Showing 72001 words to 75000 words out of 88300 words

Chapter 25 - ABDULMAJEED BOOK by Meryam Abdul.doc

09 Oct 2025

1590

kashin awaki Mike kafarta tayi dama ta gaji da zuwa gidan, ga Hinde ba labari ta shige duniya saidai tana yi musu sak'o hakan yasa basu damu da sai tazo ba, ita kuma tana can ta zama rijiyar kowa itadai muradi ta samu shegun(Allah ya shirya muna zuria).



****************



Zaune take tayi nisa cikin tunani, fitowa yayi cikin shirinsa na fita hospital cikin suit dark blue sai k'amshi yake zubawa kamar yayi b'arin perfume, sumarsa se sheki take, ga man pride nasa yasha gyara sai kyalli yake(ni kuma nace kai wannan da mace ne da anga iyayi, anya Dr zai tsufa kuwa kullum gashinan d'an chas dashi kamar d'an 20, shiyasa Hafsat da Ayshat suka nace a kansa shi kuma yace ba wata daga 'yar Baffa) lol.

Da saurinsa ya isa gareta tare da hure mata ido, sauke numfashi tayi tare dayi mishi smiling, bata fuska yayi "baby ba zaki daina ba ko koso kike nima nawa jinin ya hau ne?" Ya fad'a tare da kafeta da mayun idonsa.

"Sorry my half bafa tunani nake ba, koma tunani ai saidai inyi naka kawai" ta fad'a cikin shagwab'a tana shafa man pride nasa.

"Uh um Baby kada kiyi kalya fa kin san son naki yake Ba kyau, pls ki dena baby it will effect u and unborn too"

Dariya tayi "um my son Ana can anayi ma Mami rigima nasan".

Lakuce mata hanci yayi " ai wannan son naki ke kad'ai ke iyawa da kayanki Mami kam zanesa kawai zatayi".

"Ai duk Kaine ka b'atamin yaro da rigimarka" tace cike da tsokana.

Zaro ido yayi "Zainab dai" yace tare da harararta cikin sigar wasa.

"Ba ruwan Aunty Zee, Mami ma take ka fisa rigima da kake kamarsa ai sun sha fama itada Aunty Asma'u" dungure mata kai yayi "Allah sarki Aunty nah ta kaina" sannan ya harareta "Ku jimun yarinyar nan wai ta girma itama to koma dai meye nine yayanki" dariya ya bata yadda yayi maganar kamar wani Junior.

"Hhhhhh Yaya wlh bakaji" ta fad'a tana ci gaba da dariya tsura mata ido yayi yana kallon ta ko kiftawa bayayi hadda aza hannu a haba, sai da tayi mai isarta sannan ta tsagaita kallon tayi tare da d'aga masa gira alaman kallon fa.

Smiling yayi tare da rungumeta tsam yana kissing gefen wuyanta " I always love u baby I always wanna see u in happy baby, keep being like that baby love more and much in every second of my life ur love is uncountable" itama k'ara hugging nasa tayi tare da lumshe ido tana jin dad'in maganganunsa dan tasan daga zuciyarsa suke fitowa "love u too my half ur my everything ur my life soulmate" tace idon??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????ta lumshe tana shakar k'amshinsa mai sanyaya zuciya.

"Yaya time na tafia kada ka makara fa, nima zan shiga na duba sister dan tun jiya bataji dad'i ba" tace tana duba watch d'in hannunta "kodai itama tabi layinki ne?" Yace ba tare daya d'ago

"To muje kaji daga bakinta" harara ya watsa mata "kinfa renani yarinyar nan" 'yar dariya tayi ba tare da tace komai ba

Zamewa yayi daga jikinta tare da mik'ar da ita tare da saka mata hijab d'in ta, kallon ta yayi tayi kyau cikin atamfar ta red & milk, hijab milk slipper ne a kafanta milk suma batayi kwalliya ba powder kawai ta shafa sai lip gloss, tayi kyau ga cikinta yayi tutsu a gaba kamar wacce zata haihu yanzu, light kiss yayi mata a lip "u look like take away, kodai na fasa fitane?"

Smiling tayi "banason fitina ni Muje don Allah" shima smiling yayi sannan suka fice, a parlour suka samu Hakeem ya tasa Nihal gaba yana rarrashi sai shagwab'a take zuba mishi yana biyeta, d'aure fuska Abdool yayi bayan sun gaisa "meye wannan sakarcin kukeyi anan, ke hala yarinya ce kike wani narkewa" yace yana kallon Nihal, k'asa tayi da Kanta tare da nutsuwa dan har yanzu tsoron Abdool take.

"Ha'ah malam ya haka? Haka kawai zakazo ka takuramin mata ko lafia bata isheta ba, Aa nifa in ba jinya kazo ba kama kanka kawai banason takura haba" Hakeem yace yana watsa mishi harara.

Tsaki Abdool yayi "to me mata ni kaga tafiyata" yace tare da ficewa, binsa da kallo Ramlah tayi "kai ya Abdool rigima ko meye nasa na muzurai haka? Shegen son girma" tace a ranta.

Rarrashin Nihal Hakeem yayi sannan ya fita yana fad'in ya bawa Ramlah amana kafin ya dawo dariya tayi tace to zata yi iya k'ok'arin ta, a mota ya samu mutumin nasa yana ta cika da batsewa shi dariya ya basa wlh wai talle kema Audi gori, nan zukayi rikicinsu sannan aka dawo normal da yake kar tasan kar.

Bayan Sun wuce ne Ramlah tace "anya sisto kodai-kodai" tana dariya.

"Um bafa komai sisto Malaria ce" tace tana dariya, itama dariya tayi "gara da kika ba kanki dariya, indai ta ruba maji d'oyi....."




****************


Cikin Ramlah ya shiga wata tara ga Nihal na fama da laulayi hakan yasa dole Abdool ya d'auki Hutu shike mata komai zama dak'ar tashi dak'ar cikin kuwa yayi wani irin girma kamar ba cikin fari ba, sau hudu Abdool nayi mata scanning amma ya kasa gane komai dan abu d'aya yake gani saidai girmansa yafi k'arfin na yaro d'aya, ya shiga damuwa sosai kullum tunanin haihuwar yake ga tausayinta daya addabesa, itama duk da akwai kuruciya tana shiga damuwa akan nauyin cikin yayi mata over itakam bata tab'a ganin ciki mai girman nata ba, ga bacci dak'ar takeyi kullum cikin Addu'a suke, Mami ma tanayi musu sosai, tuni ta maida junior gurin ta, kullum saita kirata yatakejin jikinta? Idan taji ba dai2 ba ta fad'a kada tayi shiru fa? Kusan kullum hakane.


Yauma dak'ar ta samu tayi bacci, can cikin baccinta taji kamar an mintsile ta, a Mara Aa Abu kamar wasa sai gaba yake juyi ta farayi tana laluben Abdool, tana kiransa.

Abdool dake kan sallaya yana sallah kamar yadda ya saba, mafi yawan Addu'ar sa a yanzu bata wuce fatar Allah ya sauketa lafia ba, anyi sa'a yana raka'ar k'arshe.

Yana sallamewa ya isa gareta cikin rud'ewa "baby menene haihuwar ce? Ya tambayeta yana dubata, girgiza masa kai tayi cikin jin zafi " Yaya marata bayana zasu balle Yaya zafi, wayyo Yaya" dak'ar ya samu ya tattaro nutsuwarsa ya shiga dubata haihuwa ce amma tana da d'an nisa,

Wayarsa ya ciro ya kira Dr ma'aruf da Dr Zaid sannan Dr Sharhabila, suna ganin kiransa sun San kwanan zancen dan ya gaya musu a hospital d'in sa yakeso matarsa ta haihu, dan haka su zama cikin shiri da lokacin yayi zaiyi invite nasu, Hakeem ya kira shima yana ganin kiran ko Nihal bai tayar ba ya fito a filin gidan ya samesu ya riketa suna zagayawa.

Key ya bashi na hospital d'in yace ya bud'e da musu, ba dadewa saiga Drs d'in sun iso, zuwa lokacin ko tafiya bata iyayi sai nishi kawai take, Abdool duk yayi kalar tausayi, Dr Sharhabila ce ta shiga bata taimako amma shiru ba labari, fitowa tayi duk ta had'a gumi, gogewa tayi tare da kallon su duk sun zuba mata ido.

"A gaskiya tana shan wuya and as u we know babyn yayi mata girma ba zata iya haihuwar sa da Kanta ba, so inaga data jigata ko a bata lokaci azo a samu matsala better gwanda ayi masa C/S d'in kawai yanzu.

Tashin hankali k'arara a fuskar Abdool duk dama yasan da maganar amma kuma ya kasa jurewa gani yake itama tafiya zatayi kamar Zainab, aiko idan hakan ta faru yasan yayi bankwana da farinciki, saurin kawar da tunanin yayi dan baya fatan hakan ta kasance.

Dr Ma'aruf ne ya dafa sa " karka karaya Abokina don't forget ur a Dr kasan komai game da irin wannan just be strong, inshaa Allah zamuyi nasara" haka dai sukeyi ta bashi baki har ya samu courage sannan sukeyi shirin shiga theatre.

Hakeem ne ya kira Mami, yana gayamata ko magana basu k'are ba ta katse wayar, cikin gaggawa tayima maid bayani abinda ake ciki sannan ta dauki motarta ta fito, duk da gab da asuba ba hakan bai hanata fitowa ba.

Sun shirya tsaf Dr Sharhabila ta shirya Ramlah yana fitowa da ita akan be zuwa theatre room, ganin halin da take ciki na shan wuya yasa Abdool zubar da hawaye zuciyarsa ta karye, hannunta ya kama, murmushin k'arfin hali tayi masa "Yaya ka dena kuka pls kayimin Addu'a kaji, pls ka yafemin koda ban tashi ba ka kula da son da babyn da zan haifa idan Allah ya rayashi, pls Yaya kada kayi kuka"

Maganganun ta suna kama dana Zee kaddai itama ban kwana take masa, jikinsa sanyi yayi k'alau, kasa shiga theatre room d'in yayi, ba yadda basuyi dashi ba, yak'i dole suka wuce suka barshi nan, jin yayi duniya ta masa zafi gaba d'aya.

Motarsa ya d'auka ya fice daga hospital d'in gaba d'aya, shi kansa baisan Inda ya nufa ba.

Shigarsu ba dad'ewa Mami ta iso ana kiraye-kirayen Asuba, gidan Nihal ta wuce anan tayi sallah sannan sai lokacin Nihal taji meke faruwa nan hankalinta ya tashi sosai bayan sun yi Sallah suka isa cikin hospital d'in.

Ba abin take maimaitawa sai Addu'ar nan ta samun sauk'i wato *"Allahumma la sahla illah ma sahaltahum wa anta aj'alar hazna Iza shi'ita sahla"*har akayi mata allurar bacci Kalmar da ke bakinta kenan har bacci ya d'auketa.

Cikin nasara da iyawar ubangiji, cikin sauk'i sukayi nasarar ciro jarirai guda 4 daga jikinta lafiyayyu kyawawa na gaske nan fa Dr Sharhabila ta riked'e ta dawo unguzoma cikin k'ank'anin lokaci ta gyarasu tsaf cikin lallausan over roll kowa da kalar nasa, sai santin yaran Drs keyi kowannensu rige-rigen kiran Dr Abdool yake saidai wayoyinsa duk a kashe hakan suka hak'ura da kiransa suka maida Ramlah d'akin Hutu.

Dawowar Hakeem daga masallaci yayi dai2 da isowar su Mami nan suka had'u suka shiga a tare, Wanda yayi dai da Dr Sharhabila ya turo yaran a cikin d'an bed irin na kids dake asibitin dan Hospital d'in ba k'arya taji kayan aiki designers, rige-rigen isa gurinsu su Mami sukayi mamaki da farinciki ya Hana su magana, sai murmushin farinciki sukeyi suka shiga santin yaran daketa bacci maza 2 mata 2, lallai Allah mai iko fidda rai cikin rai sai Allah, ya b'oye sanin sa da baiwarsa a cikinta ya dungule kamar d'aya Ashe har had'u ne.

Drs ne suka fito suma fuskokinsu d'auke da farinciki barka sulayima su Mami sannan suka wuce masjed dan gabatar da Sallah.

Gurin Ramlah sukaje suka dubata har yanzu bata tashi ba, gida Nihal ta koma tare da Dr Sharhabila don tayi sallah ita kuma ta had'a musu kari, akabar Mami da Hakeem a nan.

Mami ganin har su Dr, ma'aruf sun dawo ba Dr Abdool yasa ta tambayesa nan suka ce sun d'auka ma ita yaje d'akkowa dan tun da ya fita bai dawo ba kuma ga wayoyinsa duk a kashe..

Abdool kuwa tunda ya fita baima San ina ya dosa ba tafiya kawai yake, jin ana kiran sallah ne ya cilasta masa tsayawa a wani masallaci ya shiga yayi sallah, anan yayi sallarsa ya duk'ufa da Addu'ar samun sauk'i da nasara ga Ramlah, saida haske ya fito sannan ya fito daga masallacin, hankalinsa ne ya koma a yaje yaga ya ake ciki, tunda duk ya kashe wayoyinsa bale a kirasa hakan yasa ya shiga motarsa baisan yayi nisa da hospital ba saida yaga unguwar da yake, hakan yasa ya shiga sharara gudu dan Ramlah kawai yakeson gani a yanzu.........




_every body shoki 'yan 4 sun iso_ =؃?





@ABDRAM TEAM###=?
?
[10/12, 6:29 PM] =؄?Meryerm Abdool=؄?: =ؤ? ```ABDULMAJEED``` =ؤ?

(' *Servant of Majesty* ('



Na
=؄? _Meryerm Abdool_ =؄?


? *Pure moment of life writers*
P.M.L=ت?
(We don't just entertain and educate we touch the heartd' of the readers=???)



*#WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM*
*#IG PML WRITERS*
*#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*
*#http://maryamsbello.blogspot.com*


*_An karb'o daga Abu huraira Allah ya yarda dashi yace" manzon Allah (S.A.W) yace :- kalmomi biyu masu sauk'in fad'a a harshe, masu nauyaya mizani, mafi soyuwa a gurin ubangiji sune, subhanallahi wabihamdihi subhanallahil azeem_* =?L?
(Husnul Muslim)




_gareku k'awayen kirki, alkhairin Allah ya riskeku aduk inda kuke, kuna raina koda kuwa munyi nisa da juna=?%? Maryam warah, maryam D/gari, Maleeka auta, Sakina mungadi, fareeda sama'ila, Auntynah Dija #double love my boo=?
?=??_








=??? *Episode* 241--245






Kicib'is sukayi da Mami a reception, harara Mami ta watsa masa "ina ka shiga ne? Kuma duk wayoyinka a Kashe tsabar renin wayo"

K'eyarsa ya shafo da hannunsa, har yanzu hankalinsa a tashe yake, amma ganin Mami cikin normal mode, yasa hankalinsa yadan kwanta "yi hak'uri Mami wlh hankali nane ya tashi shiyasa na kashe wayoyin, Ramlah fa Mami ta sauka?"

"Tana ciki" ta ansa mishi a tak'aice, tare da wucewa abinda, yasan fushi take dashi shiyasa tak'i kulashi, da sauri yayi gaba da Dr Ma'aruf yaci karo "Dr Abdool where have u been? And urs phones is off?"

"Hmmm am not in mood that time, have u successful C/S??" Ya fad'a yana zuba masa ido.

Fad'ad'a murmushin fuskarsa yayi "congrat my friends ur wife and d baby's are in good conditions"
Wani gauron numfashi ya sauke tare da Rumgesa hadda d'an kwallar farinciki bakinsa d'auke da hamdala da godiyar ubangiji "nagode sosai abokina Allah yabar zumunci, ina take yanzu?"

Kafin ya bashi amsa su Dr Sharhabila suka iso tare jariran, ware ido sosai yayi yana kallon baby's d'in sannan ya kalli Dr Sharhabila baki sake.

Murmushi tayi "all is urs Dr" ta fad'a, anan ya zube yana sujudush shukur, Bakin bed d'in ya tsaya tare da zubawa yaran ido sai motsi suke a hankali alaman suna son tashi "lallai Allah mai girma shi keyi a inda yaso kuma ga Wanda yaso a lokacin da yaso ba tare da karfi ko dabara ba, Allah na gode maka da wannan babbar kyautar da kayi mana" ya fad'a a ransa, nan su Dr Sharhabila suka shiga tayashi murna, shima godiya yayi musu sannan yayi ma yaran Addu'a kamar yadda akewa kowane jariri na musulmi a koyarwar manzon rahama tare da yi musu Addu'a.

Dr Sharhabila ce tace ya kamata Ramlah ta farfad'o yanzu, d'akin da take yaje da sauri dan ganin ta kawai yafiso a yanzu, shigarsa tayi dai2 da fara motsinta, da sauri ya isa gareta tare da yanyota zuwa jikinsa yana kallon ta, sannu a hankali ta fara bud'e idonta fes idonta ya sauka a kansa yana mata murmushi, lumshe idon tayi tare da k'ara bud'e su, a tunanin mafarki take, shidin dai ne to amma meya kawo wannan sabon gurin? Sannu kwakwalwarta ta tariyo mata abinda ya faru, hannunta takai kan cikinta jin sakayau ga zafi da taji a gurin ya sakata fara k'okarin tashi.
Maida ita yayi tare da shafa mata kai yana mata magana a kunne wacce nidai Meryerm Abdool banji me yake cewa ba, ganin nai ta lumshe ido tana murmushi (nace to harkin manta kenan da zafin).

Turo k'ofa akayi Dr Sharhabila ce ta shigo tana murmushi "sannu Madam kin farfad'o sannu ya kikejin yanayin jikin yanzu?" Tace tana gyara bed d'in na babys data shigo dasu dai2 gadon nasu.

Cikin siriyar murya tace "Alhmdllh da sauk'i" ba tare data bud'e ido "baby tashi kiga yaran ki" Abdool ya rad'a mata a kunne.

D'an bud'e ido tayi ganin yara har 4 yasa ta zaro ido ta kallesu dakyau sannan ta maida kallon ta gareshi mai cike da tambaya, lumshe ido yayi tare da smiling, ya Dora hannunsa kan k'irjinsa ya rungume hannayen nasa sannan girgiza mata kai alamar eh.

Murmushi Dr Sharhabila tayi tare da ficewa tana fad'in "wishing u spreed and quick recovery" sun burgeta matuk'a.

"Bansan me zance maki ba baby nagode sosai da wannan kyautar mai girma"

"Yaya ya zanyi dasu sunyimin yawa"
Smiling yayi "baby zaki iya Allah bazai dorawa rayuwa abinda yafi k'arfin ta ba, Ki kwantar da hankalinki inshaa Allah zaki iya kinji"

Girgiza kai tayi alaman to sannan tace Cikin sanyi" Yaya haihuwa da zafi bazan k'ara ba" dariya mai sauti yayi "haba baby nah kefa jaruma ce, nida ke tunanin next year ki bani wasu 4" yace cike da tsokana, zaro ido tayi tare da kwab'e fuska zatayi kuka "oh sowie jarumata wasa nake fa" yace yana mata dariya ransa fal farinciki tsantsa.

Ba dad'ewa su Mami tare da nihal suka dawo da abun karyawa, suka karya sannan suka kintsa aka wuce da ita hospital d'in su Abdool dama burinsa kawai Ramlah ta haihu a hospital d'in sa, admitting nata akayi nan fa akaci gaba da bata kulawa ta musamman ita da yaranta.



***********



Tuni asibiti ta cika da 'yan barka su Sadee har an kawo jiki sai yaba kyawun baby's d'in kowa keyi gasu manya ba laifi kamar d'aya d'aya, biyu sukayi kamannin uwa fatar uba, biyun kamannin uba fatar uwa.

Lokacin da junior yaga yaran washe baki yayi yana kallon su ya tab'i wannan ya yayi ma wannan kiss yayi wannan wasu duk ya rud'e yace "Maa duk nawa ne?" Smiling tayi masa Mami tace "duk naka ne beran masar saura ka koya musu bannar da rashin jin" dariya kawai yace yaga yaran da yafi girma shima ya zama babba.

Mutan Argungu ma sun iso jin wannan babbar kyautar wannan karon hadda Baba, Ard'o kam jikin Hari ya hanashi zuwa sai lokacin ya gayamusu halin da take ciki Mami ta janjanta sosai tace inshaa zasuzo bayan suna, Ramlah kam hadda hawayenta Ashe shiyasa tayi ta mafarkinta Ashe da gaske tana cikin mawuyacin hali fatar samun sauk'i tayi mata, Abdool ma ya jinjina al'amarin.

Alh Sada ma yazo yaga 'ya'yan nasa tare da basu kyauta mai tsoka, su Amal duk sun zo sai tarairayar yaran ake feeding kawai ke had'a su da Ramlah, Nihal, sadee, Amal kullum asibiti suke wuni sai dare ga kuma nurses masu kula dasu na musamman, ga uban gayyar shima yana kusa, satinsu d'aya aka sallamesu.

Abdool an gyara gida a tunanin sa can zasu wuce sai jin yayi Mami tace gidanta zasu nuna ba halin musawa duk da ransa baiso ba, dan har yanzu Mami bata huce dashi a ganin ai wauta ce ba rudu ba.

Nihal sai kullum suna gidan Mami sai dare Hakeem ke zuwa ya d'auketa da sassafe ya sauketa Sadee ma hakan ce,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login