Showing 78001 words to 81000 words out of 103127 words

Chapter 27 - DUHU Book Complete By Slimzy .txt

Slimzy   

19 Jun 2024

12518

hafsat na tallabe da husnah idanuwanta a rufe ruff duhu take gani cikin sanyin jiki hajiya hafsat ke shafa kan husnah tace "husnah bude idonki kifadamun ya kikeji yanxun"ta bude idonta tangaras bata ganin komi ta dago fararen idonta tace "banajin komi"ta yunkura ta mike Abraham na cikin dakin yana tsaye gabanta ya kasa karasawa Kusa da ita gaba daya ta canja masa dik yadda yaso ta gansa bata ganinsa tsaye yayi yace "husnah yanzun kin zabi rabuwa dani akan ki zauna da wani kin karya alkawarin da kikamun kenan?"hannu tasa ta toshe kunnuwanta jin sautin wata murya a kunnenta hajiya saude ta shigo "yadai husnah"cikin tsoro da wani yanayi tace "momy wata murya nakeji wai na karya masa alkawari momy kuma ni bansanshiba"


"baki sanniba husnah?nine mijinki Abraham ni din ne baki sanniba?"ta zabura tana waige waige cikin tashin hankali tace "momy kinji Yana cewa wai bansanshiba shi mijina kinjifa nifa bansan wayeba momy tsoro nakeji ina yaya yaseer?"ta jefowa momy tambaya hannu momy ta daga sama tace "Alhamdulillah "suka kallu juna da hajiya hafsat sukai murmushi alamu sun nuna husnah bata ganin Abraham sabanin da sanan yadda take cikin damuwa ya tabbatar musu da maganin datasha ya batar mata dashi daga tunaninta tasamu mantuwa,


ummah hadiza tace "ku fito kuyi haramar rakamu nida diyata amarya da husnah kunga Garin yana had'a hadari kar ruwa ya tsareku,husnah tashi ga gyalenki"ta mika mata babu musu ta karba"Abraham yana tsaye wasu hawaye ke zuba a idanuwansa husnah bata ganinsa? muryarsa kawai takeji dik soyayyar da husnah keyi masa yanzun shikenan bata ganinsa jinsa takeyi shima ta mance dashi?ya bace daga dakin momy suna fita tayi sujadar godiyar Allah yanzun shikenan husnah yau zata tare da yaseer?abinda suka dade suna jira?ta shige dakinta suna kokarin fita hajiya rabi ta shigo gidan harajan majaran kamar an korota suna rike da ita suna adduoi aka shiga da ita....


*****
muneeba ta makalkale yaseer cikin kissa da shagwaba kukan shagwaba take zuba masa dik yadda yaso ya zare jikinsa ya tafi taki barinsa satar kallonsa tayi ta kalli lemon data hada masa da kwayar da sukasa ciki "tin dazun nake cewa gashi kasha kaki ko dan yau amarya zata tare?"ta kwanta a kirjinsa gashin kanta ya hargitse tamkar mara lafiyar gaske "ba haka bane muneeba itama wadda kike maganar batada lafiya gatacan kwance kuma nazo wajenki kinamun korafi umm?yanzun kisha magani ko na kaiki asibiti"ta faki idonsa cike da shagwaba ta fizgo kansa ta hade bakinsu waje daya ransa ya baci sosai mutumin da beda lafiya yake wanan abubuwan ga halin da husnah ke ciki ya janye ta fashe da kuka hawaye biyu biyu ya kalleta yadda ya rame ves ce jikinta cikinta ya fito haihuwa kamar kanka fita yadda cikin yayi girma ya shiga share mata hawaye "ya isa ki daina kuka ina sonki banason abinda zai sameki ko kadan kinji?"ya gyada mata kai tasa hannu ta dauko glass cup din tayi narai narai da ido "yanzun ko abu na baka ma baka karba yaushe rabon da kaci wani abu nawa bayan da aljani naketa rayuwa bansaniba"yayi ajiyar zucuya yace "shikenan bari yanzun zansha kawo banason rigima inace idan nasha dai shikenan?"ta gyada masa kai ya karba yasha murmushin mugunta tayi ya shanye tas ya dire cup din ya tsareta da ido tadan muskuta zata Tashi cikin yanayi na ciwo tace "washhh cikina"tana yarfa hannu "menene kuma cikin ne ko muje asibiti?"wani Abu yaserr yaji yana fuzgarsa kansa na juyawa biyu biyu yake gani nan da nan idanuwansa sukai jajir idonsa har rufewa yakeyi tsananin yadda yake ganin jiri da bacci ya koma yw zauna yaraf,
ta dan gyara zama cike da kulawa tace "yadai?"yace "bacci nakeji sosai gashi na baro husnah"yana hamma yayi maganar ta miko masa pillow "akwai mutane a tare da ita ina ganin kadam kwanta kafin su watse"ya jinjina kai ya karbi pillow yasa ta bayansa ya kwanta ko minti biyu beyiba bacci yeyi gaba dashi tayi murmushi ta mike tana kallomsa ta cije baki "badai rawar jiki kakeyi ba?zakaje ka angwance da matar aljani wadda kake tsananin so kana Wani rawar kafa sai kaje"ta ciro wayarta cike da farim ciki ta turawa Anty sadiya tex,


su innah a tare suka fito dasu hajiya saude motocinsu na wajen gate iska kawai ke kadawa hadari yayi bakinkirin ta dubi ummah hadiza tace "tou ga husnah nan kisa ido maganinta Dan Allah sanan wanda yake hannun mahaifiyarta kije ki karba ya koma hannunki dan alamu sun nuna zamuyi nasara inata kiram yaserr baya dauka fatana dai ba gidansu hafeez yaje ba dan ba hankali garesa ba zan kirasa daddare inja masa kunne"


"insha Allah zan kula da husnah kamar yadda zan kula da yar dana haifa ai husnah yata ce gaba da baya"sukai sallama dasu innah itada nusrah suna daga musu hannu nusrah cike take da kewar yar uwarta databi momy suka juya suka shiga cikin gidan,


husnah na daki taji kamar motsi a kitchen tadan sa kai ta leko tace "wanene?"shiru bataji kowa ba jim ana wasa da ruwa ta diro daga gadon ta shiga kitchen din inuwar mace tagani dishi dishi ta murza idonta ta bude bataga kowa ba ta waiga su ummah hadiza suka shigo"yadai husnah?me kikeyi a nan me kike bukata"


"motsi naji ummah hadiza shine na fito naga inuwar kamar mutum tsaye na karaso banga kowaba kingani"cike da tsoro take maganar idanuwanta suka cicciko da hawaye rukota ummah hadiza tayi zuwa daki "karkiji tsoro da kinji motsi kice hasbunallahu wabniimal wakeel"ta gyada mata kai tace "kidaina lekowa in kikai magana kikaji shiru,ta sunkuyar da kai tanaso ta tambayi ummah hadiza Yaser ta kasa cike take da kunya tunaninsa takeyi tun dazun tanaso ta gansa tsananin kwadayi takeji yazo ya siyo mata abu tarasa inda zatasa kanta kwantar da kanta tayi a pillow yana can tare da matarsa kenan?ta dago kai ta kwalawa nusrah kira da sauri ta shiga dakin taga husnah shabe shabe da hawaye tadan tsorata "lafiya kike kuka?"


"kiramun yayanki a abunda kike kiransa"dariya taba nusrah waya takeso tace tsananin shagwaba da yayi mata yawa nusrah na dialing wayar Yaser akace mata a kasge,


"nusrah ki zauna da husnah bari nashiga gidan can wajen zainab na karbo magani naga dare ya somayi magriba kar ruwan nan ya kece ko?"tace "toh"ta fice,


Cikim farin ciki sadiya ke labartawa hajiya rabi plan dinsu nasawa Yaser kwaya a abunsha hajiya rabi ta gyara tsayuwa tace "kai nayi matukar farim ciki kinga dik rawar duwawum nan da sukeyi nasan cewar yaseer a dakin muneeba zai kwana kinga nan zasu tabbatar bason renom aljanu yakeyi ba"suka sheke da dariya "wai Anty dazun ina kikaje?"


'umhmm gidan boka naje yanzun zam aiwatar da abinda ya bani ya tabbatarmum in zuba abin nan a cikin abincin hajiya zainab dana badamasi da sumci shikenan"suka sheke da dariya sadiya tayi kasa da murya tana dariya kasa kasa tace "shiyasa kike makale a kitchen?"ta jinjina kai ummah hadiza ta shigo jin taku da sallama daga gate sadiya ta fice tayi sashen hajiya rabi ita kuwa saurarawa tayi taji kamar ba nan bane ta wawwaiga babu kowa ta fito da maganin har ummah hadiza ta gifta ta dawo ta tsaya tsaye tana kallom hajiya rabi tana zuba magani,




Abraham ne ya sauya kamanninsa sak ya koma hafeez ya shigo gidan cike da kudirin karbar maganin da hafeez ya kawo sallama yake dokawa shiru ya dan tsaya yadda hafeez keyi daga window momy ta hango hafeez tayi saurin daukar hijab ta nufi hanyar fitowa.....




*WANAN LITTAFIN NA DUHU 300 KACAL ZAKI BIYA KI MALLAKI NAKI IDAN BAKI BIYABA KIKA KARANTAMUN BANYAFEBA*


07042277401
08036953516




*SLIMZY*✍🏻




43
tsaye momy tayi tana kallon ummah hadiza da ta tsurawa hajiya rabi ido ganin inuwar mutum yasa ummah hadiza juyowa nuni tayi mata da tai shiru "shhh kiyi shiru karkice komi"tayi shiru ta had'iyi wani miyaun bakin ciki yau ta tabbatar da hajiya rabi asiri tayiwa daddy ummah hadiza ta tako a hankali ta karasa ta ruko hannun momy su shiga daki Momy ta yafito Abraham dake tsaye yana kallon komi tace "taho hafeez na ga shigowarka ai shiyasa ma nataho dakaina nace bari nazo barka da zuwa"a hankali ya tako ya shigo ya tsugunna har kasa "momy barka da yamma"ya sunkuyar da kai ummah hadiza ta tsaresa da ido haka kawai jikinta be bata ba yuwwww taji juwa na neman kadata ta jingina da jikin kujera,


"da magribar nan ga hadari hafeez ka kamo hanya ka taho?"ya jinjina kai yana wasa da makullin hannunsa yacev"momy dama akan maganin nan ne dana kawo nace bari inzo in karba ashe bana husnah nakawo ba na kanwata ne dama biyu na karbo maganin"


"toohhh hafeez gashi anbawa husnah hartasha kardai akwai matsala"ya jinjina kai ya dago kai yaja gauron numfashi ya sauke yace"babu momy kawo sauran maganin zan kawo natan?"tsare Abraham ummah hadiza dayi da ido tana karanto adduoi jin tsigar jikinta na tashi ta tabbatar akwai matsala tace "kai daga idonka ka kalleni"ummah hadiza tace cike da fada Abraham ya hadiyi wani miyau a ransa yace kardai matar nan ta gane niba mutum bane,,momyn husnah ta mike a sanyaye ta nufi bedroom dinta ummah hadiza ta tsaidata tace "zainab Ashe har yanzun da sauranki bakisan sharrin aljanuba ko?ai inda maganin nan bana husnah bane to take husnah bazata samu lafiya ba maana yadda ta daina ganin wanan shaidanin aljanin wanan da kike ganinsa ba hafeez bane aljanine"momy ta tsorata tana kallon ummah hadiza ta jinjina mata kai tace "tabbas Aljani ne?"momy kasa kallon inda Abraham ke zaune tayi ummah hadiza ta mike cikin azama tana kokarin karanto adduoi ganin haka bat Abraham ya bace ummah hadiza ta girgiza kai tace "shedani"


"tou waigo ki kalla"dakyar momy tayi ta maxa ta waigo ta kalli sashen daya zauna wayam bataga kowaba a wajen wata ajiyar zuciya ta sauke saidai a tsorace take matuka ta kasa ko motsi ummah hadiza ta mike jin ruwa na kokarin sauka tace "ina kika ajiye maganin?"momy tayi mata nuni har yanzun kafafuwanta rawa sukeyi data kalli wajen sai taga kamar Abraham na zaune ta wuceta ta dauko maganin tace "wanan yakin daya rage kece zakiyiwa kanki Kuma tunda kingani da idonki ana zuba muku magani a abinci idan akwai wanda baasa maganinba ki sauya ki ajiyewa mijinki gobe zansa akawomin wani magani da zaki amfani dashi akan alhaji badamasi nabarki lafiya "ummah hadiza ta fuce hawayene suka wanke fuskar momy lallai tayi bacci bayan yunkurin saka mata laya a baki yanzun gashi Ido da Ido tana gani ana barbade a abinci,ajiyar zuciya ta sauke ta kallu kular data zuba abinci a ciki iri daya ne abincin da wanda hajiya rabi ta zubawa magani ta dauka cikin sand'a ta fice ta nufi kitchen din harta zuba masa a kula ta juye abincin a leda ta ajiye gefe ta zuba nata ta gyara Kular ta fice....horn na motar daddy taji cikin sauri ta koma dakinta har yanzun cikin furgici take da Aljanin dayazo dazun ta shiga toilet ta dauro alwala anata kiraye kirayen sallahr magriba....


******
tagumi husnah tayi akan kujera two seater nusrah na zaune akan dadduma ta idar da sallah,ummah hadiza ta shigo da sallamarta "ah ah husnah ya naganki zaune kinyi tagumi?"tayi saurin kurkiro murmushi tace "bakomi ummah"


"tou Tashi maza kije kiyo alwala kizo kiyi sallah kema kin zauna kin tasata a gaba tana sallah ke kinyi tagumi ko kinada wata damuwa ne?"girgiza kai kawai tayi idonta cike da hawaye sam tarasa meke damunta wani irin kunci takeji a cikin ranta wanda batasam dalilinsa ba dakyar take taka kafarta ta shiga bedroom dinta ta jikin windown glass taga kamar mutum tsaye ta kurawa glass din ido taga yana budewa yana rufewa wata murya taji ana mata magana wani haske kamar walkiya daga jikin glass din ya taho ya nufo jikinta kafin tayi wani abu ya Shiga jikinta kasa shiga toilet din tayi ji tayi kawai bazatayi sallahr ba bataso ta nemi waje ta zauna "ina miki magana?bazaki kulani ba?"ta juya bataga kowa ba cike da damuwa tace "wai waye keson takurani ne?waye kemun magana"cikin kosawa tayi maganar tana waige waige ajiyar zuciya taji anyi hade da fad'in a sanyaye "husnah mijinki ne ina sonki husnah husnah ina sonki karki rabu dani gashi baki ganina yanzun nayi kokarin ki koma ganina abun ya faskara,amma inaso in kasamce dake karkiyi alwalar nan kinji?"wani abu taji yarrr yadda yayi maganar ya matukar bata tausayi dikda takasa tuno muryar da akeyi mata magana,ummah hadiza ce ta shigo hade da turo kofar ta zabura ganinta "husnah me kikeyi zaune gefen gado ke kadai?inace an hanaki zama ke daya anzo ana miki magana ko?"ta kalli window gani tayi ana hura window yana gaba yana baya yana fadin "karki fada"ta girgiza kai ummah hadiza ta cije lebe "baki sallahr ba kenan?"ta dago kai ta kalli ummah hadiza taga ta tsareta da wani kallo na tuhuma tsoro ya kamata ta girgiza kai "banyi ba ummah nashigo dakin kawai naji banaso inyi ummah kibarni Dam Allah"ruko hannunta ummah hadiza tayi batace komiba ta nufi toilet da Ita ta shigar da ita ta dauko buta ta mika mata "maza yi alwala kiyi ina kallonki ki fito zan jiraki kiyi sallah wato an fito da tsurfar hanaki kiyi sallah ko?"babu musu husnah ke alwala tiryan tiryan suna fitowa sukaji anja wani mugun tsaki hade da kwafa husnah taja da baya tana kallom ummah hadiza cike da tsoro tace "kinjifa kinji ummah?"tsaki tayi kawai ta shimfida mata dadduma "oya maza tada sallah kafin raina ya baci idan kin idar kizo kiyi hayaki kafin mijinki ya dawo nina rasa ina yaseer ya shiga ma mtswww"husnah ta tada sallah ummah hadiza na zaune gefen gado harta idar ta kama kanta tayi mata addua tace"tashi muje bazan barki ba nasani ko zai shigo tayaki fira munafukin"ta fuzgo hannunta husnah naso taji meyakeson fada mata tana jin tausayinsa sosai suka fito nusrah tasa tv zatayi kallo ummah hadiza ta sauya tashar zuwa ta karatun alkurani suna nan zaune gaba daya husnah hankalinta ya rabu biyu ta rasa meke mata dadi dan zaman da sukeyi da yaseer a dakin momy tana masa shagwaba yana biye mata ta fara sabawa dashi ko ina yaje oho,take wata zucuyat tace Yana tare da matarsa kin manta ku biyu ne?"wani abu ne yazo mata wuya ya tsaya mata,


"ummah akwai komi a gidan nan ko?me zaa dafa ne?"Ummah ta jinjinawa nusrah kai tace"komi akwai dik abinda kikeso ki Shiga ki dafa mana ni yanzun inata jiran wanan ja'irin yaron ne....
******
momy ta fito da hijabinta ta nufi sashen daddy inda take jiyo muryarsu ta shiga da sallamarta ta zauna yadan kalleta sau daya ya kauda kai hajiya rabi ta watsa mata wata uwar harara "yadai kika shigo me kikazoyi"daddy yace yadda yayi maganar kamar ya sauko momy ta karanto adduoi kafin tace "nazo yi maka sannu da zuwa ne dama naji shigowarka"tabe baki hajiya rabi tayi ta turo dankwalinta gaba tana kad'a kafa suka hada ido batare da daddy ya ganiba tace"yau din nan zaki gaba yau zakibar gidan nan"tayi mata nuni da hannu tana dariya hade da harara dariya taba momy murmushi kawai tayi mata,daddy nacin abinci yadan saci kallon momy suka hada ido wani kallo tayi masa irin kallon da take masa ya gigitasa gani tayi ya ajiye cokalin ya juyo gareta mamaki ne ya cika hajiya rabi ta kalli kular abincin data zuba masa magani ya cinye tasss befi cokali daya ba boka ya sanar matada cewar dayaci bazai gamaciba batareda ya saki momy ba amma gani tayi kamar yanaso ya sakewa momy ta gyara zama cike da kissa ta kalli momy tace "masu ciki kenan nikam zainab yaushene watan haihuwanki?"wani kallo momy tayi mata ta dauke kai daddy yace "badake take magana ba ki amsa mana zainab banason bakin hali kibar ganin na sake dake harna barki kim zauna mun a daki"momy tace "nima bansaniba dan bana zuwa asibiti"daddy ya kalleta ya kalli cikin kyau sosai cikin yayi mata gata nan da kurucuyarta kamar ko yaushe bata canjawa yarasa dalilin dayasa inhar zai ganta zai rinka ganinta tamkar bakin kumurci ko bakar karya sam bayason hada ido da ita zucuyarsa nayi masa zafi ,amma yau yana kallom cikinta tabashi tausayi,ta mike tana daga kafa dakyar tace "saida safe"ya dan bita da kallo hajiya rabi ta kafesa da ido,


momy tsaye tayi a jikin kofar dakin daddy wasu hawayen farin ciki suka zubo mata yau Alhaji badamasine ya kulata?tana kallon yadda yake satar kallonta lallai tayi bacci tayi sake irin saken datayi aljani ya saace mata ya gashi dataje canja abincin bayan ta zuba ta tofa addua cikin abincin yaci gashi har ya kulata?ta girgiza kai tsakaninta da rabi Allah ya isa....


******
muneeba na kwance kirjin yaseer tana shafa gashin kirjinsa dake kwance luff bacci sosai yakeyo dik yadda taso ta juyashi tasamu kansa ya kusanceta ya kasa sakamakon bashida karfi kara rungumota yayi cikin bacci da magagi yace "husnah....husnah ya jikin naki?yadai?"yace kamar bugagge tsaki muneeba tayi yana bacci yana kiran sunan husnah saboda tsabar jaraba?husnah da momy bokansu na aiki amma zatayi maganinsu yau zataga yadda zaayi ya kwana dakin amarya,wata harara tayi masa kamar yana ganinta ta turesa ta zame jikinta Daga nasa,


bugun kofa taji da sauri ta zuro kafarta kasa ta kalli agogo karfe goma na dare to waye zai buga mata kofa yanzun?ummah?ta tambayi kanta badai ummah ba tasan tanacan makale da daddy ta muskuta wani nauyi kafafuwanta keyi bugun da akayi na biyu ne yasa yaserr mikewa furgigit kamar a mafarki yaji bugun yana fadin "husnah ina rigata?"muneeba tayi tsaki cikin kasa da murya tasan ya dauka a dakin husnah yake tace "ka kwanta bari naje na duba waye ke buga kofar"girgiza kai yayi "ah ah bazaki fitaba darene karkije aljanin nan ya daukemun ke ya zuro kafarsa yana lalube cikin saa yaji rigarsa a gefe ya zura cikin duhu yake kallonta mamakin ganinta da katon ciki yakeyi idonsa har rufewa yakeyi tsabar bacci bugu na uku ne yasa yayi saurin kunna fitila muneeba ya gani yana bim dakin da kallo "muneeba?a dakin nan nake dama?"tambayarta yakeyi cikin wata irin murya yace "magana nake miki"sosa keyarta tayi cikin murya mai ban tausayi a sanyaye tace

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login