Showing 24001 words to 27000 words out of 88300 words

Chapter 9 - ABDULMAJEED BOOK by Meryam Abdul.doc

09 Oct 2025

1588

yafi ba, lafiya a jikinsa, Hajia ce tayi k'arfin halin cewa "Alhaji ka bari kaci abinci ka huta tukunna sai ayi maka bayanin komai" jiki a sanyaye tayi maganar.

Ba shida zabi hakan akayi bayan yaci ya huta haka ta kora masa bayanin komai daya faru, har zuwa tafiyar Auwal, shiru yayi nad'an lokaci kafin ya dago idonsa da suka rine sukayi ja ya nuna Hajia da yatsa.

"Ke bani mamaki kaltume duk da babu mamaki in ankai la'akari da rashin son da kike nunama Ameena, tau burinki ya cika Ameena tabar miki gida Auwal ma ya bita yanzu sai kije ki zauna da wad'anda kikeso" ta bud'e baki zatayi magana, ya dakatar da ita "bannson jin komai daga gareki tashi ki tafi" ya fad'a yana nuna mata k'ofa dama daga ita sai shine a d'akin, tashi tayi ta fice jiki ba k'wari, dan tasan hak'uri irin na Alhaji duk yakai gayin fad'a to an kureshi ne, amma ai bai kamata yaga laifinta ba, komai ya faru au Ameena ce sila, itakam wannan shine adakeka a hanaka kuka.

Alhaji sai safa da marwa yakeyi ransa a jagule, tabbas Auwal bai kyauta ba, koma meye ya faru bai kamata yabar gida, duk da iya cuta an Riga an cucesa, dan wannan dagaji sharri ne akayi mata, dan yasan Ameena ba zata tab'a aikata wannan danyen aikin ba, kuma yasan Hajia nada tsananin zafi da ak'ida Mara tushe da asali, amma yasan ba zata aikatawa Ameena wannan aikin ba, to abin tambaya anan waye ya aikata? Babu ansa "Allah ya sawwaka" ya fad'a a fili, dama iya zaman da Allah ya d'ibar musu kenan, koda wannan koba sa wannan ba tabbas sai sun rabu dai2 wannan lokacin

Bud'e wardrobe yayi dan d'aukar Abu kawai sai Leda ta
Fad'o takardune na bud'e account da komai daya k'unsa sai diary da wasik'u guda biyu, bud'e d'ayar yayi yaga ansa *zuwa ga Ameena* rufewa yayi ya bud'e d'ayar Wanda ta kasance tashi ce.

Shima dai ban hak'urin ne da Neman gafara, sai Amanar *Abdulmajeed* daya d'anka masa da kuma bayanin diary da information na Account ya aje hannunsa har sai Abdool ya mallaki hankalinsa ya mallaka masa, sai wasik'a da yake rokon ya bayar a kaiwa Ameena, bayan ya gama karantawa yace "na yafeka Auwal duk da baka kyauta min a matsayina na mahaifi ba, wannan dalilin bai isa yada ka tafi ba, amma ba komai Allah ya tsareka a duk inda kaje ya kuma dawo mana dakai lafia wuri kusa kazo ka kula da d'anka da kanka".......

B'angaren Ameena kuwa kokai waye idan ka ganta dole ka tausaya mata, ta fita hayyacinta gaba d'aya tayi bak'i ta rame sosai kullum cikin kuka take musamman ganin an kwaso kayanta, yanzu shikenan ta zama bazawara, abin tafi tsana a rayuwarta ada sai takega duk matar da ta zama bazawara a dalilin saki to laifinta ne, ita tayi abinda yasa aka saketa, amma a yanzu ta gane ba haka abin yake k'addara wacce bata wuce fata, ta gane Ashe ba matar da ke son a saketa koda kuwa ita tayi laifi, balle irin su da basuji basu gani(to in banda Ameena wake so yayi aure yau gobe ace ya dawo gidansu ai saida k'addara wacce ba'a fata Allah ya kyauta).

Ga Abdool kullum kukan Dadynsa yakeyi Abu duk ya had'e yayi mata yawa, danma ga Asma'u kusa ita ke d'auke masa kewar Dadynsa, Mama da Baba kullum cikin kwantar mata da hankali suke, Mansur kullum yana cikin kawo Abdool kayan wasa da kayan kwalama irin na yara idan yaje School 'yan Kud'insa duk can suke tafiya duk dan su kwantar Mata da hankali, Firdausi ma tazo lokacin da taji, itama Sam abin baiyi Mata dad'i, musamman ma sharrin yafi komai cin rai, inda Allah ya sota duk Wanda yaji kai tsaye yake k'aryatawa, saboda sanin halin kirkinta(tau zama dan kwarai Nada rana dan wata rana ake gujewa mu d'aure mu k'are mutuncinmu).

Alhaji washe gari yazo Argungu, Baba ya tarbesa kamar ba abinda ya faru dan yasan ba laifinsa bane, hak'uri ya k'ara bashi akan abinda ya faru, tare da tabbatar masa Sam koda abin ya faru bashi gari, saida ya dawo yakeji nan yake gayamai tafiyar Auwal, nan Baba ya jajantamai tare da fatar Allah ya bayyana shi, tsaraba Ameena da Abdool ya fito dasu hadda ma Asma'u yayima dan yasan tana gidan lokacin da ya tafi, tare da kayan buk'atar Ameena da Abdool na yau da kullum, dan yayi Alkawarin kula dasu har sai tayi Aure.

Baba saida Alhaji ya nuna b'acin ransa tukun ya anshi kayan dan yace bazai Ansa ba, saida Alhaji yace bai hak'ura da abin da yw faru ba kenan, ai sun Riga sun zama d'aya tunda har rabo ya shiga tsakani, hakan dai dole ya ansa, har Mama saida ta fito suka gaisa sannan ya bata hak'uri itama.

Lokacin da Ameena tazo nasiha sosai yayi mata tare da bata hak'uri sannan ya tabbatar mata har yanzu shi ubane gareta komai ya sameta ta sanar da shi, kud'i ya bata tare da wasik'ar Auwal, saida yayi mata fad'a sannan ta Ansa, haka ya tafi yana tausayawa mata dan bazaiso hakan ra faru akan Maryam ba.

Sosai ya k'ara daraja da girma akan idon Ameena da iyayenta.

Sai dare ta d'auko wasik'ar Auwal da tunda aka bata ta kaita ta ajiye, dan ita yanzu lamarin maza ya fita Kanta kuma duk haushi Suke bata(dama ai duk macen da aka saka tofa duk maza haushi zasu rik'a bata zata d'auka duk Wanda ta aura zai iya sakinta komai soyayyar da yake mata kuwa.

Bud'ewa tayi ta fara karantawa..

_"gareki masoyiyata tahar abada, Ameena nasan zanyi bak'i a gurin ki dan duk wacce aka saka saki uku kai tsaye tabbas zata girgiza kuma zata tsani wannan mijin, harga Allah duk da abinda idanuwana suka ganemin, zuciyata ta k'asa yadda da abinda wani barinta ke gayamata akanki, saidai ki sani dole ne na shiga rud'u dan nina gani ba ji nayi ba, amma inaso ki d'auki wannan a matsayin k'addarar muce, ki tausayawamin ki tausayawa d'ana *Abdulmajeed* ki zame masa uwa da uba agareshi ki bashi dukkanin tarbiya ta gari, dan kuwa ke uwace ta gari a gareshi, pls kada kibar rayuwarsa tayi garari koda kinyi aure ne, ki zama majib'incin lamurransa a dai2 gab'ar da ya rasa dukannin kulawata a matsayina na uba agareshi, na tafi bawai dan bana k'aunar sa ba Aa sai dan samun maslaha a gareni, ina miki fatan Alkhairi, ki saka a ranki zan rayu da sonki a kowanne second na rayuwa"._

*naki Auwal Sada*.


Koda ta gama karantawa hawaye sun wanke mata fuska, zuciyarta sai rad'ad'i take mata da suya, Abdool ta rungume tsam a k'irjinta tana tausayawa rayuwarsa, yaro k'arami ko wace rayuwa zaiyi nan gaba.

"Allahumma ajirni fi musiba"..................






*ina mai Baku hak'uri sa babbar murya, akan jina da kukayi shiru kwana biyu, na shiga busy ne, amma Ku sani kuna raina#1d'#*








=؄?Meryerm Abdool=؄?
[8/8, 7:45 PM] =؄?Meryerm Abdool=؄?: =ؤ? ```ABDULMAJEED``` =ؤ?

(' *Servant of Majesty* ('



Na
=؄? _Meryerm Abdool_ =؄?


? *Pure moment of life writers*
P.M.L=ت?
(We don't just entertain and educate we touch the heartd' of the readers=???)




=?L?
Small quote=?L?


_Aunty Khaleesat Haiydar ur r so grateful, Aunty Ummi shatu wishing oll d best in ur exams=?L?






=??? *Episode* 111--115




Saida aka kai ruwa rana kafin Baba ya yadda da komawar Asma'u makaranta, dan yace ta dawo tayi NCE kawai, dak'yar ya amince amma da sharadin zata kare mutuncin Kanta, ranar da zata tafi da kuka suka rabu da Abdool dan lik'e mata yayi sai taje dashi, Mansur ya fita dashi sannan ta samu ta wuce kice da kewar gida da Son d'inta, dan tasan zatayi missing nashi, Hostel ta koma da zama inda ta dage da karatunta baji ba gani, tayi mamakin rashin ganin Maryam sai daga baya takeji ga k'awayensu an canja Mata school, Hajia ce tasa aka canja mata, a cewarta kada Asma'u ta lalata mata d'iya, tunda tasan muddin suna school d'aya Maryam ba fita hanyar Asma'u zatayi ba, hakanan bataso aka maida ita nursing.

B'angare guda kuwa shakuwa ce ta k'ara shiga tsakanin Asma'u da Abdulrahim kullum zaka Kansu tare yana koya mata karatu musamman yanzu data dawo hostel dama shi a hostel yake dan ba dan garin bane, tun basujin komai a ransu game da juna har takai yanzu sunajin zukatansu sunaso su zama d'aya.

( *Tofah wai waye Abdulrahim?*)


Abdulrahim dan asalin kilgori ne wadda ke k'arkashin Yabo local government dake jahar Sokoto, D'ane ga Malam Umar wadda akafi Sani da Ard'o, sarautace irin ta Fulani wato mai gari kenan, Ard'o ya zamo mai garin kilgori ne bayan rasuwar mahaifinsa wato tsohon Ard'o, yana da matar Aure d'aya Hadizatu wacce akafi sani da Iya Hari, auren zumunci ne akayi musu, Ard'o mutum ne na mutane mai sanyin hali, kowa nasane, yayin Iya Hari ta kasance masifaffiyar mace, Mara mutunci kullum cikin masifa take da bala'i, tunda Ard'o ya aureta bai taba k'arda dad'in ta ba, anadai zaune ne zaman hak'uri, bai isa ya sata tayi ba haka bai isa ya hanata ta hanu ba, amma a haka sukaci gaba da zama da yake Allah ya zuba mishi hak'uri, komai tayi kauda kai yake kamar bai gani ba, sunada 'ya'ya uku Abdulrahim ne na d'aya Wanda take kira da Modibbo saboda kasancewarsa d'an fari, sai Lantana wacce ake kira Lanti sai Aisha wacce ake kira Shatu, sam halin Aisha da Abdulrahim ba irin nata bane halin babansu suka d'auko, kai harma kamar dansu farare ne sirara dogeye, kyawawa dasu, yayin da lantana ta biyo kama da halin uwar sak.

Tun Abdulrahim yana k'arami yake sha'awar boko, mahaifinsa kuwa ganin yana sha'awa yasa ya sakashi A yabo dan lokacin ba'ayi anan garinsu ba, haka yake tafiya kullum zuwa yabo don daga k'arshe da mahaifinsa yaga wahalar zatayi yawa sai ya had'ashi da wani malami, yake zama gidansa sai Hutu yake dawowa, Wanda hakan Sam baiyima Iya Hari dad'i ba, rigima ta tada akan ba inda zaiye ya tsaya yayi kiwo in zaiyi, rokonta yayi tayi akan ta barshi, amma tak'i amincewa, dama Abdulrahim baisan dad'in ta ba Sam, dan bata janshi a jiki, wai d'an fari ne, ba wani sabo a tsakaninsu yafi sabawa da Ard'o, haka kuwa ta dage akan ba inda zaije, saida Ard'o ya nuna b'acin ran yaje ya gayama iyayenta, ganin tunda take dashi bai taba nuna Mata bacin ransa haka ba balle har aje ga kai k'ara yasa ta shiga taitayinta ta amince akan dole.

Hakan Abdulrahim yayi ta karatunsa tun daga primary har secondary duk anan Yabo yayi su, gashi kanshi naja(dama Fulani akwai kai) tunda ya fara harya k'are bai tab'a yin na 3 saidai na 1 ko 2 hakan yasa malamansu bawa Ard'o shawarar kaishi university hakan kuwa ta kasance inda yake karatun medicine, ita dai Iya Hari akan dole yake karatun badon son ranta ba, dan ita gani take lalata yara kawai boko keyi, shiyasa ta hana a saka Lanti Shatu, Abdulrahim kuwa ya goge idan ka ganshi bakace dan k'auyen bane, hakan yasa 'yan matan garin kowa sonsa take, 'yar k'anwar Iya Hari ganin kowa sonsa yasa hankalinta ya tashi, ba kunya taje ta gayama Iya Hari itafa shi takeso, dama itama sunada burin hakan itada k'anwarta na had'a su aure, nanta tabbatar mata da Abdulrahim baida matar aure sai ita, shikam Abdulrahim Sam yarinyar bata mishi ba saboda batada nutsuwa Kanta rawa yake, itakam Saude sai d'aga kai take a garin da tak'ama zata auri d'an boko.


_wannan kenan_



B'angaren Ameena kuwa ganin Asma'u ta koma makaranta, Mansur ma ya koma dake boarding school yake, gidan ba dad'i duk da Asma'u na zuwa duk k'arshen sati, yasa tayima Baba magana tanason itama ta koma makaranta bai musa mata ba, saidai yake ba zataje nursing kamar yadda ta buk'ata ba, dan ko lokacin da Auwal ya kawo mata form abinta ta cike kenan, wannan burinta ne tun suna secondary, amma dole ta hak'ura da ita dan dalilan da Baba ya gayamata na hanata zuwa wani gari kara2, ya gayamata 'yan uwansa zaginsa zasuyi suce a maimakon yayi mata Aure ya turata karuwanci, hakan yasa ta hak'ura zatayi NCE anan *Adamu Augie college of Education Argungu* da kanshi ya anso mata form ta cike inda aka bata Agric/education, nan Baba ya sakata gaba yayi mata nasiha akan taci gaba da tsare mutuncinta tayi abinda ya kaita kawai banda bin k'awaye barkatai, itama Mama tayi tata, nan Ameena ta fara zuwa school cikin nasara, ba abinda takeyi sai kara2 ba ruwanta da kowa haka zatayi shigarta ta kamala taje data gama lec, ba wani tsaye-tsaye direct gida take wucewa dama can daga gida sai makaranta, sai kuma bikin yan uwa ko barka shima akan tilas take zuwa kada ta yanke zumunci, saidai abinda ke kona mata rai data had'u da taubasanta yanzu zasu fara takanarta da kiranta bazawara ina zawarawanta, yake kawai take musu amma Kalmar ba k'aramin k'onata takeyi ba, saidai ba yadda zatayi k'addara ta riga fata, shisa sam bata cika son shiga mutane ba.

Zuwa yanzu ta kwantar da hankalinta ta maida kamarta ta kuma rungume k'addarar ta, saidai Aure ya fita ranta gaba d'aya, shiyasa duk Wanda yazo da sunan yana sonta hak'uri kawai take bashi dan bataji zatayi aure yanzu.

Lokaci zuwa lokaci takan tuna Auwal da rayuwarsu ta baya, koyana ina yanzu oho!, Abdool zuwa yanzu ya manta da Dadynsa yayinda ya d'auki Baba a matsayin Babansa, yana 1? ta yayesa dan komai ci yake ga kafafu har gudu yake hak'ora ne kawai bai cika ba, bata sha wahala a yayensa ba, dan wani sa'in sauya wuni baisha ba sai dare, tunda ta aka yayesa ya koma hannun Mama can yake baccinsa.

Ta dage sosai da karatunta k'awa d'aya tayi mai suna Sakina mungadi, department d'insu d'aya, tasu ce tazo d'aya shiyasa sukayi k'awance dan itama sakina ba ruwanta da sha'anin kowa abinda ya kaita kawai takeyi(a kowanne lokaci muyi k'ok'ari muyi mu'amala da mutanen kwarai, dan kuwa har lahira kana tare da abinda kakeso, kuma zama da mad'auki kanwa shika haddasa farin kai) a hostel take zaune dan a bk suke zaune da iyayenta, kullum suna tare idan ka gansu gwanin sha'awa cikin shiga ta kamala, Sakina tasan komai gane da Ameena dan har gidansu tana zuwa, tana kuma son Abdool sosai, haka rayuwa taci gaba da tafiya yau dad'i gobe sabanin haka, rayuwar duniya kenan haka ta gada, a gefe d'aya kuma Ameena naci gaba da kasuwancinta kuma duk k'arshe wata har Alhaji Sada na zuwa dubasu da hidima sosai kamar yadda yayi alkawari, su Baba ma na iya k'ok'arin su, so batada matsala a yanzu saidai wacce ba'a rasa ba.....

Suna NCE 2 wani malami na education ya basu Assignment to group discussion ne, kuma each group ten people ne, shiya rabasu da kanshi, from d different faculty, anan aka hadasu da wani Yusuf normally tasanshi saboda suna had'uwa GSE da EDU saidai magana bata tab'a had'asu ba, shine team leader nasu ita kuma assistant, shi d'an ENG/ISS, wannan Had'uwarne ta zama sanadin shakuwa tsakaninta da Yusuf, dan Yusuf social man ne, kokai waye ka zauna dashi sati yayi wuya Baku saba ba, dan akwai barkwanci gareshi burinshi bai wuce yasa mutane cikin farinciki ba, Sam shima ba ruwan sa da shashanci, kara2 kawai ya saka gaba kuma ga kwakwalwarsa tana ja ba dama, dan 3point kawai yake bugu ga G.P, hakan yasa ya saba dasu Ameena ko bayan gama assignment d'insu saiya kasance duk lokacin da basu da lectures sukan zauna suyi discussion a tsakaninsu based on their studies.

Yauma Zaune suke suna tattaunawa sai wayanta tayi k'ara, dauka tayi basuji me aka fad'a a d'ayan b'angaren, sun daiji tace.

"Subhanallah Asma'u meya sameshi?"

Still suka k'ara jin tace "tau ganinan zuwa" mik'ewa tayi a rud'e, tare da musu zataje gida, amma yanzu zata dawo, Sakina CE ta tambayeta meya faru, nan take gayamata Abdool ba lafia.

"Aa to inzo muje kawai".

Murmushi tayi Mata " kada ki damu Besty is not so worst fa, nima I will be back soon inshaa Allah " sannan ta wuce.

Duka sun tausaya mata ganin yadda ta rude har Yusuf ke tambayarta halan k'aninta ne, nan Sakina ta gayamishi a yaronta, ba k'aramin mamikine ya Kama shi ba danshi duk kallon budurwa yake mata ba Wanda zai ganta yace tanada aure hadda d'a, yace

"Amma fa bantaba tunanin matar aure bace, duk da kuwa naga tanada kamun kai".

"Hakane amma yanzu bata tare da mijin" nan dai Sakina ta bashi labarinta, sosai ya tausaya mata, hadda k'wallarsa, tare da sak'awa ransa wani tunani.


*life goes on......*


Kwana d'aya, sati, wata, shekara, haka shekaru keta tafiya a guje kamar ana kora su, zuwa yanzu Abdulrahim ya kammala karatunsa inda yake internship a nan Uduth, Asma'u kuwa tana rubuta final exam nata, soyayya suke gudanarwa cikin tsafta, dan sun dad'e da bayyanawa juna sirrin zuciyarsu, jira kawai suke Asma'u ta kammala karatunta su sanar da magabatansu, ayi taimaka a aurar dasu. Lol

Ayau ne ta kammala jarabawarta cikin nasara, kuma a yaune kowanne su ya shirya tsaf ya doshi familyn sa dan fallasa sirrin da ke ransa, dan cikar burin zukatansu, lokacin da Abdulrahim yaje da maganar gidansu Ard'o ya goyamasa baya d'ari bisa d'ari, dan yasan d'ansa bazai zabo abinda zai cutar dashi ba, dan haka ya bashi tabbacin a satin zasuje har shi A Argungu domin ganawa da iyayenta.

Tashin hankali Wanda ba'a sa mishi rana, ai Iya Hari dukane kawai bata mishi ba, amma ta inda take shiga ba tanan take fita ba, tas tayi masa ta kuma tabbatar masa baida matar aure inba Saude ba, dan bai isa ya banna mata lokaci a banza ba dole ya Aureta(Niko nace kamar shi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login