Showing 33001 words to 36000 words out of 88300 words

Chapter 12 - ABDULMAJEED BOOK by Meryam Abdul.doc

09 Oct 2025

1591

garin gwamna...


_safe trip_ =ؗ?



~~~~~~~~~~~~


Lokacin da labarin Auren Abdulrahim ya bazu a k'auye Kilgore mutane sai tururuwa sukeyi gidan dan ganin amarya da 'yan gulma da 'yan ganin kwam, da masu yabawa da masu tsinewa, su Lanti anzo sai yatsine take dan Uwar ta kitsa mata tana yad'a bak'ak'en maganganu, Abdulrahim ko dayaji tass yayi Mata sannan yace karta k'ara zuwa gidan muddin ba abin kirki zai kawo ba, aiko iya Hari ina wuta in fad'a inda take shiga banan take fita ba, cin mutunci gaske tayi masa, wai karya kuskura ya takurawa 'yarta akan wannan korarriyar wanda iyayenta suka sallama, cin fuska dai sai Wanda ta manta, ranar Asma'u tasha kuka tare da kewar gidansu lallai kowa yabar gida ya barshi, gata ana mata gori ba yadda zatayi, hakan ya k'ara ba Lanti kwarin gwiwar yi Mata iskanci son ranta, saidai batayi in Abdulrahim nanan dan tana shakkarsa, Saude kam haukane kawai batayi ba, da taji Auren Abdulrahim haka tazo har gida tayima iya Hari rashin kunya, wai ai ita tayi mata alk'awari amma tsabar munafurci ta bari ya auri wata ba ita ba, itako Sam bataga laifinta ba saima hak'uri ta bata akan lallai zai aureta ta shigo ta biyo, tace Allah ya kiyaye ta zama ta biyu ta d'auki sauran wata, ta yafe, dama ba sonsa take ba sha'awa ce kawai.

Kamar yadda Ard'o yace haka kuwa akayi an Gina mata ciki da falo hadda bayan gida. Lol

Shanu biyu Ard'o ya Ware yayi Mata kayan d'aki a matsayin sa na uba gareta, an gyara d'aki ba laifi, nan kuma wani gorin ya tashi habaici kam tasha harta gode Allah, zuwa yanzu ta fara sabawa da cin mutuncin Iya Hari da Lanti, amma kullum abin na kona ranta bata dai yadda zatayi ne, ga uban aiki gidan da yanzu ya dawo Kanta, komai ita danma Shatu na kamata inba idon Iya Hari, dan tuni tayi Mata iyaka da Asma'u, in kaga Asma'u saika tausaya mata duk tayi baki ta rame danma ta Saba da aiki a gida da sai tafi wahala, Abdulrahim baida halin magana a balbaleshi da bala'i itama Asma'u tace ya dena magana kada ya had'u da fushin mahaifiyarsa tunda ita ta haifeshi ya zama wajibi yayi mata biyayya, Ard'o ma yayi fad'a harya gajia amma a banza da maganan sa da babu duk d'aya suka ha Hari, saidai in ya samu tanayi yace ta aje inya fita ace tazo tayi dan ubanta (oh Asma'u kina ganin rayuwa).


Sauk'inta Mijinta na tausasa mata da nuna mata k'auna, inta zauna sai taita tunani "wato mu haka tamu k'addarar take an jarabcemu da uwar miji, haka aunty Ameena tayi fama, ashe nata nafila ne, gwanda ita ina kusa kuma zata kira gida taji dad'i to nifa ba ko d'aya, yanzu ko sakina akayi INA zan nufa, ya Allah ka sassauto da zuciyar Baba yafemin ya mai domin da family i'm in need of them badly".

Ana hakane akayi posting nasu gurin service ita da Abdulrahim, ba state d'aya aka ajesu ba shi Katsina ita kuma Edo, hakan yasa yaje ya nemi alfarma aka maida ita Katsina, nan ma anyi rigima da Iya Hari wai ba inda zataje, k'aryane meyakai mace bautar k'asa, nan ma saida Ard'o yayi da gaske sannan ta Shafa musu lafia, zaman su Katsina zamane mai dimbin tarihi a cikin rayuwar Auren su dan sai a sannan ne suka samu nutsuwa, dama Dr gida ake bashi, so basuda matsala haka suka gudanar da service d'insu cikin kwanciyar hankali, ko marmarin dawowa basuyi,ranar da suka isa Abdulrahim ya sayomata waya nan ta kira numbobin gidansu amma ba wacce ke nan jikinta ya k'ara sanyi da d'auka kodan karta kirane yasa Baba sasu canja layuka(ba haka bane baraye suka kwase musu wayoyi dare d'aya) lokacin da suka gama zasu dawo kamar karsu dawo sukeji, haka sukayo tsaraba sosai suka dawo amma kam Asma'u ranta fal tsoro za'a koma 'yar gidan jiya.

Hakan ko takasance bayan dawowar su akaci gaba daga inda aka tsaya wannan karon hadda gorin rashin haihuwa ganin suna cikin shekara ta uku da Aure ba haihuwa, Abu dai kullum ba sauk'i sai abinda yayi gaba, gashi anyi Auren Shatu mai tausaya mata.

Cikin ikon Allah Abdulrahim ya samu aiki a uduth Sokoto hakan yasa Ard'o yace ya d'auki matarsa su koma can da zama, Iya Hari cewa tayi bak'in ciki ake mata tunda tana taya ta aiki, banza yayi da ita danya San Neman a tanka ne.

Haka suka tattara suka koma Sokoto, kuma Ard'o yayi Iya kashedin duk ta taka Sokoto bakin Aurenta, dole ta lahe dan tasan rabuwa da Ard'o babbar asarace gareta.

Suna shekara cikin ta 5 da Aure Asma'u ta samo ciki, fad'ar irin farinciki da sukayi ba'a ma magana, haka sukaci gaba da kula da cikinsu cikin so da k'auna har ya isa haihuwa inda Abdulrahim da Kansa ya anshi haihuwar zankad'ed'iyar 'yarsa me kama dashi, baki kamar gonar auduga, su Modibbo anyi 'ya, Ard'o yaje yazo dasu da sunan ayi mata wankan jego tunda haihuwar fari CE batasan makari ba, Amma abin takaici ko kallo basu ishi Iya Hari ba, anyi ba'ayi ba dai kenan dan komai Asma'u ce kema Kanta, da bata iya ba saidai ta rub'e anan, tayi kukan rashin 'yan uwanta harta gode Allah, lallai naka sai naka, da sunanan da bata wulak'anta ba, Abdulrahim ne ke kama Mata aiki sai kuwa Shatu idan tazo shima idon uwarta kamar ya tsiyaye gurin harara, Abdulrahim ko saidai tace shanyayye Mara tayi.

Haka sati ya zagayo ranar suna yarinya taci suna *Ramlah* rago biyu da sa aka yanka, Abdulrahim yayi k'ok'ari dan yayi musu komai na goyo tsadaddi Hari ko sai yad'a magana anyi Aure ba dangi haka suna ma, Abu sai kace mayya, ita Kanta Asma'u abun na matuk'ar damunta, dan Abdulrahim yasha cewa ta bari suje Argungu suba Baba hak'uri, sanin halin mahaifinta na kaifi yasa tace cewa Aa su jira dai(tab aiya canja duniya ta horashi) lol.

Tun kan suyi arba'in ganin wahala tayi ma Asma'u yawa, balle Abdulrahim ya kawo sai k'arshen sati yake zuwa yasa, ga dawainiyar kula da kai da jaririya gana gida yasa Ard'o yace ya d'auketa su wuce kawai, duk k'arshen sati Abdulrahim na zuwa duba iyayensa, idan Asma'u bata zo ya zama abun zagi idan taho ma aci Mata mutunci.

Abdulrahim arziki sai bud'ewa yake tana ganin haske saboda biyayyar iyaye da yake, ga kulawa da iyalinsa da yakeyi, har Saudiya ya biyama Ard'o da Iya Hari, amma Iya cewa tayi ya bata kud'in kawai (hasararriya Mara rabo) Ard'o kam ya k'ara tsorata da lamarin Hari, haka ta kashe su a banza.


~~~~~~~~~~


B'angaren Ameena da Yusuf kuma zaman su lafia lau gwanin sha'awa, kowa na kaffa,-kaffa da d'an uwansa, tare suka kowa makaranta inda take karantar Botany (ilimin tsirrai) sam rashin haihuwar bai tab'a dagama Yusuf hankali ba, shine ma mai kwantar Mata da hankali, idan tana nuna damuwarta, yace "haihuwa ta Allah ce idan sunada rabo zasu samu idan babu Abdool ya ishesu".

Suna shekara 4 da aure ta samu ciki, murna sosai sukayi da kyautar da Allah yayi musu, wata tara cip ta sunbulo 'yarta mai kama da Yusuf sak, a Besse suka koma akayi suna inda yarinya taci sunan mamar Yusuf Aisha suna kiranta Nihal, mutane Argungu anzo an kwashi shoki!

Musamman Abdool daya zama dan samari sai murna yaks yayi k'anwa.........




*lol every body a kame kam sabuwar rawa =?t?



_kuyi hak'uri Dani friends abubuwan ne da yawa #one love# =?
?_






=؄?Meryerm Abdool=؄?


=?L? [8/16, 8:27 PM] =؄?Meryerm Abdool=؄?: =ؤ? ```ABDULMAJEED``` =ؤ?

(' *Servant of Majesty* ('



Na
=؄? _Meryerm Abdool_ =؄?


? *Pure moment of life writers*
P.M.L=ت?
(We don't just entertain and educate we touch the heartd' of the readers=???)



```Manzon Allah (S.A.W) yace ma wani yaro:- kayi bismillah(idan zakaci abinci) kaci da hanun damanka, kaci daga abinda ke gabanka.```

_Ladubba ne nacin abinci mu kiyaye sannan mu koyar da yaranmu_ Allah yasa mudace=?O?


*Ina mai farinciki da wannan Auren da kikayi Aunty Kausar (kausar M Hasan) Allah ya sanyawa aurenki Albarka tare da zuria dayyiba Ameen #HML=؏?*


_Ina mik'a ta'aziyya ga Feedo Deedo (marubuciyar mamata gimbiyata) akan rashin mahaifiyarta da tayi, Allah yayi mata rahama yasa mutuwa hutuce ameen, Ku kuma Allah ya Baku hak'urin rashin da kukayi=?O?





=??? *Episode* 131-135






Bayan sunyi Arba'in sukaje Argungu ganin gida da kai musu jaririyar su gani, lokacin da Ameena ta shiga d'akin su, nan taga wasu kayan Asma'u wad'anda ba'a kyautar ba, batasan lokacin da hawaye ya wanke mata fuska cikin jimami take magana "Asma'u kina ina? Tsawon shekara biyar kenan, Asma'u kina lafia kuwa? Kina cikin farinciki ko sab'anin haka, Asma'u kizo gida mu ganki wlh Baba Neman ki yake ruwa a jallo, pls Husnatah sisto na friend dita ever kizo garemu muma buk'atar ki" cikin kuka tace maganar gwanin tausayi, kullum safiyar duniya kira gida maganarta kenan Asma'u tazo, Mama dake tsaye bakin k'ofa rik'e da Nihal dake motsi alaman yunwa dan tunda suka zo take sharar bacci abinta, Abdool na kusa da ita sai kallon ta yake ya tab'a nan ya tab'a can yana matuk'ar son k'anwar tasa, ko yanzun ma Baba ne ya kirashi suka fita.

Itama hawaye take daga nan tsaye, ita ta haifesu gaba d'aya, amma tasan akwai shakuwa mai girma a tsakaninsu sau da yawa idan matsala ta taso a tsakaninsu suke maganceta ba tare da ta sani, saidai idan tafi k'arfin su suka kawo mata, to ya zasuyi k'addara ta riga fata, saidai su bita Addu'a Allah ya k'are ta aduk inda take ya dawo musu da ita lafia, share hawaye tayi kada ta rauna nata.

K'arasawa tayi ciki tare da kamata zuwa bakin gado, cikin muryan rarrashi da tace "Ameena kuka bazai dawo da Asma'u ba, Addu'ar mu kawai take nema, kiyi hak'uri ki daure ki daina kuka kiyi mata Addu'a" haka tayi ta rarrashinta daga k'arshe ta bata 'yarta data fara kuka tare da ficewa cikin sanyi, dan ganin Ameenan kad'ai tuna mata da Asma'unta yake yi.


*****************



Satinsu d'aya a Argungu sun zaga dangi sosai har birnin lafia sunje, gidan Firdausi duk taje, Abdool kuwa kullum yana rik'e da Nihal har goyata yakeyi Mama tayita zolayarsa, da sunan mati sai cewa yake ai k'anwarsa CE, a satin Yusuf yazo nan ya dage da rokon Baba ya basu Abdool su wuce dashi tunda ya k'are primary, ganin sun dage kuma yaga shima yaron yana buk'atar uwarsa a kusa dashi duk da suma ba abinda basa yi masa amma d'a sai uwarsa, kuma ya yaba yadda Yusuf d'in ya nuna kulawarsa akansa, yanada tabbacin zai rik'e sa da Amana, amma duk da haka saida ya kira Alhaji Sada ya shaida masa abin da sukazo dashi.

Kai tsaye Alhaji ya amince dan yasan waye Ameena yasan zata bashi tarbiyar da ya dace, shi kanshi yaron zaifi jin dad'i gashi ga uwarsa, nan Baba ya basu Abdool sunyi murna Sosai bakin Yusuf ya kasa rufuwa danshi harga Allah yana son Abdool yana jinshi a ranshi kamar yadda yakejin Nihal.

Ban kwana sukayi ma Argungu garin nabame kowa sarki, sannan suka wuce Besse anan ma sam dangin Yusuf basu nunawa Abdool wata fuska k'ama ko wulak'anci ba, Wanda hakan yayima Ameena dad'i sosai, daganan suka shirya tsaf suka lula Kaduna.....

Zamansu kaduna zamane mai cike da k'auna da kulawa da yaran su sosai Yusuf ke kula da Abdool kaman ma yafi sonsa akan Nihal, dan Ameena cewa take Nihal ce babynta shi kuma yaron Dady, tare suka zuwa masjeed kullum muddin yana gida, haka zai baje a parlour yana mishi lesson don tuni suka sakashi secondary wata private, muddin Yusuf na gida to yana tare da Abdool hakan ba k'aramin dad'i yakewa Ameena ba, hakan ya k'ara wanzar da zaman lafia a familyn.

Sannu a hankali rayuwa taci gaba da shurawa kwanaki na tafiya, Nihal nada four years Ameena ta k'ara haihuwa wannan karon twins ta haifa mace da namiji, nan Ameena ta roki Akan a sakama macen sunan Asma'u hakan kuwa akayi inda ake kiranta da Husna namijin kuwa Abduljabbar, zuwa yanzu Yusuf ya gina musu gidan Kansu a unguwar K/mashi inda Ameena ta k'awata gidan da kalolin furanni masu dad'in k'amshi ga kuma garden had'adde Wanda ya k'unshi kayan more rayuwa, kai da ka taho gidan ba tambaya kasan ka taho gidan miss Botany tun farfajiyar gidan zaka fahimci haka.

Abdool yana SS1 Nihal na nursery, tuni ya saba da saka medical d'insa inda a school d'insu wasu ke ganin jin kai ne da tsabar raini dan yaga yanada Brain yasa yake saka glass dan sauka haka kawai yake sakawa ganin yadda ya zauna mishi tsaf, Abdool ya taso yaro mai kuzari da sanin ciwon kai ga k'auna da yake nunawa kanninsa haka sai saka Nihal gaba yayi mata lesson in Dadynsu bayanan shi kuma inya dawo yayi mishi, shi har mamakin k'ok'arin Abdool yake yaro sai kace dan Jamia komai kana ana bud'e kwakwalwarsa ana zuba masa, ita ma dai Nihal Kanta naja ba laifi sai yake danganta hakan da ilimin Ameena, haka sukaci gaba da gudanar da Rayuwarsu cikin farinciki, sukanje Hutu lokaci zuwa lokaci haka Alhaji Sada na zuwa har Kaduna ya dubasu, yanajin dad'in yadda suke kula da Abdool, tuni Alhaji ya saba da Yusuf haka zasu zauna suyi ta hira in yazo dama ga Yusuf da barkwanci wuni guda kukayi a tare zaku Saba.




*****************




Ranar rabuwa ranar da zukata suka nisanta da juna ranar ruhi da gangar jiki suka shiga maraici ranar da mai rabawa ta raba, ranar da Yusuf yayi accident a hanyarsa ta dawowa Kaduna ya fito daga Besse anan on d sport wuyansa ya kare nan take ya ansa kiran maliccinsa, sai gawa su Ameena suka gani fad'in kalan tashin hankalinda suka shiga anan dan page d'in ga bazai ishemu ba, kowacce ta kwatanta da mijinta ne da babanta ne da d'anta ne da k'annin ta ko yayanta ne ya zataji haka suma Familyn Yusuf sukaji da rashin da ya sameso, a Besse aka wuce da gawar akan kayi komai daya dace da shari'ar sunnar Manzo S.A.W, ba'ayi wani zaman makoki ba, duba da yadda zaman ya koma zaman hira da tsegumi da cin shinkafa, Wanda ya mutu shiya mutu kawai sai kuwa na kusa dashi, da suke cikin jimami rashin sa, duk wannan abun Abdool baida labari dan lokacin yana ABU zariya inda yake matriculation, Wanda Yusuf ne da kanshi ya kaishi ya kuma zaba mishi medicine, ganin yanata kiran Dadyn nashi wayanshi bata zuwa yasa ya kira Maminsa, nan ta sheda mishi suna Besse ba charge a wayansa, sannan tace idan da chance ya samesu Bessen k'arshen sati, nan ya tambayeta lafia dai tace qlau ba komai, amma jikin na bashi ba lafia.

Lokacin da yazo ya samu abinda ya faru, yayi kukan rashin Dady dan sosai ya maye masa gurbin Auwal yanzu gashi ya tafi ya barsu.

(Duniya labari)


Anan ta zauna harta kammala takabanta, akayi rabon gado kamar addini ya tanadar daga an kammala hada komai, tayi sa'a gidansu na Kaduna ya shigo cikin rabonsu hakan yasa tace zata koma Kaduna, sun so tayi zaman ta nan tare dasu dan Ameena mutum ce wacce kowa ke sha'awar zama da ita, saboda iya zamanta da mutane da kyautata,tafi so koda zata cutu ne wani yaji dad'i amma batason wani ya cutu akanta, hak'uri ta basu saboda ta riga ta saba da Kaduna ga kuma karantun yara (weather ma akwai banbanci sosai tsakanin Kebbi da Kaduna) haka taje Argungu tayi musu sallama nasiha sosai Baba da Inna sukayi mata duk da susan Ameena zata tsare mutuncinta aduk inda ta riski Kanta, sannan ta wuce da Mansur d'an yad'an rage mata kewa, da yake Abdool ya koma Zariya saboda karatu, shima Mansur ya kammala NCE inda zaiyi degree a can.

Bayan komarsu ta shiga neman aiki tuk'uru, shine amfanin ayi karatun koba mutuwa akwai sayin yanayi Wanda miji zai nemi agajin matarsa musamman ma inga nauyin iyali, cikin sa'a ta samu aiki ministry of Agriculture inda zata ringa basu shawarwari akan dashen itatuwa da fulawowi da dai duk wani dangin tsirrai, haka kuma gefe d'aya ta bod'e nata gidan koma inda ita kula da abinda sai Mansur da wasu matasa data d'auka take biyansu, in fact dai ita keda mallakinsa nata ne, ga business tana yi da tana bada odar kaya daga Dubai, Alhamdulillah, tafi k'arfin buk'atunta dana yaranta, yayin su kuma ta saya musu shares da gadon su ana jujjuyawa a Ja'iz bank inda suka halattacen kasuwanci da kud'in.

Wata rana in ta zaune sai tayi ta tuna maganganun Yusuf da yake cewa "Ameena ko a yanzu nabar duniya bana shayin Wanda zai kulamin da yara na da tarbiyar su, saboda nasan zaki iya ke namijin duniya ce, wacce kowane namiji ya sameki zaiyi alfahari da ita, ina k'aunarki Ameena har numfashi na, na k'arshe" ita kuma idan yana fad'ar haka saita rufe masa baki tace.

"Ba zaka mutu ba mijina kai kad'ai inshaa Allah saidai mutuwa ta doke mu tare bana fatan ka barni a duniya ni kad'ai, pls ka dena fad'ar haka" murmushi kawai yakeyi ya canja zance, gashi yanzu tana tunawa shikenan ya tafi ya barta, nema masa gafarar ubangiji take dan shine kadai ya rage a tsakaninsu yanzu, ga zawarawa sunyo mata caa abokan Yusuf da abokan aikinta itakam hak'uri kawai take basu, yanzu kam renon marayun yaranta ne a gabanta bata sake jajibo wani Auren ba, ko iyayenta da sukaji sun goyi bayanta dan yanzu tasan meye mai amfaninta da Wanda baya amfaninta...

Ciwo ne ya tasowa Alhaji Sada da gaske har anyi admitting nashi hospital, hakan yasa Abdool zuwa kiran Maminsa akan zaije ya dubasa, sosai ta tausaya masa itama taso taje ta dubasa dan Alhaji kamar ubane gunta ga kirki, har Besse yaje mata gaisuwar Yusuf, amma kuma tana tsoron yadda familyn zasu karb'eta, tsoron abinda zaije ya dawo yasa ta fasa zuwa tace Abdool ya gaishesa sosai.

Alhaji yayi murna sosai da zuwan Abdool Wanda shine na farko tun bayan rabuwar iyayensa haka 'yan uwa da iyayensa maza ga su Isma'il sa'anninsa ga kuma k'anninsu gida ya cika sosai sa zuria, Hajia tunda ta ansa gaisuwarsa a

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login