Showing 3001 words to 6000 words out of 88300 words

Chapter 2 - ABDULMAJEED BOOK by Meryam Abdul.doc

09 Oct 2025

1604

ita kam sai uh da uhum da to take binsa dashi.

Aiko har suka isa ba'a samu Wanda ya daga ido ya kallesu ba saboda sanin hali, haka yake gadinta kamar kwai, ba kuwa ubanda ya isa ya kalleta balle yace yana sonta duk kuwa da dimbin masoya da takeda shi, amma suna gudun rasa rai dan k'aramin aikinsa ne, kisa.

Saida yaga shigarta sannan ya juya zuwa sabgarsa..........



_Rikici ba gado ba_ >?#?=??









=؄? Meryerm Abdool=؄?
[7/4, 10:31 PM] =؄?Meryerm Abdool=؄?: =ؤ? ```ABDULMAJEED``` =ؤ?

(' *Servant of Majesty* ('



Na
=؄? _Meryerm Abdool_ =؄?


? *Pure moment of life writers*
P.M.L=ت?


*DOLE NA JINJINA MUKU*

*MAMAN USSEY*
*ABDOOL AAJ*
*FATYY AZLAND*
*UMMI A'ISHA*

_kud'in daban kuke, kamar yadda halinku na k'aramci ke nuna Ku, bazan gaji da fad'a ba wato da bazarku nake takawa =؃?


=??? *Episode* 16--20




Saida sukayi fresh up suka d'an ci abinci da yake an shirya musu better, amma Abdool kad'an yaci dan idan da abinda ke bashi wahala to cin abinci ne.

Maamii ya kira ya fad'a mata sun sauka lafiya tare da gaisawa da k'anninsa wad'anda ya fara missing tun yau, cikin gida suka shiga suka gaida da kakarsa wato Haj, Saude wacce ta ansa su sama2 ko halinta ne haka oho!.

Daga nan suka shiga sauran gidajen suka gaisa da iyaye, yayyi, da kanni, daga nan suka koma inda tsoho mai ran k'arfe inji Abdool fa.

Hira suka sosai kaman ba wad'anda suka sha hanya ba har 12, Alhaji Sada yace suje su huta zuwa gobe kuma aci gaba.

"Wane gobe Alhaji nida zanyi sammako saidai na barku da Hakeem."

"Au abun 'yar hakane shine ka gudu *Yabo* dan kada ka zauna Sakkwato ?" Alhaji ya fad'a yana hararan Abdool.

Dariya yayi "Alhaji aiba laifina bane kuma ai anan Sokoto akwai consultant doctors da yawa k'auyukan sunfiku bukatar likita."


"Ho dan nema badai iya fad'a ba, Allah ya taimaka, k'ilama acan ka samo 'yar budurwa, koda yake naga alaman tsoron mata kakeyi, kila sai munyi maka gangami an d'aura maka a k'afa."

"Hhhhhhh kajika da shirmen tsufa, an gayama ni Kaine, aini matata ba'ama haifeta ba" shidai Hakeem sai dariya yake suna burgesa.

"Aa kak'i cewa mamarta ma ba'a haiheta ba, ja'iri zanso naga wacce zata aureka da shirmen nan naka, kaidai ba abinda ka bari na 'yan fari"

Dariya sukayi banda shi murmushi kawai yayi tare lumshe ido.................




_wannan kenan_




^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^



Zaune suke a Dandali, wasu na gad'arsu yayin wasu ke samartaka, wasu na siye da siyarwa, "Laure kina zuwa Yabo ran juma'a kai nono?"

"Kai Delu kema kesan dolena intahi inhar inason in tsira da mutuncina, Iya Hari, tun yau tayo tatsarta baki ganai ba mai yawa kuma nid'ai."

"Aa na d'auka ko mutuminki ya hana kinsan shi dole yabi dokarsa koya taka ta."

B'ata fuska tayi tace "wane mutumin nawa?"

"Jauro mana ko kinada wani bayan shina?"

"Ni wallah Delu kibar had'ani da wannan mugun abu" sai hawaye sharrrr..

Tasowa tayi da sauri tare da rungumeta "yi hankuri abukkiyata nifa da wasa nikai miki, amma ai bana fatan ki kasance matarsa koda maza sun k'are ko."

Sauke numfashi tayi tare da share hawaye "wallahi Delu na tsani Jauro bansan ya nikai dashi ba, amma ita Iya Hari ba Wanda takaso saishi, saukina Ardo har yanzu baice komi ba, ina tsoron kar shima ya yadda."

"Ina Ardo bai tab'a aura miki, Jauro kuma inshaa Allah saikin auri d'an arziki kamar kowa, me ake da J......" Kasa isuwa tayi saboda arba ta tayi dashi yana zuwa, da alama a buge yake sai layi yake ya tunkarosu ga muk'arrabansa bayansa suna take masa.

Jin k'awar tata tayi shiru ne yasa ta d'ago dan ganin meke wakana, arba tayi dashi ya kusa kawowa wurin da suke, d'aure fuska tayi tare da d'auke kai.

Cikin muryan 'yan sha yake magana "ya ke Laure baki ganeni ba halan kiyi fuskar shanu tare da d'auke kai" sannan ya kalli Delu da tasha jinin jikinta "ke munahuka tashi wuce gulmammiya."

Aiko da sauri ta d'auki tirenta ta cika bujenta.

"Haba Jauro wai meyasa kakaimin haka, kaga banson haka, hakad'ai ka korar min abokiyata."

Tunda ta fara magana kallonta kawai yakeyi cike da sha'awa Sam shi bai gane fad'a take ko hira take masa saboda tsananin so.

Wani daga cikin yaransa ne yace "ke oga kika dagama murya saboda ke rammai?"

Tsawa ya daga masa "kai Shago Laure ce fa, kakewa fwad'a?"

Ya fad'a yana zare ido kaman ya maresa, "tuba nike oga."

"Ka kiyaye gaba" koda ya duba har ta bar gurin, murmushi kawai yayi tare da k'arawa gaba.


_so kenan hana ganin laifi_




*Pls friend kuyi hak'uri dani ina fama da matsalan wayatane shiyasa bana typing da yawa.* love u all=??








=؄?Meryerm Abdool=؄?
[7/7, 8:42 PM] =؄?Meryerm Abdool=؄?: =ؤ? ```ABDULMAJEED``` =ؤ?

(' *Servant of Majesty* ('



Na
=؄? _Meryerm Abdool_ =؄?


? *Pure moment of life writers*
P.M.L=ت?


```Where r u? Here is ur page, Momyn sultan, Sakwara, Iya Amima, Sadnap, Sadnas, kanwata jannart, Rukie kax and d rest. ur d best among besties. =ؕ?```






*In dedicated 2 Abdool all over d world* =ؘ?







=??? *Episode* 21--25






Bayan sun dawo da sallar asubah a d'akin kakan nasa ya yada zango, ya iskoshi zaune kan kujera tasbaha a hannunsa yana ja, hannu ya bashi sukayi musabaha tare da yimai barka da asuba sannan ya zauna k'asa dai2 kafarsa yace.

"Ina kwana Alhaji?"

"Lafia lau Abdulmajeed ya gajia?"

"Gajia ta tafi, ya girma ya kuma hak'uri da jama'a?"

"Alhamdullilah, zuwa yaushe zaka tahi yabon?"

"Um zuwa goma nakeso na tafi, shima Hakeem tare zamu fita yaje yayi report a Uduth d'in?"

"Amma anan zai zauna ko?"

"Aa zasu bashi gida to inaga acan zai zauna"

"Ikon Allah tahiya zakuyi gabad'ai?"

"Aa ai Hakeem zai ringa zuwa yana gaida ku, ni kuma zan ringa zuwa end of week inshaa Allah."

"Tau ba damuwa, Allah ya taimaka ya baku nasara a aikinku" sannan ya k'ara da cewa.

"Kaci gaba da hak'uri Abdulmajeed, dama nasan kai mai hak'uri ne, kowane bawa da yadda Allah yake tsara mishi rayuwarsa, idan aka d'auke shi a jarrabawa akayi hak'uri sai kaga ya wuce sai labari, Allah yayi maku Albarka."

"Ameen Alhaji nagode, zan shiga daga ciki nad'an kintsa kafin lokacin yayi."

"Tau yaushe zakaje Argungu can inda kakanninka?"

"Shima idan nayi clearing abubuwa zanje."

"Tau ka shiga ciki kayi sallama da iyayenka da kakarka kaji ko?"

"Inshaa Allah" ya fad'a tare ficewa yana share hawayen da suka zubo masa Wanda ni kaina bansan dalilin zubarsu ba, (tofa kona meye? Mubi a sannu zamu fahimci na meye nan gaba).


Tsaf ya kimtsa shida aminin nasa bayan sunyi sallama da mutan gidan, uduth suka nufa saidai ya tabbatar anyi komai daya kamata ayi sannan ya wuce yabar Hakeem tare cousin nashi su Isma'il, saboda a dalilin sa ya cika garin yaso su samu asibiti d'aya saidai hakan bai samu ba.

Hakeem aminine na kwarai ga Abdool Wanda bayada kamarsa amintarsu ta samo asaline daga secondary har jami'a Wanda har takai ga iyayensu, kullum Hakeem yana lura da akwai wata b'oyayiyar damuwa tattare da Abdool yasha tambayarsa amma kullum amsar d'aya ce ba komai, ya dad'e da sanin halin Abdool na zurfin ciki Sam baya bari damuwa tayi tasiri akansa yana k'ok'arin boyeta, dole shima ya hak'ura yasan in lokacin ya Sani yayi to tabbas zai gayamasa.

Shima dai ya isa garin Yabo kuma ya samu karb'a mai kyau daga mutanen garin amma kam asibitin na buk'atar ma'aikata da kayan aiki, a dalilin haka yayi alkawarin taimaka musu iya k'arfinsa Dana aljihunsa.

_wannan kenan_




^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^



Tana tafe tana tunanin irin k'iyayyar da Iya Hari da Gwaggo Lanti ke nuna mata basu tab'a sonta ba, kullum cikin zaginta suke, k'arshe k'iyayya yakai su zab'a mata jauro a matsayin masoyi.......

"Ramlatuna" ko bata juyo ba tasan duk fad'in duniya bamai kiranta da wannan sunan sai shi kad'ai, juyowa tayi da murmushi akan fuskarka yana zaune bakin gidan yana duba littafi ashmawi Sam bata lura dashi ba ta tafi duniyar tunani.

Dawowa baya tayi tare da duk'awa tace "sannu Baffa, ban kula dakai ba."

Murmushi yai mata "daga ina kike da darenga?"

"Baffa daga Dandali tallen gujjiya."

"Bana hanaki zuwa Dandali da daddare ba?"

Duk'ar da kanta tayi ba tare da tace komai ba.

"Koda yake ba laihinki naba, kiyita hank'uri Ramlah da Hari inada tabbacin wata rana zata gane batai miki adalciba, kuma da yardar Allah inaji a raina sai ke zama abin alfahari a wanga karkara."

Wani k'unshi ya d'auko bayan shi ya mik'a mata "kici wanga nasan da wuya in keci abinci"

Ansa tayi zata shiga ciki tare da cewa "nagode sosai baffa" dakatar da ita yayi tare da nuna tabarma.

"Zauna nan kici" saboda sanin halin Hari idan ta gani ba barinta taci zatayi ba.

Ba musu ta zauna tare da kwance ledar nama ne agashe da zafinsa ci take hannu baka, kallonta Ardo yakeyi cike da tausayi yana mamakin hali irin na Hari, Sam batada zuciyar imani.

Cikin k'ank'anin lokaci ta cinye, ruwa ya bata tasha sannan yace ta shiga ciki, cike ta shiga zuciyarta wasai tana mai jin k'aunar Ardo har cikin ranta.

Shima d'auke kayansa yayi tare da shigewa ciki dama ita yake jira.


*Washe gari*


Kamar yadda ta saba tashinta da ruwan sanyi yauma hakane, dasu ta tasheta tare da binta da zagin k'are dangi kamar yadda ta saba.

Haka ta tashi tayi abinda ya zame mata dole sannan tayi shirin zuwa Yabo.

Zuwa karfe 9 sukaje titi don zuwa Yabo, sun kuwa yi sa'a sun samu mota, tunda suka fara tafia sai murmushi take kallonta Delu tayi "Laure missa meki na farinciki sai murmushi kikai ked'ai."

"Ni kaina bansani ba, nadaiji yau farinciki nikeyi Wanda bansan dalilin inaji a jikina wahalata ta kusa zuwa k'arshe."

"Tau Allah ya tabbatar."

"Ameen abukkiyata."



*A garin Yabo*

Abdool ne zaune kan mota bakin asibiti kasancewar yau ba aiki da yawa patients basuda yawa yaje yayi round shine ya fito waje yana shan iska, yau tunda ya tashi gabansa ke fad'uwa baisam me yasa ba, ya kira Maminsa yaji suna lafia, haka bangarensu Alhaji suma lafia.

Jin bugun zuciyarsa ya tsananta yasa ya rik'e gurin tare da yin Addu'a.

Jin ta sassauta yasa ya d'ago kansa karaf idanunsa suka sauka kan na NATA...........

Lokaci d'aya zuciyarsa ta buga kamar ta fito.....



_wacece wannan_
>??




*Friend kuyi hak'uri da jina shiru da kukayi hakan ya farune a dalilin rashin nepa da mukayi 2days* love ud'







=؄?Meryerm Abdool=؄?
[7/10, 1:32 PM] =؄?Meryerm Abdool=؄?: =ؤ? ```ABDULMAJEED``` =ؤ?

(' *Servant of Majesty* ('



Na
=؄? _Meryerm Abdool_ =؄?


? *Pure moment of life writers*
P.M.L=ت?



*Annabi Muhammad (S.A.W) yana cewa:-*

_baya shiga aljannah wanda mak'wabcinsa bai amincewa ha'incinsa ba._


*'yar uwa koda kafiri kike mak'otaka ya zama dole ki sauke nauyin hakk'in mak'otaka daya rayata akanci, makota abune mai girma saboda fadar manzonmu.*

"Jibrilu ya kasance yana yimin wasiyya da mak'oci har saida na d'auke idan na mutu zai gajeni".


_Allah yasa mu gyara_ =?O?



*Point of correction*

_Abdool service sukeyi ba internship ba, fatar kun gane frnds_.




=??? *Episode* 26--30





Sanye take da kaya irin na Fulani, fuskar nan tasha d'ige-d'ge ga k'waryar nono a kanta, kyakkyawace ba laifi farace ga mai tsayi da jiki, tanada kyawun fuska ba can sosai ba, fuskarta d'auke da murmushi amma zaka fahimci tana tare da damuwa, duk cikin sakan da bai wuce 50 ba Abdool ya karance yarinyar wacce ke tare da k'awarta, amma da alama yarinyace sosai saboda fuskarta ta nuna girman jikine kawai, amma abin tambayar meyasa yake ganin kamar ya Santa?, meyasa k'irjinsa ya harba saboda ganinta?

Ganin baida wad'annan ansoshin kuma gashi zasu wuce yana bukatar nonon yasa ya kirasu.

" 'yan fulani masu nono kuzo in siya".

Laure da saukarsu kenan, jin ance 'yan fulani yasa ta kalli, gurin me kiran nasu, k'irjinta ne ya buga ba shiri ta kalli k'awarta.

"Delu kega me kiranmu ko? Diba kigani kamar ba d'an nanniya ba, duba kalar idonsa abun tsoro, jishi d'an gaye, da kayan lifitoci irin na binni, muje ko kar muje"?

Me Delu zatayi inba dariya ba, saida tayi mai isarta ganin mutuniyar an fuske yasa ta sassauta.

" wlh Laure wani lokacin shirme ke dibarki yoni mi'arruwanmu da shi, nono yace zai saye fah, bayan shi mizaiyi muna? Nidai mutahi kar yace ya hwasa".

Tana gama maganar ta Kama hanya, ganin k'awar tata ta tafi yasa tabi bayanta da sauri.

Abdool kuwa dake kallonsu duk da baiji me suke fad'a yasan akansa ne, ganin suna zuwa yasa shi d'an d'aure fuska.

Suna zuwa yace "ke me kike fad'a mata, wato kikace a kalli idona ko"?

Cikin tsoro ta girgiza kai cikin siririyar murya irin ta Fulani " niya bance komi ba akanka".

K'ara d'aure fuska yayi yace "kinsha ba banji me kika fad'a ai naji komai kikace dan haka gun 'yan sanda zan kaiki"

Wayyo zanso kuga Laure kamar ta saki fitsari kunsan bafillace da tsoron d'an sanda, ba ita kad'ai ba har Delu saida ta tsorata jin an kira 'yan sanda, tuni suka fara da sun sani da basuzo inda yake.

Abdool ganin sunyi tuk'u tuk'u dariya suka bashi amma saiya danne yace.

"Nawa ne nonon"?

"Um...em.. Na nawa kakeso"? Suka had'a baki gurin tambayarsa.

D'an yats??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????ina fuska yayi " nawane duka"?

Kallon juna zukayi sannan Delu tace " jikka talatin"

Maimata kalmar jikka yayi "meye jinka"? Ya tambaya yana kallon Laure.

Tsuru tai masa da ido dan batasan me zatace ba, suna hakane saiga wani nurse d'an garin ya taho gurin.

" Sir dama kanason nono"?

"Sosai nake shansa Jabir".

" Ayya ai bansani sir na d'auka bakasha da kullum na kawo maka shi, ke kutafi abinku zan kawo masa yanzu".

Ai su Laure dama kamar a k'aya suke tuni suka m'ike suna shirin d'ora nononsu.

"Aa bari nasiya tunda na tsaidasu" ya fad'a tare da mika musu 1k.

Delu CE ta ansa tare da zuba mishi "gashi mun gode, sai anjima" a lokaci d'aya ta fad'a tare da Dora nononsu sukabar gurin ba tare dajin ansa ba.

Jabir ne ya anshi nonon, shikam Abdool da kallon kawai ya bisu har suka bar gurin sannan ya kalli Jabir tare da cewa.

"Bari na shiga gida nad'an huta, idan an samu patient u should let me know".

"yes sir".

Gidanda aka bashi na cikin quarters d'in asibiti ya shige, murmushi kawai yake idan ya tuna yarinyar komai nata abin burgewa a fili yace " beautiful and silly girl" can kuma yace "meke shirin faruwa danine ni *Abdulmajeed*"?

"Kai no impossible".

(Tau kai kad'ai ne dai) lol.


Su Laure kam suna barin gurin sunyi nisa tace " Delu yau Allah ya cecemu da wanga d'an binni mai glass yakaimu inda 'yan sanda aida munci bone".

"Wallahi ko zuwan wannan mutumi ta cecemu".

"Hmmm amma kam dan binni nada kuddi har nonon jikka biyar"?

" Aida gani kilama shina kayinsu diba kigani sabuwa dal".

"Amma kam ban komawa ta hanyagga kar atai ya ganmu ya had'amu da 'yan sanda".

"E walla mubi ta waccen hanya".


Haka dai sukayita tattaunawa har suka isa kasuwa........




^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^












Wasa-wasa tunanin yarinyar yayi tasiri a zuciyarsa shi yasa kullum daya gama aiki zai fito ya tsaya waje, amma ko mai kamarta bai tab'a bai gani, mamaki yakeyi meyasa ya damu da yaga yarinyar? Meyasa yake son sanin labarin yarinyar?

Ba Wanda zai ansa mishi amma tabbas zuciyarsa ta matsa mishi daya ganta yaji boyayyiyar damuwarta.......



*A garin kilgori...*


Kamar kullum Ardo tare da Amininsa Malam Garba ne zaune daf da magrib yana jiran Ramlah ta kawomusu ruwan Alwala, numfasashinsa ne yaji yana sassarfa kamar zai d'auke sai k'ok'arin janyosa yake.

Malam Garba da suke fira da Amininsa jin yayi shiru, yasa shi d'agowa ya kalleshi, ganin halin da yake ciki yasa ya tashi da sauri tare da kamashi yace.

" subhanallah Ardo ciwon ne ya tashi" duk ya rikice ana haka saiga Laure ta fito ganin halinda Baffanta ya yake, sakin buta tayi cikin kuka ta isa gareshi tana "wayyo Baffa, meya sameka Baffa" kan jikinsa ta kwanta tana kuka.

Jayeta Malam Garba yayi "ba kuka zakiyi ba Laure, jeki kiro Hari muje asibiti".

Da gudu ta shiga gidan "ke tambad'add'ya minana kika shigoma mutane uwa kamun hauka".

" Iya Baffa ....." Ta kasa magana sai nuna mata k'ofar gidan take.

Ganin taki magana taja tsaki "ko minana babu ruwana can ta matsemuku ke dashi" ta bud'e baki zatayi magana.

"B'acemin da gani sauna" ta fad'a cikin tsawar da ya firgitata a guje ta fita, koda ta fita har Malam Garba ya kira mashin ana shirin d'ora Ardo.

"Ina Harin"?

" tana zuwa" kawai ta fad'a D'ora shi yayi shima ya hau tare da cewa su samesu a can.

Aiko suna wucewa ta bisu da gudu tana kuka, d'an clinic ne garesu a garin, ba kuma likita sai nurse kawai, ganin yanayinsa yasa sukace a wuce dashi Yabo kawai.


Koda ta iso har an samo mota, an sakashi, ai bata jira jin komai ba ta fad'a ciki driver yaja........




_manage pls friends_ =?O?






=؄? Meryerm Abdool =؄?
[7/11, 4:04 PM] =؄?Meryerm Abdool=؄?: =ؤ? ```ABDULMAJEED``` =ؤ?

(' *Servant of Majesty* ('



Na
=؄? _Meryerm Abdool_ =؄?


? *Pure moment of life writers*
P.M.L=ت?



```WASIYYAR LUKMATUL HAKEEM GA D'ANSA ITACE :-```

*Ya kai d'ana kada kayi shirka ga Allah(kada ka had'ashi da wani a gurin bauta) domin shirka itace mafi munin zalunci, ka zamo mai biyayya ga iyaye, domin neman dacewa duniya da lahira.*

*Yakai d'ana ka tsaida sallah, kayi hak'uri da abinda ya sameka, kada ka nemi biyan buk'atarka ga mutane, kada kayi tafiya a cikin k'asa kana mai alfari da tak'ama, domin ubangiji bayason mutane masu alfari da tak'ama.*

*ka zamo mai tafiya cikin nutsuwa, kada ka zamo mai d'aga sautinka a gurin magana domin mafi munin sauti shine sautin jaki.*( _suratul Lukman_)

_Allah sarki, mutum mai mutum mai hikima kenan, ni dah keh dasu wance mun tab'a tunanin yima 'ya'yanmu wasiyya, tofa musani 'ya'ya amanace kuma abin tambayawa ne gaban ubangiji ranar gobe k'iyama._

Allah yasa mudace=?O?





=??? *Episode* 31--36





Suna isa aka k'arbesu I&E aka wuce dashi, haka Laure da Malam Garba suka bi gadon da aka d'orasa, sai hawaye kebin fuskarta ganin yadda numfashin Ardo ke zuwa yana dawowa gani take rasashi zasuyi, idan Ardo ya tafi ya barta shikenan batada sauran gata (Allah ne gatanki Laure).

Suna isa bakin k'ofa aka dakatar da su daga waje, anan reception suka zauna kan bench, sai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login