Showing 51001 words to 54000 words out of 88300 words

Chapter 18 - ABDULMAJEED BOOK by Meryam Abdul.doc

09 Oct 2025

1610

da gayamata sunanta kamar yadda ta gayama Nihal tana murmushi.

Itama murmushi tayi mata "Ramlah Abdulrahim modibbo by name".

"wow i like ur style, may I have a seat here?"

Kallon Nihal Ramlah tayi sannan tace "why not" ta fad'a tare da nuna mata seat...

Tun daga ranar suka zama k'awaye irin sosai d'innan akayi sa'a kuma itama House d'insu aka ajeta room d'insu d'aya, nan suka koma su uku komai tare sukeyi.

Sadee irin marasa jin nannan irin bata yadda d'innan ba, classy girl ce ta sosai ga rawar kai kaman me, saidai fa itama akwai kai shiyasa zamansu yayi kyau, a class kuwa ji yake dasu suke d'aukar 1,2,3 position, zamansu da sadee sun k'ara wayewa idonsu ya bud'e sosai musamman Ramlah.

Sun koyi saka k'ananun kaya a gurin ta, haka tazo dasu trolley guda haka ta shiga basu tana koya masu yadda zasu saka, nan fa suka shiga nuna Kala ko'ina suka wuce 3stars kakeji, har Senior burgewa sukeyi.

Har Mami tasan Sadee haka iyayenta har sun kulla zumunci suma, su Abdool ma daga India suna shan labarinta.

Yanzu su Ramlah anyi mastering gurin swag haka idan suka dawo Hutu a gida ma sun daina saka atampha ko less English wears kawai, mini skirt, top, tight, pencil, body hug, bomber short iri-irensu dai.

Haka idan zasu koma Hutu zasu shiga boutique su sissiya tare da M bash suke zuwa dake itama anan Kd take, Mami dai ta zuba musu ido ganin iya gidane kawai basa fita dasu.

B'angaren su Abdool kuwa tunda suka tafi basu zo ba, dan ba damar d'agawa nan da can amma har cikin ransa yana missing gida yana missing Ramlah sosai, abun haushin ma an k'ara musu rabin shekara abun ya bata masa rai saidai ba yadda ya iya dole ya jure.

Su Ramlah an zama sun zama cikakun 'yan mata sosai musamman ita dama gata kamar kajin Agric, komai na cikar mace ya cika gareta, 8 shape d'in nan ya fito sosai, dukiyarsu ta Fulani ma sun cika barakallah, duk namiji lafiyayye ya kalleta sai yaji wani Abu a ransa........




_to friends ya kamata fa mu waiwayi Iya Hari, muji wace wainar suke toyawa =??>?#?_







=؄?Meryerm Abdool=؄?
[9/10, 4:14 PM] =؄?Meryerm Abdool=؄?: =ؤ? ```ABDULMAJEED``` =ؤ?

(' *Servant of Majesty* ('



Na
=؄? _Meryerm Abdool_ =؄?


? *Pure moment of life writers*
P.M.L=ت?
(We don't just entertain and educate we touch the heartd' of the readers=???)







```Allah mad'aukakin sarki tsarkakakke ne kuma baya karb'a sai Abu tsarkakakke=?L?
Muyi k'ok'ari mu tsarkake tsakaninmu dashi.=?L?


*Namecy ur a d most grateful ever meet ur d best namecy, ur ur ur hmmm am speechless dear, may Allah bless be wit u always namecy _Maryam Y Zango_ here is ur page.=؋?=؋?=؋?*







=??? *Episode* 181--185




Iya Hari tun ranar da aka d'aura ma Ramlah Aure aka kuma ga 'yan uwanta tasan lallai Ramlah tayi mata nisa, kuma tayi mata fintinkau saidai tsinka, musamman ganin irin dukiyarda ke garesu, amma saboda bak'ar zuciya irin tata da sharrin shed'an(Allah yayi mana tsari da kaidinsa) suka had'u suka yi mata b'akar hud'uba na yadda zatayi ta maida Ramlah baya taya zata maida ita k'auye taci gaba da musguna mata.

Duk masifa da bala'in Hari da d'ibar albarka irin tata bata zuwa gurin boka ko malamin tsibbu saidai tayi addabeka ka gwammace inama baka Santa ba a rayuwa, amma a yanzu ta fara tunanin zuwa inda boka domin ya lalata auren Ramlah sannan ya saka mata bak'in jini a idon dangin mahaifiyar tata su korota inda take daga nan taci gaba da musguna mata bayan tasa an rufe bakin Ard'o, wannan kullum shine tunanin amma ina zata samu kudin zuwa shine matsalar dan kudi sam baya zama ga Hari saboda shegen kwalama da kwad'ayin tsiya, ga Ard'o yanzu zama k'ankamo injita, dama can halinsa ne (Inji fa).

Tunda aka wuce da Ramlah Ard'o bai k'ara maganarta a gidan ba, ko tanaso ta tambaya ba dama duk zuwanda yake Kaduna da zuwan da Abdool keyi gurinsa bai taba gayamata, saidai taga kayan tsaraba kawai ko tambaya tayi ina, cewa kawai yake ba damuwarta bace.

Ganin zaman kad'aici ya isheta ita kad'ai a gida yasa ta d'auko Hinde d'iyar Lanti dan tayata zama da taimaka mata, amma kuma sai hakan bata samu dan Hinde gantalliyar yarinya ce, b'atacciya kuma 'yar iska irin ta k'auye nan.lol

Inta kwanta bacci sai hantsi ya dubi ludayi take tashi, ko tsince bata kawar mata hasalima ko Inda ta kwanta bata gyarawa da kuma ta samu abin kari ta fita bata gidan biki bata na suna bata dakin saurayi bata matattarar 'yan iska ba ita zata dawo ba sai bayan isha, shima tana zuwa taci abinta sai dandali daga ta dawo sai bacci, aikin sisi bata mata kuma datayi mata kallon banza ko fad'a rashin kunya take mata inta zageta ta rama, inta doketa kota hanata abinci taje ta gayama uwarta, haka Lanti ke kwaso jiki wai akan me zata dokar mata 'ya kota hanata abinci ko tana nufin yadda tayi Laure ne zatayi ma 'yarta, wallah bata yadda ba dan ba jaka ta haifar mata ba, haka zata tasata gaba da masifa akan 'yarta kuma ba halin kwab'arta dan tarbiyarta ai(kaikayi koma kan mashekiya) wani sa'in Ard'o na jinsu bai cewa k'ala, saidai yayi murmushi kawai yasan farawane ma indai alhaki ne.

Haka Hinde ta zamewa Hari wani bala'i kadangaren bakin tulu a kar ka akai tulu a barka ka bata ruwa, gefe d'aya kuma Jauro ruwa a jallo yake Neman Hari, dan Ard'o ya masa kashedi da gidansa shiyasa bai sameta a can ba, amma yasa alwashin idonsa idonta ba'a mai kyau.

( _Sorry Iya Hari, farawa ne ma_ )..=??=??



******************





Komai aka masa rana tau za'a cimmata a yaune Dr Abdulmajid tare da Zainab suka diro Nigeria cike da nasarori ciki hadda tsulelen cikinsu d'an 8months, sunyi fresh abinsu musamman Dr Majeed idan ka kallesa saika k'ara kaman wani saurayi d'an 20 ya hade cikin suit ash, yasha cover ga glass as usual ya zauna daram, sumar sai sheki take, man pride nasa yasha gyara, Zainab kuwa cikin Arabian gown ja tayi rolling da gyalenta ga cikinta daya fito tutsu dashi, tad'anyi jiki irin na cikin nan.

Sale driver ne yazo d'aukar su, direct gidan Mami suka wuce wacce ta shirya musu better tana jiran isowarsu, tayi murna da ganin su musamman ganin Zainab da ciki cikin ranta fad'a tace "Ashe gwanda da akayi auren nan gashi har rabo ya samu zanga jikana" sai nan da nan take da Zainab ina zan saka ina zan d'auke, itakam sai sunne kai take alaman kunya, Abdool kam sai murmushi yake gaskiya no place like home.

Yanzu babban burinsa ganin Ramlah yasan ta k'ara girma yanzu, anyi sa'a kuwa end of week ne visiting, surprise yakeso ya musu....

Ranar visiting su Ramlah ne zaune kan bench su 3 sai fira suke sama-sama, lokaci zuwa lokaci zata kalli gate, duk da tarasa dalilin hakan, sai smiling take tana felling special.

Can ta hango su Husna d'auke da basket, zame jiki tayi sallat ba tare dasu Nihal sun sani ba sunyi nisa da hiran Uncle lukman wani Cooper da aka kawo musu dake bala'in son Ramlah, itakam Sam bata bashi fuska ba, dan tasan ba kyau ko a musulunci and then yanzu tasan ma'anar so kuma mutum d'aya takewa so shi kad'ai yayanta mijinta, shine fa Sadee ta d'age wai tasoshi ya had'u...

"Husna, Abj ina Mamin ne" ta fad'a tana isowa gunsu, ita Sam bata kula dasu Dr Majeed ba, inama zatayi tunanin ganinsu tunda tasan basa k'asar kuma ko jia sunyi waya.

Rungume hannayensa a k'irji yayi, tabbas girman d'an mutum ba wahala, ta canja gaba d'aya, badan yayi mata Sanin kwarai ba ai kila bazai ganeta ba.

"Aa ya ina magana kunmin shiru kodai Ku kad'ai ne?" Smiling Husna tayi tare da nuna mata inda su Abdool suke.

Idonta ne ya sauka kan na Abdool dake mata murmushi, cikin ihu ta daka tsalle "Lah Yaya what bunch of surprise" ta fad'a tare da fad'awa jikinsa, wani shock ne ya ziyarcesa tun daga yatsar kafa zuwa brain d'in sa.

Wani bak'on lamari wanda bai saba ji game da Ramlah shine ya ziyarcesa a yau, duk kuwa ba yau ne lokaci na farko da ta saba rungumesa ba, cikin wayau ya zameta daga jikinsa, Zainab na ankare da halin da ya shiga saurin d'auke kanta tayi zuciyarta sai harbawa take, ba abinda take ambato sai "innalillahi wa'inna ilairajiun" sannan ta samu nutsuwa, murmushi ta k'irk'iro "wato Aunty Ramlah Dr kawai kika gani".

" laa Aunty Zee ba haka bane ai kune kunyi min bazata Allah " ta fad'a tana isa gunta, rungume juna sukayi suna dariya.

"Um um" Abdool yace, inda yake suka kalla, tuni Zainab ta gane yaren wato ayi masa a hankali da baby, hararan wasa ta jefa masa, Ramlah tace "wani abun ne yaya?"

"Um ba komai Ramlatun Yaya, ina su Nihal ne?" Ka gansu can, basu ma San nazo ba" nuna musu gun bench d'in tayi, can suka nufa a tare sai tambayan su take game da India (kunsan dai Ramlatun baffa da tambaya).

"Kinaji ko besty ni banga illar uncle Luku ba kawai ki amince masa" Sadee ta fad'a saidai me ba Ramlah da takema magana a gun.

Baza ido sukai suna nemanta can ta hangota tafe tare da wasu da bata sani ba sai su Husna "la haula Yaya Abdool ne da Aunty Zee yaushe suka dawo bamu sani ba" Nihal ta mik'e tana fad'a.

"Nihal wai wannan shine ya Abdool d'in?"
"Eh wlh shine kinga matarsa Aunty Zainab"

"Kai Amma wlh ya had'u ba k'arya gashi Dr, wow gaskiya I love him"

Zaro ido Nihal tayi "me? Rufamin asiri kafa matarsa can" to meye ba sai naje ata biyu ba"

"To ai.." Shiru tayi.

"To ai me?"

"Uhmm share kawai Sadee" zata yi wata magana suka k'ara so hakan ya tilasta yin shiru.

Anan suka shimfid'a darduma, lunch sukayi as usual bayan an gaisa sun gabatar musu da Sadee, firan Yaushe rabo suka shigayi da Aunty Zainab ta yaushe rabo, jefi-jefi Abdool ke saka bakinsa, duk hankalinsa ya tattara ya tafi ga Ramlah sai kallon ta yake in style, mamakin girmata kawai yake, Zainab na ankare dashi, dama tasan za'a rina tun tana kwaila ya kalla balle kuma yanzu data cika fam, Sadee ma ta kula da kallon ta dai share ne kawai.....


**************

Sokoto sukaje suka kai musu tsarabansu, har gidan Alhaji Sada sunje, momyn zee tayi murnar ganin hankali kwance harda albarkar aure.

Sunje Kilgore inda Ard'o shima yayi murnar ganin su, daga nan suka wuce Argungu, nan fa Mama ta shiga tsokanar Zainab wai daga zuwa India sai dawowa da babbar tsaraba ita dai sai sunne kai take kunya, Abdool ne mai shige mata.

*2 weeks later...*

Wayarsa ce tayi k'ara my Zee ya bayyana a screen, da sauri ya d'aga "yadai Zee ko jikin ne?"

Cikin walahalalliyar murya ta ansa "Dr kazo gida banda lafia".

" u see saida da na gaya miki bazan fita ba labour kika saboda naga syn nata kikace lafia qlau kike, koma dai ba shine ganinan in d next 2mnt" saida ya gayama wani Dr abokinsa sannan ya d'aukota dan shi duk b'angarensa ne, bazai iya k'arbar haihuwarta ba, balle yanda yaga tayi wujiga-wujiga da ita, Mami ya kira tuni ta dira a asibitin.

Suna nan Zaune tun abin safe har har rana ana Abu d'aya, sai fitowa nurse keyi suna cewa ta kusa dai, yanaso yaje saidai zuciyarsa ta gama tsinkewa, ya tausaya mata sosai irin doguwar nak'udar nan ce, ganin tasha wahala tayi har k'arfinta ya k'are, yasa suka yanke hukuncin yi mata C/S.

"Dr ka yafemin bana tunanin tashi daga gadon nan, don Allah ka yafemin duka laifuka na" ta fad'a da muryan rad'a Wanda shi kad'ai yaji dan yakai kunnensa dai dai bakinta, cikin wahala take maganar, kama hannun Mami tayi amma ta kasa magana sai bakinta dake motsi.

Mami sarkin tausayi har da hawaye ganin yadda surukar tata ta koma "Aa Zainab bakiyimin komai ba, Allah ya fito dake lafia, Allah ya saukeki lafia" daganan aka shiga da ita
Operation room.

One hour...

Jariri ne kato kaman ka lashe don kyau aka fito dashi, an shirya shi tsaf cikin Round up Red, cikin murmushi Mami ta amshi babyn tare da cewa "Mashaa Allah, barakallah".

Dr kam tambayan uwan kawai yake kota kan babyn baibi ba, kasha nurse tayi dakai " sorry sir...." What "ya katseta tare da tafiya luu k'asa a some.


_=?-?=?F?


=؄?Meryerm Abdool=؄?
[9/12, 4:05 PM] =؄?Meryerm Abdool=؄?: =ؤ? ```ABDULMAJEED``` =ؤ?

(' *Servant of Majesty* ('



Na
=؄? _Meryerm Abdool_ =؄?


? *Pure moment of life writers*
P.M.L=ت?
(We don't just entertain and educate we touch the heartd' of the readers=???)



```Manzon Allah S.A.W yace da d'an Abbas:-```

_"yakai yaro ka kiyaye Allah zai kiyayeka, ka kiyaye Allah zaka samesa a gabanka, idan zakayi roko toka roki Allah, idan zaka nemi taimako toka nema gurin Allah, ka sani da ace al'umma zasu taru gaba d'aya akan su amfaneka da wani abu, to bazasu iya amfanarka da komai ba face abinda Allah ya kaddaro maka, kuma da ace zasu taru akan su cutar kai da wani Abu, to ba zasu iya cutar da kai da komai ba face abinda Allah ya kaddara maka, takardu sun bushe, an d'auke alk'alami,_tirmizih

A wata ruwa daba ta tirmizih ba cewa yayi _ka kiyaye Allah zaka samesa a gabanka, ka tuna da Allah yayin farinciki sai tunaka yayin ki'unci, ka sani duk abinda ya sameka ba'ayi shi dan ya kubuce maka ba, haka duk abinda ya kubuce maka dama ba'a yishi dan sameka ba, ka sani dukkan nasara tana tare da hak'uri, haka bakinciki yana tare da farinciki, kuma dukkan tsanani yana tare sauk'i_ ( Arba'una Hadith).=?L?

*=?? k'anwata Jannart lamed'o ki sani kina raina kullum, bazan mantaki ba koda kuwa ke kin mantani ne=?? #ana mugun tare iya wuya# >?8? @&>?8? @&>?8? @&*






=??? *Episode* 186--190




"What nonsense u done here Nusaiba?" Dr Ma'aruf ya fad'a cikin tsawa yana fitowa daga theatre room d'in.

"Sorry sir" ta fad'a cikin tsoro, "get out in my sign, ki jira query dan bakisan aikinki ba" sum2 ta fice cike da fargabar abinda zai faru, umarni yabayar na d'aukar Dr Majeed sannan yaje gun Mami dake tsaye kamar an dasa jikinta sai rawa yake kamar mazari, Allah ya tsare yaron bai fad'i ba.

"Mama don Allah ki kwantar da hankalinki kada abun yayi yawa, dukkan rai bata wuce lokacin ta, don Allah ki zauna, barin duba Dr" babyn ya ansa tare wucewa d'akin da aka shiga da Abdool.

Taimakon gaggawa ya shiga bashi cikin 'yan mintuna ya fardad'o da sunan Allah a bakinsa, sannan a hankali ya fara bud'e idonsa ganin d'akin da yake ciki ya tabbatar masa ba makarki yake ba komai ya faru da gaske kenan, sauke idonsa akan Mami dake gefensa yayi, sai Dr Ma'aruf dake tsaye Kansa, bakinsa ne yayi masa nauyi yana son magana amma ya kasa sai bakinsa dake motsi, hannunsa Mami ta kama "ka daure Son" shine kawai ta Iya fad'a, saboda yanda zuciyarta ta tsinke, tasha ganin mutuwa kuma tasan zafin mutuwa saidai wannan akwai tausayi a ciki musamman ma jaririn da d'anta su tafi tausayawa.

"Mami na daure fa kikace kina nufin, da gaske Zainab ta tafi ta barni da tabar jaririnta?"

Dr Ma'aruf ne ya dafashi tare da bubbuga masa kafad'a "Abokina kada ka mantafa kaine mai bawa wasu hak'uri da nuna musu yadda da k'addara idan sukayi rashi, kayi hak'uri Addu'arku kawai tafi buk'ata yanzu"

"Hakane Dr Ma'aruf, na yadda da k'addara kuma na yadda kowace rai bata wuce lokacinta, Zainab inshaa Allah ke 'yar Aljannace, ke matar kirki ce, ke mai addine, ina miki kyakkyawan zato, Allah yasa mutuwa ta zamo hutu a gareki Allah ya arbarkaci abinda kika bari" sai hawaye kebin fuskarsa kaman fanfo, haka Mami, Dr Ma'aruf ma saida ya zubar da nasa hawayen gwanin tausayi.

"Dr ina abinda aka Ciro" yace ganin ba baby a d'akin, "yana hannun nurses bari na karb'oshi" dawowa yayi tare da babyn, ansarsa Abdool yayi tare da kafesa da ido, tuni k'auna da tausayin yaron suka rufesa, sai bacci yake abinsa, baisai mai ake ciki ba, maganar Zainab ya tuna.

_Dr pls idan namiji na Haifa ka maida mishi sunanka, idan kuma mace ce, ka saka mata sunan Aunty Ramlah_

Wasu hawaye ne suka zubo masa yasan yayi rashin mai k'aunarsa da gaskiya mai son duk abinda yakeso, hud'uba yayima yaron da _Abdulmajid_ sannan ya mik'a shi ga Mami, "Dr Kaine gurin Gawar Zainab" yace tare da sakkowa.

Addu'a sosai yayi mata, yana hawaye ganin ta a kwance kamar me bacci amma kuma ba barcin duniya bane.

_Duniya! Bakida tabbas_ =?-?


Wani envelope Dr Ma'aruf ya bashi yace Inji marigayiyar ta bayar a bashi, ansa yayi sannan suka d'auki gawar zuwa gida dama tuni Mami ta kikkira kuma duk sun taso don samun jana'izar.



***************

Wasik'u ne guda 3 cikin envelope d'in, ta sama a rubuta zuwa ga mijina, bud'ewa yayi ya fara karanta wa.

_"Amincin Allah ya tabbata a gareka mijina, nasan koda wasik'ata zata sameka, watak'il bana numfashi a duniya, kayi hak'uri da rashina inada tabbacin Aunty Ramlah zata maye maka fiye da gurbina, addu'arka nafi buk'ata a yanzu mijina, naso ace na rayu a dai2 wannan lokaci da nake buk'atarku saidai Allah yafimu sanin gaibu, naso na rayu koda na minti gudane da abinda na Haifa naso naji duminsa shima yaji nawa, ina rokonka daka zame masa uwa da uba dan Allah karka barshi ya koka da rashina kaida Aunty Ramlah, ina muku fatar Alkhairi, sannan ka sani ina k'aunarka har numfashina na k'arshe, ka bawa aunty Ramlah wasik'arta a ranar da ta tare gidanka, d'ayar ka bawa iyayena, pls kazo ga gawata ka wankeni kamin sutura sannan ka sadani da gidana na gaskiya, nagode da k'aunar da ka nunamin a iya zaman mu mijina_

Zainab Salis.

Sanda ya gama karantawa hawaye kwance a idonsa, yana tuna rayuwarsu da Zainab tun daga ranar da ya fara saninta har yau data barshi, bari na har abada, murmushi yayi irin na k'unci "ina miki fatar Alkhairi Zee ta".

Kamar yadda ta buk'ata shi yayi mata wanka da sutura, cikin ikon Allah natsuwa ta saukar masa, sai addu'a yake mata har ya kammala.

Tuni gidan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login