Showing 63001 words to 66000 words out of 88300 words

Chapter 22 - ABDULMAJEED BOOK by Meryam Abdul.doc

09 Oct 2025

1600




=??? *Episode* 211--215




Ware takardar Mami tayi, bayanai sun nuna tana d'auke da cikin 3weeks, Mamaki ne ya kama Mami Ashe dai abinda take hangowa a idon Ramlah shidin ne, "to yaushe hakan ta faru?" Tunani ta shiga, "okey wato ranar da yace ta zame kenan, kai yaran yanzu bata ido, tunda yace na bashi ita nace ba yanzu ba, shine ya nunamin iyaka, to ai yanzu yazo gatanan can su k'ara sa" duk Cikin ranta take maganar, amma a kasan ranta tayi farinciki da cikin saidai bataso ya faru kafin tariya ba, duk da tana da tabbacin Abdool bazai juyawa Ramlah baya ba, hasalima sonta ne yaja faruwar lamarin.

Murmushi tayi tare da kallon Dr Ubaid "mashaa Allah, Allah ya inganta".

Shima smiling yayi " Ameen Mama, amma Dr Majeed baya gari ne ko?"

"Aa yana nan hospital dai ya kwana shiyasa muka zonan kawai" ta fahimci so yake yasan meya hana ya dubata da kansa, tunda b'angaren sa ne.

"OK, bari nayi saurin kiransa na bashi albishir" murmushi kawai Mami tayi, sai yanzu ta gane dalilin sa na rashin zuwa wato yasan meyake damunta, kwafa tayi a ranta alaman zasu had'u.

Magunguna ya basu yace ayi amfani dasu kafin Dr Majeed ya k'ara dubata, Ramlah dai zaune kawai take kamar mutum mutumi duk an sakata a duhu, ta k'asa gane komai, sallama sukayi masa sannan suka wuce, biye take da Mami jikinta duk sanyi ganin kallon tuhuma da Mami ke aika mata.

Bayan sun shiga mota ne Mami ta mik'a mata result d'in, hantar cikinta saida ta kad'a tare da zaro ido, sai hawaye sharr "wlh Mami ba lai....." Katseta tayi.

"I know ba laifinki bane, amma meyasa bakk gayamin gaskiyar abinda ya faru ba? Kodai baki d'aukeni a matsayin Asma'u ba?" Mami ta fad'a Cikin d'aure fuska.

Girgiza kai ta shiga kamar k'adangarwa sai hawaye ta k'asa magana, Aida nauyi ta tunkareta da wannan zancen koda Asma'un ce raye ba zata iya gaya mata ba".

"Na fahimceki yi shiru, share hawayen ki kinji" Mami tace da sigar lallashi, sannan tayiwa motar key.

Life kanta tayi a cinyarta tana kuka mara sauti "shikenan Yaya Abdool ya wargaje min rayuwa, yanzu shikenan, irin abinda ya faru da Larai ne zai faru dani, na shiga uku" wata 'yar kauyensu ce bayan an d'aura mata Aure ba tare ba mijin yayi mata ciki, aiko akayi ta rikici daga k'arshe ya saketa yace ba cikinsa bane.

Itama tunanin ta haka Abdool zaiyi mata, k'ara rushewa da kuka tayi na tausayawa kanta, yanzu shikenan idan Mami ta yadda Kilgori zata koma gurin Iya Hari "oh dota meye na kuka? Wipe ur tires zanyi maganin abin kinyi" Mami ta katseta jin sautin kukanta.

Tissue da Mami ta ta mik'a mata ta k'arba ba musu ta share hawayen, saidai ranta a jagule yake, lumewa tayi akan seat tare da lumshe ido, tunani barkatai takeyi, na neman Mafita.

Mami da kanta da had'a mata soft breakfast ta sakata gaba sanda taci sannan ta bata magani tanasha ba dad'ewa bacci ya d'auke ta nan parlour kan 2seat, jin saukar numfashinta ne ya tabbatar wa Mami tayi bacci, mik'ewa tayi bayan ta gyara mata kwanciyar.

Nihal ce ta fito "Mami kun dawo, meke damunta? Sisto ya jikin?" Ta fad'a a tare tana k'ok'arin tab'a jikinta.

"Karki tasheta mana yanzu ta samu bacci" Mami tace, sannan tace "ina junior?" Yana ciki yayi bacci " ta ansa.

Shigewa d'aki tayi ba tare data k'ara magana ba, wayar ta, ta janyo ta kira k'awarta bayan ta Zaune kan sofa, bayan sun gaisa "furnitures nakeso ayimin oda designers a satin nan Hajia in da hali" banji abinda k'awar ta fad'a ba.

"Uhum kedai bari, 'yata ce zata tare kuma Cikin satinnan nakeso ayi tariyar".

"Ada kenan, ai Abdool ya b'ata komai, ciki fa yayi mata dan ya nunan iyakata, nidai ayi k'ok'ari ayi komai in time ta tare kawai su barni na huta nima, koma kawai ki sayo komai biyu na had'a hadda na nihal ayi zuwa d'aya" ta sake ansata

Dariya itama tayi "to ai yaran yanzu sun shafawa idonsu toka ba kunya" sannan sukayi sallama, saida k'awar tata ta bata shawaran ta bashi matarsa tun da ya nuna buk'atar ta tace Aa sai sun shiga jami'a to ai ga digiri nan an samar mata Inji kawar.




**************



Yanke shawarar yaje gida kawai yaga halin da tace ciki, ba wani boyo a yanzu kam tunda Allah ya tonasa, koma ya fad'i ko kar ya fad'a bayyana kansa zaiyi, tare da Hakeem suka taho dan yace zai biya yaga sweetyn sa, Abdool sai tsiya yake masa wai baya kunyar sa a matsayin sa na sirikinsa, dariya kawai yayi yace ba wannan kuma, nan dai sukayi ta zolayar juna kamar yadda suka saba.

Nihal da har yanzu tana parlour tana jinya, itama har yanzu bata farka ba da yake harda maisa bacci a maganin, gashi tasha kuka, sai bacci take, ga hawaye sun bushe a idon, ita Nihal a nata tunanin zafin ciwo ne ya sakata hawaye.

Tsayuwar motarsu ce, tasa Nihal shigewa d'aki, dan tasan tare da Hakeem dayake ya gayama ta zuwan, da sallama suka shigo yana ganinta kwance a parlour tare k'ofa yayi wai saidai Hakeem ya tsaya daga waje Nihal ta iskoshi can amma bazai kallar masa mata ba.

"Dad'in ta dai nima inada matar ko?"

"Bamu shaida ba, kanada jingina dai" ya fad'a yana dariya.

"Zaku shaida ne very soon, kai kanka ka sani"

"Tau naji tafi dai" ya turasa baya, girgiza kawai Hakeem yayi yana fad'in "zaka zo hannu zan rama nima" yace yana wucewa farfajiyan gidan, shi kuma ciki ya shige yana dariya "koka rame ba"

Sunkuyawa yayi tare da pecking goshinta, yana kallon ta da murmushi a fuskarsa, tayi wani fayau da ita ta k'ara haske, ga hawaye kwance a fuskarta, alaman kuka tayi kafin tayi baccin, tausayinta ne yaji yasan idan aka bibiya shine silar kukan, k'ara sunkuyawa yayi da niyyan lashe hawayen, dai2 fitowa Nihal cikin kwalliyar ta ta zuwa gurin Hakeem.

Fuskewa yayi, ita kuma ta sunkuyar da kai tare da gaidashi d'akin Mami ta wuce dan gayama ta zuwan Hakeem, shi kuma d'an siririn tsaki yaja "mutum ba damar ya sake da iyalinsa, gaskiya ya kamata mu tare hakanan" part nasa ya wuce, wanka yayi tare da sauya kaya, sannan ya fito dan shiga inda Mami.

Still bacci kawai take shaka abinta "aifa kin samu aikinyi baccin masu ciki" yace yana smiling, sannan ya shiga d'akin Mami da sallama.

Ciki ta ansa mishi fuska tamke, zama yayi a darare kan sofa, yana gaida ita "lafia" ta ansa a tak'aice, tare da mik'a masa takardar .

Shiru yayi kansa k'asa bayan yaga abinda takardar ta k'unsa Wanda already yasan dashi "sannu ko Abdool aikin ka yayi perfect" Mami tace ba tare data kallesa ba, still shiru yayi dan bai da bakin magana.

Jin shiru baice komai ba ta shiga surfa masa "wato tunda ban amince, sai kayi mai gaba d'aya ko? Yanzu ka kyauta kenan, duk da addini bai hana kaba amma ai yaci Karo da al'adar bahaushe ko? Yanzu kai fisabilillah idan akayi wa 'yarka haka zakaji dad'i eye?"

"Yanzu da ace ba gida d'aya kuke rayuwa ba, kuma ba jininka bace? Saika iskota har gidansu kayi mata cikin?" Nan fa taita mishi inda take shiga ba nan take fita ba, shiru yayi mata har saida ta sauke aya sannan ya shiga bata hak'uri

"Ba wani hak'uri ai, kaje kayi gyaran gidan ka k'arshen satinnan zata tare, ina shikenan ko?"

Hak'uri kawai yake bata, Sam baiyi tunanin lamarin zaiyi zafi haka ba, ya d'auka rigimar iya ta Ramlah ce, shi baiga abin fad'a ba, tunda dai sunnah ce yayi ba zina ba, akan wata al'ada can daban za'a damu, ai kowa yasan matarsa ce, kamar yadda Cikin ma nasane kuma ta hanyar halal, baiga abin damuwa dan miji ya kusanci matarsa kawai dan bata tare ba.

Kuma ai ko meye ita taja, tunda ita ke shigar da ke tayar masa da hankali kuma har d'aki take iskoshi fa tana kusantansa ai yayi k'ok'ari ma, a nashi ganin, kuma ai zaifi dad'in fad'a ace yayima matarsa ciki before ta tare da ace yayi zina da wata daban.

Sai bayan ya fita ne ya bawa Mami tausayi, tasan yanayin d'anta sarai mabuk'aci ne, ga shigar k'ananun kaya dasu Ramlah keyi Wanda saida yayi magana akan hakan tace ai ba laifi ne, laifin ba nasa shi d'aya bane hadda su, but still dole ta nuna b'acin ranta dan siyama Ramlah mutunci gareshi, amma ba laifi a Cikin haka a musulunci saidai al'adar bahaushe (mata iyayen kariyar al'ada).

Koda ya fito bata a parlour, ta tashi taji jikin da d'an sauk'i shine tai ciki dan watsa ruwa, wucewa yana tunanin ita kuma koda wace rigimar zata zo masa.

Murmushi yayi "unborn ka taimakamin daka zo gashi za'a bani matata cikin sauk'i, love u much 'yar baffa iyayen rigima"................






_kuyi hak'uri waya tace sai a slow matsala tace bani, Hocking take inna dad'e INA typing_








*love u guys buhut- buhut kunsan kanku=?? yes u!=؋?=?
? #one love # all of u* =?L?
















=؄?Meryerm Abdool=؄?
[9/26, 5:39 PM] =؄?Meryerm Abdool=؄?: =ؤ? ```ABDULMAJEED``` =ؤ?

(' *Servant of Majesty* ('



Na
=؄? _Meryerm Abdool_ =؄?


? *Pure moment of life writers*
P.M.L=ت?
(We don't just entertain and educate we touch the heartd' of the readers=???)



*#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*
*#IG PML WRITERS*
*#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*
*#http://maryamsbello.blogspot.com*




```Daga Baban Darda'i (R.D) yace, Manzon Allah (S.A.W) yace:-
Duk Wanda ya k'are mutuncin d'an uwansa, Allah zai k'are fuskarsa daga wuta ranar alk'iyama.

Ma'ana Wanda ya tsare mutuncin d'an uwansa, ya rufa masa asiri, ya boye miyagun dabi'unsa shima Allah zai k'are sa daga wutarsa.

Kenan rufawa d'an uwanka musulmi asiri koda ka kamashi miyagun ayyuka wajibine ka boye su, sannan ka naima masa shiriya gurin Allah a maimakon ka fallasa shi, Allah yasa mu gyara``` =?O?
Tunatarwa ce=?L?







=??? *Episode* 216--220






Tsaye take gaban mirror daga ita sai k'aramin towel tana busar da gashinta da hand dryer, bayan ta gama ne ta shafa mayuka akan ta kama da ribbon, kallon kanta tayi ta mirror tare da d'ora hannu kan mararta "yanzu da gaske cikine dani?" Tace tana b'ata fuska da turo lip gaba, kamar mai shirin yin kuka "oh yanzu mai zan gayama su Besty idan suka gane, wayyo yaya ka cuceni Allah..... Shiru tayi jin an turo k'ofar tare da juyawa dan ganin mai waye.

Tsaye yayi b'akin k'ofar, yana binta da mayataccen kallon, smiling kwance a fuskarsa, tsuke baki tayi tare da d'aure fuska taci gaba da Shafa man ta, smiling yayi mai sauti tare da takowa zuwa inda take, rungume ta yayi ta baya tare da d'aura hannunsa kan mararta, kansa bisa kafad'arta.

Turashi ta shiga yi ba tare da tace komai ba, amma ko motsi baiyi ba saboda rik'on da yayi mata bana wasa bane, ganin ta k'asa kwatar kanta ne yasa ta fashe masa da kuka Wanda da gani na renin hankali ne.

Sakinta yayi tare da janta zuwa bed, zaro ido tayi sannan ta shiga turasa, sakinta yayi yana 'yar dariyar tsokana sannan ya rad'a mata a kunne " me haka baby na, lafiyar unborn d'ina, bafa abinda kike nufi bane, idan kuma Shi kikeso to sai muje d'akina, kinga da junior anan" ya fad'a cike da tsokana.

Wani takaici ne ya turnuk'eta ta k'ara bud'e baki "ka tafi Allah ko in tada junior ya ganka, kuma Allah dole ka zubar min da Cikin nan ko naje a zubar dashi haka kawai sai a ganni da ciki ba tare dana tare ba, kuma bazan yadda na haifesa yayon fitsari ya kamani a banza ba" har ya juya zai fita, yana dariya sai ya jiyo furucinta na k'arshe, tsayawa yayi cak tare juyowa fuskar murtuk'e yayi kanta gadan-gadan.

Baya ta rink'a yi cike da tsoro ganin yanayin fuskarsa, saida ta manne da sofa sannan ta dafe kanta da hannayenta, tana jiran abinda zai mata, shiru bataji komai ba, d'agowa tayi ta gansa tsaye idonsa sunyi ja.

Nunata yayi da yatsa "ke ashe mahaukaciya ce ban sani ba, to duk Wanda zai ganki da ciki shiya dad'e bai canyeki ba, da yake nina kiraki d'akin har nayi miki Cikin, to bari kiji ba yawon fitsari ba, ko yoyon kashi zakiyi sai kin haifesa tunda dan sunna ne ba zina ba, naga alaman kin renani tunda kinga gadon bacci na ba, to mu zuba nidake" sannan ya fice Cikin b'acin rai.

Tunda ya fara balbaleta ta rufe ido jikinta sai rawa yake dan bata tab'a ganin b'acin ransa kamar haka ba, iya sanin ta dashi, duk'ewa tayi k'asa tana rusar kuka lallai wannan shine a dakeka a hanaka kuka, kukanta ya tayar da junior shima ya tashi yana tayata.

A dole ta daina kukan ta d'auke sa tare dayi mishi wanka, shiryashi tayi itama ta shirya sannan ta wuce parlour dashi dan bashi abinci amma duk ranta a jagule yake tama rasa wane tunani zatayi, anan taci karo da Nihal ta dawo tare dasu Husna da driver ya d'auko daga school.

"Sisto kin tashi ya k'arfin jikin, wai meke damunki ne?" Ta jero mata tambayoyin same time, yake kawai tayi mata "uhm Malaria ce fa, na samu sauk'i sosai" sannan ta sauke junior ta rungume su Husna dake mata sannu tana tambayan su school.

"Allah k'ara sauk'i sis, barin shiga na fito" Nihal tace tana shigewa ciki.

"Ok" tace tare da shigewa kitchen...

Safa da marwa kawai yake tsakiyar d'akin, ransa a b'ace "lallai yarinyar nan ta gama renani at all, ni zata gayawa zata zubarmin da gudan jinjna? Lallai dole na jingine sonta a gefe na koyamata hankali, dan naga kanta na rawa, Amma zanyi maganin abin"........





*****************




Gaba d'aya ya watsar da lamarin Ramlah gefe, duk da yanda ruhi, zuciya gangar jiki suke son kasanewa da ita, a ganinsa hakan zaisa ta shiga taitayinta, bai cika zama gida ba yanzu inya fita tun safe sai dare kuma, yafi maida hankali akan gyaran gidan kamar yadda Mami ta umurcesa, duk da ba wani gyara ne sosai ba, amma kullum yana gurin ana k'alk'ale-k'alk'ale kunsan Drs komai nasu unique ne, yau ma office d'in Hakeem yaje tare da damunsa ya tashi ya rakasa ya dubo aikin da ya bayar ayi masa.

" wai kam wannan gyaran gidan na meye ne? Naga dai tare zakuyi tariyar nan da bikinmu gaba d'aya, kuma still have time"

Dariya yayi "naka wasa, ada kenan, aini a satinnan zamu tare"

"Bansan da wannan ba, kode ka k'asa jurewa ne da jiran 'yar renon taka zakayi mata k'anwa" Hakeem ya fad'a cike da zolaya.

" 'yar reno ai ta dawo Uwar reno kuma yanzu, saidai kace Maman Unborn " ya bashi amsa Cikin seriousness.

Cikin mamaki Hakeem ya kallesa, ganin iya gaskiyarsa ne yasa yakai masa duka yana dariya "amma dai wallahi bakayi ba, yanzu saida ka lalube yarinyar nan ka lallab'a kayi mata ciki, amma dai anji kunya".

" dalla matsa can mutum da matarsa zakace naji kunya, ni kaga tashi muje ayi a gama gyaran nan dan nafison ta tare da wuri kasan eh..yane..eh" ya fad'a yana dariya tare da kanne ido daya.

"Kai kam Allah shiryamin kawai zance, yaro dakai sai jarabar tsiya" Hakeem ya fad'a yana hararansa tare da mik'ewa suka fice.

B'angaren Mami sai shirye-shirye take, kullum bata nan bata can anata hada-hada, ta kira ta gayama su Inna maganar tariyar haka Ard'o ma ta kirasa, saidai yace bazai samu zuwa ba, zaidai aiko da sak'o, har gidan Zainab ta kira kuma sun ce zasuzo ai an zama d'aya, wata 'yar sakkwato Mami ta d'auko take gyara Ramlah ciki da waje tasan yanayin d'an nata saida gyara.

Ita dai Ramlah batasan ma'anar gyaran ba, sai ta d'auka ko don tana da ciki ake mata gyaran, to amma saboda me bata da Amsa dole ta kama bakinta, itama Nihal da batasan wainar da ake toyawa ba danko labarin Cikin bata bale tasan na tariya data tambayi Ramlah cewa tayi itama bata sani ba wlh, bata hak'ura ba ta tambayi Mami, harara ta rakata da ita tace meye nata inta sani dole ta kama kanta.

Sai a bakin Hakeem takejin komai aiko jiki na rawa ta fesawa Sadee M bash, da sauran k'awayensu na jiki, nan suka had'u sukazo suka yima Ramlah caaa da masifa da tsiya irin ta 'yan mate, hadda fad'in ashe taje garin....shine bata gayamusu ba, to ta basu labarin ya abin yake..

Banza tayi dasu ita abinda ya dameta ya isheta ga Mami tace ta shirya k'arshen sati zata tare, tasan tata tazo k'arshe idan ta shiga hannun yayan nata, gashi ta daina ganinsa ya daina shiga sabgarta, alaman fushi yake da ita saboda yasan ya gama da ita shida laifi shida mata fushi.




************





Gidan Mami ya cika da jama'a da yake ita mutuniyar mutane ce, kamar wani biki ake ba tariya ba, Maman Zee ma ta iso da kanwarta Amal da yake itama tayi graduation itama tare dasu Ramlah, sun ji dad'in ganin junior Cikin kulawa kowa nan nan yake dashi musamman Ramlah Wanda hakan ke nuna musu baya cikin tsangwama, Inna 'yar tsohuwa ma sunzo ita da matar Uncle Mansur, sai tsiya takema ma Ramlah wai Amarya zata tare da d'an kunshi sudai kam anyi mara kunyan yara, Abdool ma tayi masa, amma shikam saidai ya bata amsa yace su ai 'yan zamani ne ba irinsu ba k'auyawa.

Ard'o ya aiko tsumi da sauran kayan gyaran amare yace zaizo daga baya in an kwana biyu yaga gidansu, ranar Asabar aka gudanar da walima anan gidan Mami inda su Nihal da M bash suka taka rawar gani, anyi rabon kayayyaki Wanda duk sune suka d'auki nauyin yi hadda Amal, Amarsu ansha kyau, gyara tasha har ta gaji, ansha Kitso da kunshi Wanda duk akan dole tayi su dan itakam a firgice take, lafewa kawai tayi tana yak'e, da daddare bayan tasha nasiha sosai daga iyayen nata, sai kuka take dak'ar aka rabasu da Junior ta dage tare zasuje saida Mami ta amsheshi Wanda shima sai kukan yake yana kiran "Maa" Inna, da Sauran k'awayen Mami ne matar Uncle Mansur sai su Nihal sukayi rakiyar amarya zuwa tamfatsetsen gidanta dake unguwar Dosa, fad'in kyawun gidan ma bannan lokaci ne, just guest friends. Lol.

Su Nihal sai zagawa gidan suke suna ta santinsa, daga nan suka tsere, dama su Inna sun dad'e da wucewa, Nihal tana

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login