Showing 30001 words to 33000 words out of 88300 words

Chapter 11 - ABDULMAJEED BOOK by Meryam Abdul.doc

09 Oct 2025

1592

report sheet yake, ba abinda ya damesa....

Likitan ya tabbatar musu ba wata babbar matsala bace, ciwon a jininsa yake so yayi inherited ne saidai ya kamata a nema mishi medical saboda idon yayi lasting, sai yanzu Ameena ta tuna tana ganin idon Auwal suna irin hakanan sometimes, no wonder shiyasa yake amfani da glass always Ashe medical ne.


**************

Har k'ofar gida suka sauke malam Garba da k'annin Ard'o sannan suka isa gida suma.


Da kallon mamaki iya Hari ta bisu sannan tace "malam ina kuka shige tun safe, wagga kuma fa?"

"Ai dai kin kawo tabarma tukun" tabarma tasa Shatu ta kawo tare da shimfida sannan ta kawo musu ruwa.

Zama sukayi sannan Baba yace Asma'u tasha ruwa ba musu tasha, guri ya nunawa Hari da tayi musu tsaye k'erere tana musu kallon dibar arziki, tuni jikin Asma'u yayi sanyi.

Zama tayi sannan Ard'o ya gayamata dukkan abinda ya faru, mik'ewa tayi cike da gatsali.

"Mi wagga uwar mata"................






=؄? Meryerm Abdool=؄?
[8/11, 3:14 PM] =؄?Meryerm Abdool=؄?: =ؤ? ```ABDULMAJEED``` =ؤ?

(' *Servant of Majesty* ('



Na
=؄? _Meryerm Abdool_ =؄?


? *Pure moment of life writers*
P.M.L=ت?
(We don't just entertain and educate we touch the heartd' of the readers=???)




*All thankful and praises be to Almighty Allah, d one who give me chance to live and make Muslim in Muslim ummah without my knowledge,=?O?
```Alhamdulillah, mashaa Allah, after long journey and go up and down crossing over many obstacles finally I get it, I mean my NCE result, I wish my self, big success in every stage i go, thank you Allah for every blessing upon to me hidden one and d one that appear``` =?O?



=??? *Episode* 121--126




"Mi! Wagga uwar Mata? Hehehe ah dole daga zuwa gaisuwar iyaye da nema, a baku aure baki d'aya, yo dama daga ganin wannan kasan neman kai ake da ita, an tsofe gida ba mashinshini yo ai dole, tab wayaga akwala" sannan ta juya ga Abdulrahim tare da nuna shi da yatsa.

"Tir! Amma ka bani kunya, dama akan wannan mai bak'ar huska da bak'ar kamane yassa kak'i 'yar uwarka, yo Allah na tuba wannan ai sa'a tace, to nidai bani cikin wannan kwaba taku ehe" ta k'ara sa tare da hararan Ard'o.

"Ke! Hari ashe dama haukarki da rashin hankalinki yakai har haka, ashe baki da imani bansani ba, yanzu da ace cikin d'iyanki ne hakan ta faru dasu zakiji dad'i?"

"Aa Malam yada kiramin rashin hankali da hauka daga fad'ar gaskiya? Kuma ni d'iyana tuff! Tohe musu mugun yawu, nidai nace bana cikin wannan auren, kuma ban d'auka a sirika ba ehe" tana gama fad'i ta wuce tana gunguni.

Girgiza kai Ard'o yayi "Allah ya shiryeki" sannan ya dubi Asma'u wacce tunda Hari ta fara tu'annatinta kanta ke k'asa tana zubar da hawaye zuciyarta sai zafi take Mata "inna lillahi wa'inna ilaihirraji'un, Allahumma ajirni fi musibatih wa'akhlilni khairun minha, oh ni Asma'u tawa kalar jarabawar kenan, ya Allah ka bani ikon cinyeta...."

"Kiyi hak'uri 'yata Kada kalamanta su dameki, kamar yadda na gayamiki zan rik'e kamar 'ya'yana, kada ki damu ba abinda zai faru sai Alkhairi" sannan ya dubi Shatu wacce duk jikinta yayi sanyi abinda uwar tasu tayi sam baiyi Mata dad'i ba, ita bataga aibun Asma'u ba, dan daga gani tafi Saude nesa, ita dama can Saude bata yi Mata, wannan saidai Lanti da suke k'awance kullum suna tare, tasan Idan taji itama sai tayi tata haukan(dake anyima Lantanar aure).

"Aisha kai matar yayanki wancen d'akin, su fara zama can kafin a Gina mata na, ni zan koma d'akin zaure" (d'akin sa ne da Abdulrahim gina mishi bada dad'ewa ba).

"Muje Aunty" mik'ewa tayi ba musu ta bita, daga Leda sai katifa, kujerar roba sai kwaba da littafan musulunci ke cikin d'akin, zama tayi gefen katifar, ita kuma Shatu ta zauna k'asan Leda "Aunty don Allah kiyi hak'uri da abinda iya tayi miki, haka take komu data haifa yimana take yi".

Murmushi yak'e ta k'irk'iro " ba komai k'anwarta ai nima uwace a gareni kada ki damu" jinjina kai Shatu tayi "lallai yaya yayi dacen mata, duk wannan abun da iya tayi mata" ta fad'a cikin ranta, ita kam Wallahi ta kwanta mata a rai, nan tayi ta mata fira dan ta kwantar mata da hankali.

"Modibbo kaje ka rarrashi matar ka, ni zan fita na samo mata abinda zataci" yace ma Abdulrahim da yayi sugum tsabar kunya da bak'in ciki abinda uwar sa tayi.

"Baffa Aida ka Bari naje, ka huta kaima" .

Murmushi Ard'o yayi "kaidai kayi yadda nicce kawai" tare da ficewa daga gidan, shima tashi yayi ya shiga d'akin, shigarsa yasa Shatu yi mata sallama ta fita.

Zama yayi daf da ita tare da ciremata hijab jikinsa ya janyota yana d'an bubbuga mata baya Alaman rarrashi, cikin muryan rad'a ya fara mata magana "kada ki damu matata koda duka duniya zata taru ta k'iki nikam ina tare dake, bazan taba barin ki cikin kad'aici ba, zan game miki bango abin jinginawa" haka yayi ta rarrashinta da tsadaddin kalamansa na k'auna, ita kuma tai lahu a jikinsa tana saurarensa yayinda wasu kasu na damuwarta suka tafi ( hmmm k'auna kenan Allah ya had'a kowa da masoyinsa na gaskiya Ameen).




**************



B'angaren Yusuf kuwa tun ranar da Sakina ta bashi labarin Ameenah yaji wani irin tausayi da k'aunarta sun k'ara lullub'esa danshi tun ranar da ya fara ganinta a school d'in, yaji ta kwanta masa komai nata burgeshi yake musamman natsuwarta, saidai bai San ta inda zai fara ba, dan iya sananinsa da ita bai tab'a ganinta da ta kebe da namiji ba, sai shi shima d'in da sunan karatune kuma tare da Sakina, gashi shiba ya tab'a soyayya ba balle yace yasan yadda sai samota barin abin a ransa yayi kawai, saidai daga ranar kullum cikin tambayanta Abdool yake yana lafia, haka zai sayo kayan wasa dana kwalama ya bata ta kai mishi, koya kirata a waya yace ta bawa Abdool suyi hira, yaita yi masa shirme yana biye masa, ita abun har dariya Suke bata wai friends ne, dama ance mai da wawa hakan yasa ta sakance dashi wani lokaci sai sake-sake zuciyarta ke Mata game dashi saidai nan da nan take saurin ka yima Kanta fad'a akan bama zai yuyu ba.

Ko bayan kammala karatunsu zumunci bai yanke ba, yakan kira ko ita ta kira lokaci zuwa lokaci, ko lokacin da akayi Auren Sakina yaje Bk dan kawai ya had'u da Ameena danshi asalin d'an Koko-besse(local government ne a Kebbi) ne karatu ya kaishi Argungu.

B'angaren su Hajia kaltume kuwa tun suna saka ran dawowar Auwal shiru shekaru sun tafi ba labari hakan yasa suka fitar da rai, har anyi Auren Maryam da wani Dr, inda suka wuce Germany an turashi course, Ayuba ma ya k'ara Aure, yayi yayi da Rafia suje hospital amma tak'i tana tsoron tonon silili, Hajia kin amince tayi da Auren saboda kar abatama 'yar gaban goshinta, saida ya nace sannan ta yadda dan itama rashin haihuwa na damunta, saidai duk da haka Rafia CE ke mulkinta a gidan sai abinda tace.

_wannan kenan_



***************

Kawunnan Alhaji Abubakar sukazo daga k'auye sukayi masa tas wai ya maida d'iyansa d'iyan yahudawa, ita waccen saboda ta isa da Kanta tabi namiji ta barsu cewa da Asma'u (baki ke yanka wuya shiya kira ya fad'a musu) sannan ita kuma wanga shekararta nawa da rabuwa da mijinta ance karatu to ai tw gama, zaman me take idan ba tana bin maza ba, taya za'ace bata damu ba, cin mutunci dai inda Suke shiga banan Suke fita ba, kalamansu sun mugun b'ata ransa, amma ba yanda zaiyi iyayensa ne.

Bayan tafiyar su ya kira Ameena yace mata tayi k'ok'ari ta fitar da miji cikin masu sonta tayi Aure, amma cikin sanyi yayi Mata maganan dan shima tausayi take bashi, itakam ya zatayi bayan bamai zuwa inda take, da za'a bud'e ranta tafi son tayi Auren nan kota huta da surutun mutane, amma ya zatayi.

Cikin satin Alhaji Sada yazo dubasu shima dai maganar d'aya ce ta daure ta manta baya tayi Aure.

Kwance take kan gado tunanin abin duniya ya isheta, tana matuk'ar son aure dan itama ai rayuwa ce kuma matashiya mai cikakikiyar lafia, saidai tasan komai yanada lokaci da lokaci yayi ba makawa zatayi shi, tana rokon Allah, kuma tana da tabbacin zai ansa mata, ringing din wayarta ne ya dawo da ita daga duniyar tunani.

Sunan Yusuf ne ya bayyana kan screen sauke numfashi tayi sannan ta d'auka, bayan sun gaisa ya tambaya Abdool daya dad'e dayin bacci yake CE mata.

"Ameena wai yaushe ne zamuzo Argungu musha biki?"

A bazata taji tambayan shima kenan ya k'osa tayi Aure? Murmushin dole ta k'irk'iro "Umm Yusuf bada dad'ewa ba inshaa Allah"

Jin sukayi gaba d'aya kowa na sak'a Abu a ransa, shikam yau ya shirya fallasa sirrin ransa gareta kota amince ko tak'i, gyaran murya yayi "Ameena" ya kirata cikin wata irin murya "Na'am".

"Inaso kiyima magana ta kyakkyawar fahimta ki d'ora a mizani mai kyau," sannan yaja hanci "maganan gaskiya Ameena I'm deeply in love with u".

" what " shine abinda ta fad'a cikin firgice, tare da katse kiran.

Kanta ta dafe "lahaulah walakuwwati, meke shirin faruwa ne, kai never yaudara kawai zaiyi...." Karan shigowa message taji, bud'ewa tayi.

_"everyone is a someone dream, and ur a my dream, pls don close ur heart to d one that is in need of u, never say goodbye 2 ur lover accept it as destiny, as I said I really love u with one heart, don't let me go astray..!"_

Tana gama karantawa kiran sa na shigowa d'auka tayi ba tare da tayi magana ba "Haba Ameena ki yadda dani da soyayya ta nayi miki alkawarin bazan cutar da ke, zan rikeki Amana da zuciya d'aya pls Ameena ki yadda dani".

" taya Yusuf taya zakace ni, koma manta nifa bazawara ce, bazawarar ma mai d'a, kaifa saurayin da bai tab'a Aure ba, to taya hakan zata kasance?"

"Haba Ameena kada ki canja daga yadda ba sanki mana, nasan ke mai ilimi CE, fiyayyen halitta da wace Mata ya fara? Nina ganki a yadda kike nace ina sonki, saidai idan sonane bakyayi daban ne, amma kima var wancen maganar.

K'aryane ne tace batason Yusuf domin ya had'a komai daya cancanci aso namiji domin shi, to amma ya fa?.

" Koda zan amince mata saika je kayi magana da iyayenka idan sun amince maka, sannan zan amince ".

"Shikenan Ameena inshaa Allah, zanyi yadda kikeso, ki shafan kan Abdool, saida safe".

Wayar tabi da kallo, ita haka take ganin abun kamar almara, mik'ewa tayi ta d'auro alwala tahau dadduma tayi raka'a 2, sannan ta fara Addu'ar istikhara(Neman zabin Allah) kamar haka:-

_Allahumma inni astahiruka bi ilmika, wa'astagfiruka bik'udratika, wa'as'aluka min fadlikal azim, fa'innaka tak'dir wala ak'dir, wata'alam wala a'alam, wa anta allamul guyuwbu, in kunta ta'alamu anna hazal amru(saika fad'i buk'atar ka) khairun liy fiy deeniy wama'ashi wa'akibatu amri, fak'durhu liy wayassirhu liy summa barak liy fiyhi, wa'in kunta ta'alamu Anna hazal amru sharrun liy fih deeniy wama'ashi wa'ak'ibati amri, fasrifhu anni wasrifni anhu wak'dul liy khairan haisu kana summa raddani bihi._

Fassara

*ya Allah ina Neman zabinka domin iliminka, kuma ina Neman ka bani iko domin ikonka, kuma ina rok'onka daga falalarka mai girma, domin Kaine mai iko ni kuma bani da ikon, kuma kaine masani ni kuma bani da sani, kuma Kaine masanin abubuwan fake, Ya Allah! Idan kasan cewa wannan al'amari (ka ambaci buk'atar) Alkhairi ne a gareni cikin addinina da rayuwata da k'arshen al'amarina (wata rayuwar ) da magaggaucin al'amarina da majinkircinsa, ka k'addara mini shi, kuma ka sauk'ak'e mini shi, sannan ka Albarka ce ni a cikinsa, kuma idan kasan wannan al'amari sharri ne, gareni a cikin, addinina da rayuwa da k'arshen al'amarina (a wata rayuwar) da magaggaucin al'amarina da majinkircinsa, ka kawar da shi daga gareni, kuma ka kawar dani daga gareshi, ka k'addara mini Alkhairi a duk inda yake, ka kuma sani in yarda dashi*

(Cikin husnul Muslim take, yana da kyau komai bawa zai gabatar a rayuwa ya nemi zabin Allah a ciki. Allah yasa mudace)


Bayan ta kammala ta nad'e dadduma tare da kwantawa kan bed, tana tunanin wannan al'amarin,sannu a hankali natsuwa ta fara shigarta, a haka bacci mai dad'i yayi gaba da ita.................





_masoyana ina Neman addu'o'inku, I really in need of it=?O?





=؄? Meryerm Abdool=؄?
[8/12, 6:07 PM] =؄?Meryerm Abdool=؄?: =ؤ? ```ABDULMAJEED``` =ؤ?

(' *Servant of Majesty* ('



Na
=؄? _Meryerm Abdool_ =؄?


? *Pure moment of life writers*
P.M.L=ت?
(We don't just entertain and educate we touch the heartd' of the readers=???)





=?O?







=??? *Episode* 126--130






Koda Yusuf ya jema iyayensa bai samu matsala da yake yayi dace da iyaye masu hangen nesa, sunce tunda shi yake sonta in har anyi bincike 'yar kirki ce to su basu da matsala, amma 'yan uwansa sunce sudai basu amince ya auri bazawara ba yana saurayi dashi, saida Baban yayi musu fad'a yace "meye naku a ciki tunda a hakan yakeson abarsa, kuma ma in banda abinku, fiyayyen halitta ma da bazawara ya fara, to meye dan yace zaiyi koyi dashi idan har ba zaku bashi k'warin gwuiwa ba bai kamata Ku hanashi dan haka kar in sake jin wani daga cikinku ya soki wannan tafiyar" da haka Baban ya kwabesu dole suka hak'ura badan ransu yaso ba.

Koda ya fad'ama Ameena tayi farinciki sosai a ranta amma bata wani nuna mishi cewa kawai tayi "to yayi" sauke numfashi yayi "Haka kawai zakice Ameena tah, kamar bakya farinciki".

" um inayi mana tome kakeso ince ne".

Smiling yayi kamar tana kallon sa harda lumshe ido " cewa ya kamata kiyi yaushe zaka turo my love".

Dariya zancensa ya bata dama tasan Yusuf da barkwanci kamar me "au dariya KO, ai gara ma ki gayama Baba dan kada ayi mai ba zata, dan bazan tsaya kallon ruwa ba kwado yazo yamin kafa" nan ma murmushi kawai tayi dama Ameena ba yawan surutu...

"Um nidai bana Abdool dan naga yau miskilancin ya motsa" nan ta ba Abdool sukayi ta fira kamar wani babba dama Abdool badai wayau ba, in yayi wata magana ka d'auka fad'a mishi akayi.

Malam Sa'id mahafin Yusuf yayi duk binciken da ya dace ya kuma tabbatar da Tarbiyar Ameena, hakan yasa ya gaya ma 'yan uwansa domin Suje su nema nasa auren.

Lokacin da Ameena taje ma su Baba da labarin sunyi farinciki Sosai dama babban burinsu kenan Ameena tayi aure, shima yayi nashi bincike kamar yadda addini ya tsara, hakan yasa saka shiga cikin maganar har an tsaida rana wata uku masu zuwa.

Suma su Yusuf ba wasu masu arziki bane akwai dai rufin asiri, nan family house d'insu, aka gyara wasu dak'una biyu aka maida mata room and parlour sai toilet, ba laifi zaman dai mutum d'aya a talauce ba sarauce ba.

Alhaji Sada ma da yaji maganan Auren yayi mata murna Sosai, kuma yace ko bayan tayi Aure Abdool zaici gaba da zama gurin su Mama, dan yasha alwashin saidai in Abdool ya girma yakai Kansa Sokoto da kansa tunda dai sun nuna basa ra'ayinsa har gara iyayensa maza suna zuwa dubashi sa'in sai kuma Maryam kafin tayi aure duk da Hajia ta hanata zuwa hakan bai hana in Alhaji zaije ba, ta bishi wani sa'in kuma ta bada Abubuwa akai masa.

Cikin ikon Allah Anyi Aure lafia cikin farinciki ranar Ameena tasha kukan rabuwa da iyayenta uwa uba kuma Abdool shima dai yasha naji kukan dakyar aka banbareshi jikinta, a son Yusuf ma yaso abasu shi amma Baba yace Aa a barshi nan yayi karatunsa lokacin yana 6years yana primary 1, haka dai Ameena ta tare cikin aminci a gidan Angonta Yusuf.

Farkon Auren ta had'u da kalubalen dangin miji haka zasuzo suna yad'a mata magana, da yake macece mai matuk'ar hak'uri hakan yasa sam bata nuna tamasan sunayi, Amma kam surukarta suna zaune lafia, yawan kyautata Mata da dawainiya da take Mata, haka zata saka Yusuf ya d'auko kayansu ita da Abbansa su had'u su wanke su goge, komai ta dafa da nasu, suma 'yan uwan nasa da yake yayin nashi Mata ne duka suna gidan mazajensu sai dai in sunzo, shine namiji babba sai k'annin sa, hakan yasa in sukazo tana yawan kyautata musu gada Sam batada rowa ko kyashi tuni suma ta saye zukatansu(dangin miji saida kyautata ake zama lafia note women).

Taci gaba da teaching d'inta dan an samo mata transfer haka tana business d'inta, shima dai Yusuf teaching yake yana kuma zama kasuwa inda mahaifinsa da haka suka rufama junansu asiri Sam bakajin Kansu, zaman k'auna da soyayya suke dan sai yanzu tasan lallai Yusuf son gaskiya yake mata, kullum cikin tattali da nuna mata k'auna yake, Sakina ma anzo bikin tayi murna sosai dama ta dad'e tana hango son Ameena a idon Yusuf.

Tana zuwa Argungu lokaci zuwa lokaci har yanzu dai ba labarin Asma'u abin kullum yana ranta "oh ina zamu ganki Asma'u, Allah ka bayyana mana ita ka tsareta a duk inda take" kullum shine Addu'arta, Abdool na zuwa mata idan anyi Hutu.

Shekararsu 2 da Aure Yusuf ya samu Aiki a NNPC KADUNA, ba k'aramin farin???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?ciki sukayi da cigaban da ya samesu ba, haka yaje yayi interview aka bashi upper, watansa uku sannan ya dawo, nan ya gayama iyayensa zai wuce da Ameena dan an bashi gida, nan sukaje Argungu sukayi musu sallama, nan ma Yusuf saida ya tada maganar son abasu Abdool, hak'uri Abba ya basu yace kada su katse mai karatu, hakan suka wuce badan ransu yaso ba, irin kulawarda Yusuf ke bama Abdool shiyasa Ameena k'ara sonsa da ganin girmansa, haka sukayi bankwana da yan uwa da abokan arziki suka lula

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login