Showing 45001 words to 48000 words out of 88300 words

Chapter 16 - ABDULMAJEED BOOK by Meryam Abdul.doc

09 Oct 2025

1611

shima sukayi mishi bayani, yayi na'am kuma yace dashi za'aje Neman Auren.

Daga nan suka wuce Argungu Baba yace tunda yana da Baban sa Mansur yaje masa, ita kuma inna tace kishi take taya Ramlah, nan dai sukayi wasan kaka da jika.

Sunje an tsaida rana wata uku masu zuwa aka saka sunyi komai na al'ada da Ard'o akayi komai, haka sukaci gaba da soyayyar su da Zainab duk dashi ba wani jinta ransa yake ba, adai rashin uwa yayi Uwar d'aki ne.

Zainab kuma ta dage da kula dashi da nuna mishi salon soyayya dan tasha alwashin saita koyamasa sonta saita samu gurbi a zuciyarsa ko baikai ba kamar na Ramlah ba (fatar Alkhairi Zainab).


*******************

B'angaren 'yan boarding kuwa ranar da aka kaisu Ramlah taga students birjik da irin uniform d'inta, dad'i kamar yayi killing d'inta, bale data ganta a class, gata kan desk ga malamai na shigowa suna yi musu lesson, duka attention nata yana gunsu, 'yan aji kuwa sai zuwa suke suna mata welcome tare da tambayan sunanta suma suna gaya mata nasu.

Ana tashi suka d'auki kayansu zuwa hostel, nan sai murna take tsarin ya burgeshi ga gado up and down, suna sallah suka huta tace ma Nihal.

"Nifa yau tuwon milk zanyi insha miyar Milo" ganin tulin madarar da aka jibgo musu, dariya Nihal tayi "aiko kiyi abinki nidai abincina zanci"

Nan ta kwaba madara kamar tuwo ta dama Milo tana dibar madaran tana tsoma Cikin Milo, tana ci tana daga k'afa sama Nihal kam sai dariya take mata, suna cikin hakane sukaji an buga CSTA.

Maida abincin Nihal tayi "Ramlah ki kwanta an buga kwanciyar rana" shekeke ta kalleta "haka nan mutum baijin bacci ya kwanta, tab kidai kwanta ke, in kinaji".

Jin alaman senior zasu shigo yasa Nihal kwantawa ita kam sai k'ara daga kafa take tana dariya, " kutuma kit! Ke dan Ubanki me kikeyi baki kwanta ba" wata daga Cikin su ta fad'a.

"Nidai ba Ubana, yo mutum bayajin bacci, na dole zaiyi ne?"

"Ke!! Wa kike zagi d'an kazar ubanki" wata ya fad'a tare da gara bulala zata watsa mata.

Da Sauri Nihal ta tashi "yi hak'uri Senior Zulfa, new comer ce yau tazo".

" me ai irinsu nake nema dama, naga alaman Kanta na rawa tashi muje, filin daga dan k'aniyarki yau zakisan kin shigo boarding "


"Me, meye shi d'in? wallah ba inda zani....."





*WO Ramlatun Baffa 'yan boarding*>?#?















=؄?Meryerm Abdool=؄?
[9/3, 9:37 PM] =؄?Meryerm Abdool=؄?: =ؤ? ```ABDULMAJEED``` =ؤ?

(' *Servant of Majesty* ('



Na
=؄? _Meryerm Abdool_ =؄?


? *Pure moment of life writers*
P.M.L=ت?
(We don't just entertain and educate we touch the heartd' of the readers=???)




*_Alhamdulillah bini'imatihi tatimmusalihat, may wishes 2 all as d witness of seeing eid~el Mubarak bil khair indeed, takabbalallahu minna wa minkum.ina taya daukacin musulmin duniya barka da sallah, Allah ya maimaita mana shekaru masu albarka Amen, eid Jamil 2 all=?K?


_And I need ur wishes cos 2morrow is my day, I mean is my birthday, so I need ur concern, hope I will get it!_




*Sallah gift just for u my fans*<؁?=?L?






=??? *Episode* 161--165






Da sauri Nihal ta sakko daga gadon, duk'awa tayi gaban wata daga cikinsu wacce tunda sukazo gun ko tak batace ba, sai wani kallo da takebin Ramlah dashi wanda ni kaina basan ma'anarsa ba.

"Pls senior Safara'u kuyi hak'uri wallahi bak'uwa ce batasan komai ba akan harkar school" tasan shirun Safara'u ba alkhairi bane dan duk a cikinsu tafi kowa k'eta.

Mugun kallo ta watsa mata "go back to ur bed stupid! Ko sai na had'a dake ne?" Ta fad'a cikin tsawa.

Sannan ta k'ara cewa "me kuke jira ne Zulha a kaita mana idan ba zata da kafanta ba" tare dayi gaba.

Jiki a sab'ule Nihal ta koma kan bed tare da kwantawa tasan halinsu sarai idan ma kana begging nasu kamar zugasu kakeyi, kuma shi yafi komai sauk'i su had'a da ita, gata tsoron a tab'a mata lafiyarta, sam basuda imani shiyasa daga an dawo Hutu suke dawowa basa k'ara ko kwana d'aya(tau anyi missing cin amana).

Ramlah sai kallonsu take d'aya bayan d'aya ko a jikinta wai an tsikari kakkaura, unexpected taji an figxota da k'arfin tsiya, kaman ta kife, haka Zulfa ta fara janta kiiii! A k'asa, turjewa ta farayi amma da yake Zulfa namijin gaske ce, cikin k'arfi taci gaba da janta, a haka suka fice daga room d'in.

Wani corridor sukabi saiga fili ya bayyana tsakanin room zuwa room, already Safara'u na gurin damin buloline gabanta, fuskarta murtuk'e ba rahama a ciki, tsakiyar filin Zulfa ta jefa Ramlah, mik'ewa tayi tare da kakkab'e jikinta tana binsu da kallon renin hankali..

Nihal tana ganin sun fice ne, ta d'ora hannu aka dan tasan yau k'ashin Ramlah ya bushe tunda ta shiga hannun wad'annan hatsabiban miyagu ba da kowa shakkarsu yake, wani tunanine yazo mata da sauri ta sakko a gadon tare da ficewa zuwa room d'in metrum d'insu..

"Wato kega fitsararriya ba, tabas yau zakisan kinzo boarding yau zamu sauke miki kome ke kanki" kallo sauran tayi tare da zabar zabgegiyar bulala, nan fa kowacce ta zabi tata, suka rufa Kanta da duka ta ko'ina.

Ramlah akwai taurin rai kuma idan bugune ai Inda sabo ta saba, saidai fa wannan dukan ya girmi na Iya Hari, amma taurin rai da kafiya irin na Fulani, ya hanata ko motsawa balle kuma ayi tunanin tayi kuka kota basu hak'uri, hakan ya k'ara tunzirasu su ci gaba da jibgarta kamar Allah ya aikosu gareta.

Da gudu ta isa dak'in metrum d'in "Inna Yashe ga can su Senior Zulfa sun rufa da duka akan 'yar uwata da aka kawo yau, kawai saboda tak'i ta kwanta CST".

Mik'ewa tayi tsaye tana salati "Oh ni yashe! Ba an dawo ba, wad'annan ja'iran yara bazasu tab'a barina na huta ba, ke mutahi kahin su la'anta 'yar mutane" a tare suka fita Nihal ta koma d'aki ita kuma ta nufi filin daga.

"Lahaulah wala kuwwati, me nake gani haka? Ke Sanfara kasheta zakuyi eye? Walle ku rabu da 'yar mutane ko 'yanzu in hadaku da firansafal" duk tana k'ok'arin janye Ramlah take wannan maganar, saidai ko kallo bata ishesu ba balle tayi tunanin suji magananta.

Ramlah ta bugu iya buguwa amma saboda taurin rai da kafiya tak'i basu hak'uri kuma tak'i kuka duk kuwa da tanajin bugu har ranta, hakan ya k'ara tunzurasu suketa gibgarta a dole saita basu hak'uri.

Inna yashe kuwa gurin ansar Ramlah aka tsala mata bulala, nan fa ta shiga tsine musu hadda kukanta, gyale ta Zara tana tafe tana bala'i "shegu bak'ak'en d'iya yau iya shegen naku harni bai bari ba, idan na gayama ita firansafal ai sai Ku had'a har ita" a haka ta isa gidan Mama picy tana banbami, nan ta shiga zayyana mata hadda k'ara gishiri, nan take ran picy ya b'aci labour master da sagen ta kira nan suka hadu suka nufi hostel d'in a motarta.




*****************




"Don't ever touch her again useless girls" a tare suka tsaya cak da dukan da suke mata jiyo muryan principal d'insu, a razane suke kallonta tare da sauran mutanen da suke tare dan basuyi tunanin inna yashe zataje ba.

Itama Ramlah jin muryan matan da kuma tsayawar dukan da ake mata dataji ne ya sakata d'agowa da rinannun idanuwanta da suka yi jajir tsabar azaba ta taji.

"U should meet me at assembly ground right now, and announce it 2 all" ta fad'a tare da mik'awa Ramlah hannu alaman tazo.

"Come here dear" da sauri ta isa gareta, rungumeta tayi sannan suka juya gaba d'aya suka nufi mota.

Su Safara'u jiki a mace sukayi announcement d'in sannan suka shirya in house where dake lokacin pref ma ya kusa.

Principal umarni taba labour master akan a kira sauran malamai sannan ta wuce da Ramlah gidanta, ruwa masu zafi tasa maid d'in ta ta tafasa, Inna yashe ta gasama Ramlah jikinta Wanda yayi rud'u-rud'u da zanen bulali ga wani jawur da tayi abinka da fara, rub aka shafe mata jiki dashi sannan aka bata magani tasha, daganan suka nufo assembly ground d'in.

Students da teachers gaba d'aya sun hallara an shiga layi as always, da yake ma farkon dawowane wasu basu dawo ba, fuska murtuk picy ta hau saman gurin tare da Ramlah da inna yashe, addu'a akayi as usual sannan akayi taken k'asa kana picy ta fara jawabin mak'asudin taron na gaggawa.

"Na samu abinda banyi tunani ba a wannan makarantar tawa, wato seniority abin ya bani mamaki da tsoro, kamar yadda kowa ya Sani wannan makarantar private ce, ba government ba, kud'i mai tsoka iyayenku ke biya su kawoku nan dan Ku samu ingantaccen ilimi, da kuma rayuwar 'yanci amma abin takaici Ashe akwai wasu 'yan iska wad'anda sam ba karatune gabansu sai tsabagen k'eta da cin amana, I shock in dis school ace ana irin wannan abun, tanx god dan ba yau aka fara ba amma Allah ya tona mana su yau."

Taci gaba cikin murtuk'e fuska har iya yau "to ba zamu lamunci wannan sakarcin ba ya zama wajibi ayiwa tukkar hanci gudun abinda zaije ya dawo, kuma ya zama darasi ga duk mai niyyan aikata irin abinda sukayi" nan ta kira sunayensu jiki a sanyaye suka hau gaban Assembly duk jiki a Mace, nan aka umurci sajen yayi musu 30 lashes and then labour master ya yanka musu field mai girma gashi schools tayi haki ko'ina, tare da anshe musu prefect ship nasu da tabbacin duk wacce ta k'ara kwantanta hakan to za'ayi withdrew nata ne kawai kuma ba dawowa ko waye ubanta ko, sannan taja kunnen junior akan hakan bazai zama dalilin su raina senior nasu ba, su basu respect a matsayinsu na na gaba dasu, duk wacce aka kawo da laifin raina senior tofa zata fuskanci hukunci.

Da haka taro ya watse junior sai murna suke sun samu freedom, yayin da Senior suka shanye jinin jikinsu.

K'ara kiran Ramlah ta bata hak'uri akan abinda ya faru tare da bata tabbacin hakan bazai sake faruwa ba, a mtsayinta na new comer kada ta tsorata tace ba zata dawo ba, daganan suka wuce class don gudanar da pref, tun daga ranar komai ya dawo normal ba wani seniority a school d'in tuni su Safara'u suka shiga taitayinsu suka kama Kansu.

Sannu a hankali Ramlah ta fahimci boarding da rayuwar boarding, ta saba da ita a yadda take, bata wani sha wahala dan duk k'uncin rayuwar boarding tafi ta gidan iya Hari saidai tana kewar baffa da mami da uwa uba d'an binni mai gilashi, kullum suna tare da Nihal ita kad'aice k'awarta, ba Momy ba Darling duk da dinbin masu son k'ulla alaka da ita da takeda.



***************

B'angaren Zainab kuwa ta Dage gurin Neman fili a zuciyar Dr kuma da alama tayi nasara, don Zee mutum CE mai kulawa da nuna damuwarta akan Abu, tun Abdool bayajin komai game da ita har yanzu yakai yana jinta a ranshi soyayya tsabtatacciya suke gudanarwa kowanne na kaf kafa da d'an uwansa.

Lokacin da ta gayama Waleed ya shiga tashin hankali dan harga Allah yana k'aunar Zainab, saidai dole ya hak'ura don yanason farincikinta, fatan Alkhairi yayi mata, itama tayi masa fatan dacewa da mafi alkhairi.



****************



*End of month*

Tsaf su Mami suka shirya zuwa visiting d'insu Ramlah cike da provision kaman ba'a zo musu last month da irinsa ba (ni kuma nace koya zasuyi dashi oho) Abdool ne ke driving cike da nishad'i zaije yaga Ramlatunsa, su Husna sai zumud'i suke zasuga Aunty's.

Tun gate Ramlah ta tsinkayo aiko da gudu ta kwasa taje garesu, Nihal sai k'urarta ta hanga itama nan ta bita da nata gudun.

Tasa isa jikin Abdool ta fad'a tare da sakin...........





_Fatan Alkhairi masoya barkanmu da Sallah, barka sake saduwa_=?K?





=؄? Meryerm Abdool=؄?
[9/5, 11:49 PM] =؄?Meryerm Abdool=؄?: =ؤ? ```ABDULMAJEED``` =ؤ?

(' *Servant of Majesty* ('



Na
=؄? _Meryerm Abdool_ =؄?


? *Pure moment of life writers*
P.M.L=ت?
(We don't just entertain and educate we touch the heartd' of the readers=???)





```=?1? Wallahi i'm so speechless, bansan da wane word zanyi amfani na gode maku ba friends, kun nunan k'auna sosai, kunyi min k'ara nagode da birthday wishes naku, Allah yabar zumunci da k'auna Ameen=?O?






=??? *Episode* 166--170




Tare da sakin kuka "subhanallah Ramlah kuka again menene kuma ko an k'ara dukanki ne?" shiru tayi tare da lafewa, yayi dai2 da isowar Nihal da murnan ta, ta rungume Mami "uhm ba'a mata komai bafa kawai dai tana murnan ganinku ne, kunsan munyi missing naku".

Dungure mata kai Mami tayi "tau parrot munji, aifa yanzu zaki fara surutun naki" sannan ta Shafa kan Ramlah "dota haka zaki dinga mana ko, aiko saimu daina zuwa tunda tayar maki da hankali muke, sai a ringa aiko maku Sale driver kawai".

" Aa Mami na daina baran k'ara ba, kinji Mamina?" Ta rungumeta, su Husna sai dariya suke mata, Abdool kuwa kallonta kawai yake yana murmushi, a haka suka k'arasa Filin visiting d'in.

Wani babban carpet suka shimfid'a aka zazzauna, abinci aka gabatar nan sukayi lunch gaba d'aya, sai nishad'i su Ramlah keyi, ji suke kaman a gida ake, daga nan aka shiga fira, sunata basu labarin School wahalarta da dad'inta, nan suka gangaro firar gida Mami ke gayamusu Auren da Abdool zaiyi.

Duk da k'aranci shekaru irin na Ramlah saida Abinda ya daketa a zuciya, amma dake tanada wayo saita waske, murmushi tayi tare da d'an tsalle.

"Allah Mami, waye matar?" Nihal kam kwab'e fuska tayi tare da turo baki, Abdool kam ji yayi ba dad'i duk sai yaji wani iri.

"Auntynki ce fa Zainab".

"Lah! Aunty Zainab? Wlh nayi murna sosai Yaya, pls d'an kira mana ita mu gaisa Yaya"

Shidai baice komai ba sai kallonta yake, Nihal sai jifanta da harara take irin ta bata Haushin nan (oh su Nihal akwai aiki kenan) Mami kam sai murmushi take ba kad'an ba Ramlah ta burgeta, saidai dama tasa hakane zai kasance dan tasan ai yarinya ce da wuya ta damu tunda ko ma'anar auren bata sani ba.

"Kaji Yaya" ta k'ara fad'a hakan yasa dole ya kira mata ita, aiko da murna suka gaisa, hadda su Nihal duk sun gaisa ta tare da tambayansu karatu.

Zainab ta yadda da Ramlah yarinyace sosai kamar yadda Abdool ke fad'a, ko a jikinta bata nuna ta damu ba hadda kiranta da Aunty, nan take ta sak'a a ranta zatayi zama mai kyau da Ramlah zata rik'eta kamar su Amal k'anninta, zata roki Allah ya yaye mata azabar kishi da takeda.

Anan suka wunin musu tun safe sai marece suka wuce, suka barsu da kewa, haka suka kwashi kayansu nik'i-nik'i sai hostel, Nihal kam tun tana mata fushi ganin bata kulata yasa ta ware sukaci gaba da sha'anin gabansu...


********************


Kwanaki sunja wata ya wuce tuni su Ramlah sun zana jarabawarsu anyi Hutu, an dawo gida cike da farinciki, sai kuma hada hadar biki da aka shiga basu can basu nan Nihal ma tuni anyi giving up, dan ta fahimci Aunty Zainab akwai kirki tuni suka saba da ita kullum suna mak'ale a waya, tuni sukayi sabo har ma da Amal kanwarta kusan sa'arsu ce, Baffa kamar yadda ya alkawaranta yazo ganin Ramlah ranar kuwa kamar ta koma cikinsa tana nanik'e dashi har dare bacci ne kawai ya rabasu, kashe gari ya koma da kukanta da komai na kar ya tafi, haka Mami ta cikasa da tsaraba, itama Ramlah ta bada tata akaiwa iya Hari da gwagwaninta da Aminiyarta Deluwa.

Komai aka saka masa lokaci to za'a yazo kamar wucewar iska, a yau dubban jama'a suka shedi d'aurin Auren Abdulmajid Auwal Sada da Zainab Salis Madaki, taro yayi taro can na hango Ango da abokansa su Hakeem k'irjin biki, su Ismael da sauran su, gefe d'aya su Alhaji Sada na hango su Baba, Ard'o ma ansha rawani, su kawu Mansur, su Dady Ayuba, Sani, salis, Rabi'u, Dadyn Hakeem, duk ba'a barsu a baya uban amarya ma baki har kunne tsabar farinciki taro dai mashaa Allah sai fatan Alkhairi.

Cikin gida na garzaya, ya cika ya batse dak'ar na zak'ulo Amarya subhanallah zanso Ku hasko Zee tayi kyau like take away, ni kaina sai daga baya na ganeta sanye take cikin wani Arnen code lace Red and golden, head, shoes, purse duk golden ne, anyi mata d'auri irin na Amare fuskar tasha make-up sosai irin na amare, sai k'amshi take zubawa kamar anyi barin perfume a jikinta.

Ido ta k'ara warewa dan ganin 'yan biki dakyau can na hango su Ramlah ansha ankon wani material black and silver su uku da Nihal da Amal, ware ido nayi nace su kuma wad'annan yaushe gari? Harara ta balla min "naki wasane ai tun ranar da aka fara even muka bayyana" ah lallai kunsha gari na fad'a tare da k'ara wa kafata iska, Uwar Amarya sai nan da nan ake da bak'i zuciyarta fal farincki ayau sun sauke wani nauyi d'aya rataya a kansu, sosai ta yaba da Ramlah don tun zuwansu yarinyar ta kwanta mata arai duk Wanda aka nunama ita a matsayin abokiyar zaman Zainab saiya yaba don dagani yariyar batada matsala ita kam batamaso ana nunata, sai sunne kai take tanajin kunya dan harga Allah mantawa take da auren.

Zuwa karshe 4:00p suka nufi giginya hotel inda aka gudanar da mother's day, last even nasu sai dare aka tashi inda su Ramlah suka rak'ashe kamar ba gobe, su Abdool kam basusan ma anyi ba, dan ana gama d'aurin aure suka d'auki hanya don gudanar da tasu walimar da Hakeem ya shirya musu.

Washe gari da saffafe motocin d'aukar Amarya suka sola hanya, bayan tasha nasiha sosai daga iyayenta, sai kukan rabuwa take da gida duk soyayyarta da Abdool.

2:00pm a Kd tayi musu gidan Mami suka sauka bayan sunci susha an dank'a amanarta ga surukar tata, daganan Mimi da k'awayenta sukayi musu jagora zuwa gidanta dake unguwar malali Wanda Abdool ya kama dan yace gidan sa na cikin asibitinsa ba yanzu zasu tare ba sai ya an tashi bude hospital din gaba d'aya.

Gidane matsakaici mai kyau dashi, sosai danginta suka yaba, har kuryar d'aki kan gadonta sannan suka barta da k'awayenta suka koma gidan Mami inda sukayi masauki.

Haka k'awayenta suka sakata gaba da tsokana yaudai gata ga Dr tsami yakar, shiru tayi musu tanata murmushi Allah dai tasan farincikinta a yau, yau gata gidan Aure kuma da masoyin rayuwar ta Dr

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login