya ki zuba mai sosai sai ki saka tafarnuwa da albasa amma kaɗan
2) idan suka ɗan ɗauko soyuwa sai ki zuba shinkafar ki ki ci gaba da soyawa, kina yi kina juyawa har sai tayi brown sosai sai ki sauke ki tsane man
3) ki yanka attaruhu da albasa yankan cubes, sai ki zuba a tukunya da ɗan mai, sai ki cigaba da soyawa, idan sun dauko soyuwa sai ki zuba ruwan da zai dafa miki shinkafar ki
4) ki zuba maggi, curry thyme da duk wani seasoning da kike so, idan ya tafasa sai ki zuba shinkafar ki tafasa ɗaya sai ki zuba carrot, peas, green beans ki rage wuta, idan ya dahu sai a sauke
*liver and egg sauce*
*ingredients*
-tomatoes
-attaruhu
-albasa
-hanta
-kwai
-curry
-thyme
*method*
1) ki wanke sai yanka hanta ƙanana sannan ki tafasa ta da maggi, thyme, tafarnuwa, albasa
2) idan ta dahu sai ki sauke, ki jajjaga attaruhu, tomatoes albasa da tafarnuwa
3) ki zuba mai a kasko sai ki ɗan saka masa albasa ko tafarnuwa don yayi zafi, idan yai zafi sai