Showing 6001 words to 9000 words out of 88300 words

Chapter 3 - ABDULMAJEED BOOK by Meryam Abdul.doc

09 Oct 2025

1608

addu'a take duk Wanda tazo bakinta nah nemama Kakan nata lafeeya, Malam Garba safa da marwa kawai yakeyi yana jiran tsammani tare da tausayawa aminin nasa, dan ciwon bai tab'a taso masa irin hakaba zuwa d'aya, saidai fatan samun lafia yake masa.

Taimakon gaggawa suka fara bashi ta hanyar saka masa oxygen, nurse Zainab ce ta fito, sanye da uniform irin na nurse, domin kiran Dr, Abdool saboda baya nan yaje gida yanzun, gashi ta kira wayarsa yana busy, da sauri ta fita, ganin ta yasa suka taso suna tambayarta jikinsa "da sauki" kawai tace ta fita.

Knocking tayi "yes" aka bata Umurnin shigowa, flat ne gidan mai one sitting room and 2bed room sai kitchen, irin dai na quarters d'innan, kwance yake kan 3seat idon sa lumshe yana waya, kan 1seat ta zauna tana k'arema gidan kallo dan shine first time d'inta shiga, komai neat sai k'amshi ke tashi kamar gidan mace.

"Hmm haba Hakeem duk matan da na gani ABU basu dama min lissafi ba, sai wannan 'yar fillon? Never."

Banji me Hakeem yace ba, murmushi yayi "any way yanzu inada bak'uwa, amma zan shigo end of week inshaa Allah".

'Yar dariya yayi tare da cewa "shegen kaya" sannan ya katse wayar.

"Yadai Zainab" ya fad'a ba tare daya bud'e idon ba.

Zainab da tunda taji ya ambaci 'yar fillo, k'irjinta yai mummuman bugawa sai zafi yake Mata.

Zainab itama Attachment takeyi daga Sokoto tazo, tunda taga Dr Majeed haka suke kiransa, taji ba Wanda takeso duk duniya kamarsa, tun daga lokacin take shige masa muddin yana hospital to tana tare dashi tanada kyau sosai itama siririyace mai matsakaicin tsayi kalar fatar tah bak'a CE amma irin mai kyallin nan.

Tayi mamakin yadda ya kira sunanta bah tareda yaga waye ba, kodai shima yana sonta neh? Waye zai ansamata wannan tambayan? Abun ko ba haka bane normally idan Abdool yaji muryanka sau biyu to yana noticing idan ya k'ara jinta.

Jin shiru nad'an mintuna ya sakashi mik'ewa zaune tare da ware manyan idonsa a Kanta.

Karaf ya idonta cikin nasa, cikin rawan murya tace "Sir we have a patient right now, he is in a very critical condition".

" OK am coming " kawai ya fad'a.

Mik'ewa tayi ta fice, binta yai da kallon "ko miye damuwarta oho!" Ya d'aga kafad'ar sah tare da tab'e baki.....




Sosai ya tausayawa tsohon dan yana jin jiki sosai, kusan 30mnt yayi a kansa kafin yayi nasarar daidaituwar numfashinsa, allurar jijiya yayi masa sannan yasa aka maidashi d'akin Hutu.

Fitowa yayi yana cire hand glove tare da Handkerchief ya fito dashi yana share zufa, dai2 lokacin Malam Garba ya iso inda yake "dofto ya ake ciki ya mai jikin"?

Murmushi yayi masa " kwantar da hankalinka Baba, ya samu sauki yanzu yana d'akin hutu muje muyi sallah koh"....

Laure data shige duniyar tunani bata masan Malam Garba ya tashi ba sai dubawa tayi bata ganshi ba d'agowa tayi ganin shi da Dr suna magana saidai bayansa kawai take gani, tashi tayi zuwa inda Suke.

Kaman ance ya juyo sukayi four eye cikin mamaki yace "you again"? Itakam tsoracewa tayi ganinsa, ita tama manta dashi.

Sunkuye kai tayi ba tare datace komai ba don batasan meyace ba, ganin idonta jajir alaman tasha kuka " me kikeyi anan."

Malam Garba ne yace "kasantane dofta"?

" eh to na tab'a ganinta anan garin tazo saida nono harma nasiya toh shine nake mamaki."

"Ayyo! Ai kakanta neh baida lahiya."

K'ara kallonta yayi cikin ransa yace "dalilin kukan kenan"? A fili yace "OK, amma meyasa kuka taho da ita Baba"?

" wallahi d'anga an rud'e ne, ni bammasan ta shigo ba."

Wayarsa ya d'auko yayi kira " Zainab d'anzo reception zakiyimin wani aiki" ya fad'a tare da tsinke wayar.

Minti kad'an sai gata tazo "kije da yarinyar nan gidanku pls" kallonta tayi sannan tace "muje ko" tana mata murmushi.

Binta tayi sannan ta shima Abdool suka fita jin an fara kiran isha'i, bayan sun fito gida yaje ya d'akko bargo da filo ya kawoma Malam Garba sannan yaje yayi round ya wuce gida, har yanzu Ardo bai farka ba, saboda hadda alluran bacci a ciki.

Tana zaune k'asa sai raba ido take, Zainab ce ta fito daga kitchen abinci ta aje mata tare da ruwa da drink, "ya sunanki ta tambayeta"?

" Ramlah " ta fad'a a takaice.

"Wow nice name."

Itakam name kawai ta gane, da yake tadanyi makaranta zuwa primary four Iya Hari ta fidda ita.

Murmushi yake tayi mata, "ciki abinci sai kizo kiyi sallah" Zainab ta fad'a tare da shiga bedroom d'in ta, da yake gidan su 2 ne dashi tare da wata Christan.

Aiko tana shigewa Laure ta kama cin abinci hannu baka, sai dadi ke ratsa mata k'wak'walwa tana jinjina ma 'yan birni akan cin dad'i.

Cikin minti biyar ta gama dashi tsaf, cikin kayan gida Zainab ta fito ganin plate kawai tayi, smiling tayi sannan ta d'auke takai kitchen, kunyace ta kama Laure, amma saita share kada ta Renata(hoho su Laure aja girma) lol.

"Muje kiyi sallah" dakin tsaf2 ba wani tarkace gado ne sai wardrobe, toilet ta nuna mata "ruwa nanan a bocket kiyi wanka akwai ruwa a bota na alwala" nagode " ta fad'a tare da shigewa.

Girgiza kai Zainab tayi tare da cewa "kodai itace 'yar fillon"? Tab'e baki tayi tare da fitar mata da kaya, sannan ta shimfida mata dadduma.



^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^




*A k'auye...*


Iya Hari jin shiru har bayan isha ba Malam ba Laure yasa hankalinta yad'an d'aga, fita tayi ganin ba kowa yasa ta koma gida rikice ta d'auki mayafi, a waje taga wani yaro ta tambayesa nan yake shaida mata yagansu bakin asibiti an sakashi mota a mace.

K'ara rudewa tayi ta rasa inda zata saka Kanta, 'ya'yanta ta aikawa Lanti da Shatu, suma tuni suka iso a firgice.........




_love u friends_ d'.





=؄?Meryerm Abdool =؄?
[7/13, 10:01 AM] =؄?Meryerm Abdool=؄?: =ؤ? ```ABDULMAJEED``` =ؤ?

(' *Servant of Majesty* ('



Na
=؄? _Meryerm Abdool_ =؄?


? *Pure moment of life writers*
P.M.L=ت?




```Manzon Allah (S.A.W) yana cewa:-```


_Baya shiga aljannah, maiyin annamimanci._


*Annamimanci yana nufin munafurci, munafurci yana nufin kayi maganan mutum koda abinda ka fada gaske ne abayan idonsa, Wanda ya kasance tozarci ne garesa.*

*a wannan zamanin da muke ciki abin ya zama ruwan dare saidai fatan Allah ya kawo mana sauki, ni dake dasu, muyi k'ok'ari mu duba yadda muke tafiyar da rayuwarmu ta yau da kullum shin mun kiyaye harshenmu ko kuwa Aa.*

Allah yasa mudace=?O?



_Where r u? Rukie gwando, mlm ubaida, mino, qwlly, Maman Ramlah, Maman Nana, Sarat, Maman xee, sisto shafcy Abdool, oh kuyi hak'uri wadanda ban kira ba, mu had'u wani jik'on. ILYVM FROM D BUTTON OF MYd'_








=??? *Episode* 36--40



Suma rud'ewa sukayi ganin halinda mahaifiyarsu take ciki, barin ma Lanti taji, Shatu CE ta tambayeta cikin nutsuwa, nan ta gayamusu abinda wannan yaron ya fad'a mata, asibitin garin sukaje suka tambayi inda akaje dashi nan sukai musu bayani, gida suka dawo suka fad'a mata sannan sukai mata sallama da niyyan gobe suyi asubanci.

Iya Hari sai k'ara tsinewa Laure take a nata ganin mugunta tayi Mata tak'i gayamata (oh wannan tsohuwa sai Allah).


B'angaren Abdool kuwa zuwa ten ya k'ara komawa asibiti koda yaje ya samu Ardo ya farka, nurse na cire mishi ruwan da aka saka mishi Malam Garba na gefensa ya d'aga mai filo ya jingina dashi, murmushi yayi tare da cewa.

"Sannu Baba jiki yayi kyau" lokaci d'aya Ardo yaji yaron ya kwanta mishi a ransa, Sam baida alaman wulak'anci ko d'aga kai irin Wanda wasu likitoci keyi (ai ba duka aka zama d'aya ba).


"Alhamdulilah naji sauk'i sosai docta, gashi numfashina ya daidaita, saidai k'arfin jikinne ya rage."

"Ayya shima zuwa gobe zakaji ka dawo normal" ya fad'a yana d'an dubashi, maganinda ya siyomai ya basu tare dayi musu saida safe, sauran ward d'in ya shiga ya dudduba patients.

Wani massenger asibitin ne ya kawo mishi wata leader "gashi Sir an samo dak'yar" ansa yayi sannan ya d'aga mishi hannu "well done zaka iya tafiya" ya fad'a tare da wucewa, gidansu Zainab yaje kiranta a waya yayi.

Tana zaune tana duba wani littafin biology, Laure na gefe a k'asa bacci yayi gaba da ita, ba yadda Zainab batayi da ita ba, akan tahau kan seat tace k'asa ya isa, ita batamasan tayi bacci ba, dan atunaninta kallon da ta saka mata takeyi.

Wayarta ce tashiga Neman agaji "Dr Majeed" tace d'an mamaki a fuskarta, sai kuma tai smiling mai k'ayartarwa kamar tana gabanshi sannan ta d'aga.

"OK" kawai ta fad'a, tare da zura hijab d'in sallarta sai k'asa, dayake kayan bacci ne a jikinta, tana mamakin da Daren nan ya taho gidansu, smiling ta k'ara yi, gefen Laure ta kalla taga bacci yayi gaba da ita "sllly girl" ta fad'a sannan ta fice.

Yana jingine da motarsa ya rungume hannuwansa a k'irji, sanye da blue jean da shirt red ya d'ora lab court a sama, as usual glass dinsa na mak'ale a idonsa, duk kafin ta k'araso ta k'are masa kallo, itadai wannan gayen na tafiya da ita ba kad'an ba.

Sallama tayi masa ya ansa bayan sun gaisa ya Ciro Leda a mota ta bata "gashi ki bama yarinyar nan, dan naga da alama kayan jikinta ne kawai tazo dasu".

Ansa tayi tare da cewa "ai dama baka siyo ba dan nama bata wasu dana d'inka ban riga na saka ba, amma duk cikin k'ari ne an gode."

"Nine da godiya Zainab, thanks once again"

Murmushi tayi "wannan k'anwar taka akwaita da kunya, sam bata magana" (bugun ciki taji ya Suke).

Shima smiling yayi "zan tafi saida safe" ya shiga motarsa...

"Tau gudnyt Sir" ta fad'a tare da wucewa ciki cikin farinciki, tada Laure tayi takaita d'aki "da sannu zanyi nasara ishaa Allah (tunda kikace Allah kin gama komai Zee).



?!?!?!?!?!?!?!?!?!?!?!?!



Laure asuban fari ta tashi saboda sabo, kan gado ta ganta, sauka tayi a gefen gado taga Zainab kan dadduma, murmushi tayi mata " kin tashi cute Ramlah" itama murmushin tayi mata ba tare datayi magana ba.

"Je kiyi alwala kiyi sallah inaga time dinma yayi" girgiza mata kai tayi tare da murd'a k'ofan "am akwai brush a gefe mirror da MacLean sai kiyi" nanma kai ta d'aga mata dan bata fahimci me take nufi ba tadai ansa kawai.

Zuwa 8 Zainab ta shirya cikin uniform bayan sun gama breakfast itama Naomi fitowarta kenan "Sainab kayi bakone" yes Naome she's my sister ".

" wow so beautiful like u" dariya tace "as said always and u are beautiful too".

" ha ah Sainab don't said that again, see me se troubIe, Hmm look like fate-fate"

Dariya sosai Zainab tayi hadda kama ciki, Laure sai kallonsu take tana inama tanajin me suke cewa abin ya birgeta duk da bataji.

"U are too funny Nao, oya let go time is going".

" Hah! na true shaa"


Kallon Laure Zainab tayi "Ramlah zamu tafi asibiti, zan dawo naje dake idan Dr yai magana" narai-narai tayi da ido cikin sanyi tace "zan biku inga baffa".

D'an tunani tayi kada taje da ita kuma Dr baice ba, can dai ta koma d'aki, fitowa tayi tare da kayan Ramlah da wadanda Dr ya kawo mata da NATA wad'anda tazo dasu, da wadanda ta cire jiya " kinga wad'anda yayanki ya kawo maki" tana nuna mata kayan da Abdool ya kawo mata.

"Yayana"? ta fad'a cikin mamaki, " eh doctor da ya had'ani dake koba yayanki bane"?

Kad'a mata kai tayi alaman eh, "well to muje, aranta tace " koma ke meye tasa a sanadinki nad'an samu kusanci da Dr, hmm inasonka Dr Majeed" tai smiling mai tashi tare da lumshe ido....


Suna shiga ward d'in da Ardo yake da gudu ta isa garesa tare da rungumesa, yana zaune wani messenger ya kawo kayan breakfast da Abdool ya aiko ya kawo musu Malam Garba ya had'a mishi shayi yana sha, ajewa yayi tare da Shafa Kanta.

"Ramlatuna Ashe dake akazo, kinga wannan Dr mai karamci da mutunta mutane ko"?

Kai ta girgiza alaman eh " Baffa ya jikinka" na samu sauki Ramlatu ba in kemin ciwo yanzu".

"Allah ya k'ara sauki Baffana" nan malam Garba yayi ta tsokanarta ga Ardo nan bai tafi ya barta ba, haka tai ta cewa jiya tana kuka, fuskarta ta rufe tana murmushi dai2 nan su Zainab suka iso suka duba jikinsa sannan suka wuce suna mishi fatan samun sauki.

Nan Ramlah ta gayamai Alkhairin da tayi mata aiko kiransu yasa tayi yana ta kwararo musu addu'a da sanya Albarka "ba komai Baba yiwa Kaine" ta fad'a tana murmushi don taji dad'in addu'ar.....

Kusan 10 su Iya Hari suka iso Yabo, basu sha wahala ba gurin gane ward d'insu, suna isa Iya Hari sai masifa tahau Laure dashi ba tambayan Ardo jiki ba komai, sai ruwan bala'i hadda fad'in da mijinta ya mutu da sai tayi k'ararta (jimin k'arfin hali).


Ardo kam kwantawa kawai yayi ya rufe ido, yanajin zafi har cikin zuciyarta, wannan wace irin musiba ace ko gaidashi batayi ba ta hau masifa akan rashin dalili, a bak'on wuri ma ba zata rage ba, kai Allah wadai da hali irin na Hari.

Itama Shatu tunda ta gaida mahaifinta da jiki, ta koma gefe tayi tagumi, ta tsani irin halin mahaifiyarta, musamman yadda take nuna tsana akan 'yar d'an uwanta saboda dalilinta mara tushe, Lanti murna take dan halinsu d'aya da uwar shiyasa tafi k'aunarta.

"Kedai Laure anyi muguwa mai bak'ar aniya jikar mayyu" Kanta sunkuye ranta sai suya yake, malam Garba sai tausar Hari yake amma kamar zugata yake.

Karaf a kunnen Abdool Wanda fitowarsa kenan, maimata maganar yayi "muguwa mai bak'ar Aniya, jikar mayu, wacce ce haka...."?.........






_love u friends_ =?
?








=؄? Meryerm Abdool=؄?
[7/16, 10:50 AM] =؄?Meryerm Abdool=؄?: =ؤ? ```ABDULMAJEED``` =ؤ?

(' *Servant of Majesty* ('



Na
=؄? _Meryerm Abdool_ =؄?


? *Pure moment of life writers*
P.M.L=ت?



```Annabi Muhammad (S.A.W) Yana cewa:-```


_Mafi sharrin mutane mai mummunan masauki a gurin Allah (ranar alk'iyama) shine wanda mutane suka guje masa saboda alfasharsa_ (hakkun mubeen.)

*nida ke dasu, ya kamata musan me muke furtawa, me muke aikata saboda mu tsira a ranar gobe k'iyama.*

Allah yasa mudace =?O?



=??? *Episode* 41--45


Kansa ya danna cikin d'akin, da kallon wannan fa yabi Iya Hari dashi, ganin sai masifa take zubawa ita kad'ai, ga Laure kanta duke da alama ita ake mawa.

"To meye had'inta da ita, me tayi mata" ya tambayi Kansa a zuciyarsa.

Malam Garba ne ya kula da tsayuwarsa saboda kowa hankalinsa baya gun "Dr sannu da fitowa" ya fad'a.

Jin hakane yasa Ardo bude idonsa, a dai2 lokacin itama Laure ta d'ago nata idon kan nasa ta sauke dama ita yake kallo, ganin yadda fararen idanunta sukayi ja ranta a dagule.

Gyaran murya yayi sai lokacin Iya Hari tasan da zuwansa, d'an kame-kame ta farayi dan ba k'aramin kwarjini yayi mata ba tare dayin shiru.

"Haba Inna meye, haka a asibiti kike fa? Marar lafiya baya buk'atar damuwa, pls kud'an fita daga waje".

Jiki sanyaye suka fice aka barshi daga shi sai Ardo " kayi hank'uri don Allah docta, kasan mata sai a hankali" murmushi yayi masa.

"Ba komai Baba dama dan lafiyarka ne, ya kakejin yanayin jikinka yanzu"?

"Madallah jiki inajinshi dai2 babu inda kaimin ciyyo yanzu".

D'an duddubashi yayi kujera yaja ya zauna sannan yace "yanzu komai ya dawo normal saidai kana buk'atar rage tunane-tunane saboda bayan asthma har hypertension kanada (baiyi mamaki ba saboda jarabar Hari kad'ai ta isheshi) kuma yawan saka damuwa a zuciya ba naka bane pls ka kiyaye Baba kodan lafiyarka" ledar magani ya bashi.

"Ga wannan kayi amfani dashi" sannan yayi mishi bayanin yadda zaiyi amfani dasu.

"Yanzu zanyi discharge naku, zaku iya tafiya" ya fad'a tare da mik'ewa "Allah ya bida lafeeya.

" d'an nan to nawane kudin maganin"?

"Aa Baba ka barshi Allah dai ya baka lafia" godiya sosai Ardo ke kwarara masa yana jinsa kamar d'ansa "dama akwai sauran irin wad'annan mutanen Ashe" ya fad'a a ransa.

"Ba komai Baba, nima nagode da addu'arka Bari inyi magana dasu, yanaso ya tambayesa game da Laure da alak'arsu saidai yana ganin rashin dacewar haka toya zaiyi?.

Can wani tunani yazo mishi, smiling yayi tare da ficewa.



""""""""""""""""""""




"To shi kuma wanga wanena? Yaka korarmu iyii"?

Malam Garba yace " dofto na, mai kula da Ardo".

Zata k'ara magana sai gashi ya fito da kallo ya bita Wanda yake na raini, yawu ta had'iye, gefen Laure ya kalla ta rabe Kanta cikin cinyar ta, girgiza kai yayi alaman tausayi.

Shatu dariyace ta k'onota saidai ba damar yi ganin yadda uwarta ke raba ido alaman tsoro, dan Hari akwai masifa amma tsoro kamar farar kura, haka take tsoron Jauro kamar ranta.

"Dofto ya ake ciki"?Malam Garba ya tambayesa.

" zaku iya tafiya sai a kiyaye b'ata masa rai, sannan a ringa kula da shan maganin pls Ku kiyaye".

"Inshaa Allahu dakata" Iya Hari ta fad'a don Neman sulhu.

"Madallah dofto za'a kiyaye inshaa Allah, mungode da hidima fa, takardar magani fa? Wanda za'a siya".

" no ku barshi kawai na kai masa maganin, adai kula sosai".

"Kai madallah mun gode sosai Allah yayi Albarka, Bari intai in samo mota, Ku kutai ku kimtsa" yace dasu Shatu.

"Ameen, amma indai wannan Ku had'a kayanku zan kaiku, sai kumin magana idan kun shirya" ya fad'a tare da wucewa.

Da Zainab ya had'u yana daf da shiga office "morning Sir".

" morning Zainab, am kiyima Dr bakori magana yayi replaced d'ina zan fitane".

"OK Sir".

" koda maganan?" ganin ta mishi tsaye ta kashesa da ido.

"No" ta fad'a tare da wucewa, girgiza kai yayi tare da smiling ya Shafa sumarsa "ciwon mu iri d'aya ne, son maso wani" ya fad'a tare da shigewa office d'insa..........

Har k'ofar gida ya kaisu, wannan karon harda su Iya Hari sai godiya ake zubawa (su iya ansha A/c) lol.

Fura zallah Ardo yasa aka damo masa wacce tasha kindirmu damun kyale mod'a(ba'a saka ruwa a ciki) yaji dad'in hakan sosai dan dama Abdool ma'aboci shan furane da nono, nan waje suka zauna da Ardo suna d'an fira, yara kuwa sun zagaye mota sai shafata Suke sunga irin wacce basu saba gani ba, mata kuwa sai lek'e Suke ta Katanga, mutane sai kwararowa suke gaida Ardo da jiki.

Har ya shiga mota zai tafi sai ga Laure ta fito, nono ne da kwan zabi tace Ardo ya bata, tsayawa tayi ta k'asa magana Kanta k'asa, kallo ya k'are mata tsaf komai nata mai kyaune yanzun ma da take yarinya to inaga ta girma Hmmm.

Ganin tak'i magana ga lokaci na tafiya yasa yace "yadai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login