Showing 93001 words to 96000 words out of 103127 words
da mari zai kuma innah ta ruko hannunsa "banda duka badamasi abi komi a hankali yanzun ni dik ba wanan ba babbar damuwa shine halin da muneeba take ciki"daddy yayi saurin yadda kwaryar hannunsa yace "wani hali muneeba ke ciki?wani hali kikasamun yata?"
"ka tsaya mana ba ita tasata ba zata iya yuwuwa ciwo daga Allah tunda matsalace data shafi cikin dake jikinta"dammm gaban Hajiya rabi ya yanke ya Fadi jikinta sai makyarkyata takeyi gumi na karyo Mata ji tayi kamar ta saki fitsari innah ta fadawa daddy halin da ake ciki ya kalli hajiyq rabi yana nunata da yatsa "ki fadamun meye silar faruwar hakan baxaki rasa saniba ko mugun abun da kikayi ne ya koma cikinta?"ya daka mata tsawa cikin in ina tace "ah ah ahah aljanu aljanune"daddy yace "aljanu sukai me?su suka dauke d'an"tayi saurin jijjiga masa kai "eh ehh sune"ya girgiza kai yace "dare yayi innah gobe in Allah ya kaimu zamu dauketa muje asibiti idan be yuwuba mu kira mai magani"
"saidai mu Kira mai magani Alhaji bana asibiti bane wanan"a sanyaye hajiys saude tayi maganar sukace "mu zamu tafi sai gobe"suka bar wajen daddy ya wuce masallaci.....
hajiya zainab na zaune a daki tana rike da jinjirinta daya take jiyo ihun hajiya rabi ta zabura harta ajiye dan ta dawo tadau Daya tasa a bayanta ta dauko dayan a hannu ta jiyo ihunta a sashen daddy tana shiga taga hajiya rabi tayi zaman yan bori tana rusa kuka "badamasi kada ka sakeni karkamun haka"wani kallo yayi mata "ni zaki zubowa magani a abinci kikawomin saboda ke shedaniya ce?yanzun nan fa na fito da abubuwa daga dakinki shine zakice bari ki zubamun wadda zaki rufemun baki ko to na sakeki saki uku rabi dama auren bansan dashi ba....turus momy tayi tana kallonsu daddy ya karaso ya tarbeta ya karbi dan dake hannunta yace"muje sashenki"
husnah rike da hannun juna suka nufo sashen muneeba surutan da takeyi ya furgitasu suka kasa shiga yadda take jifa da kaya yaseer ji yayi kansa kamar zai rabe biyu jikinsa ne ya hau rawa jiri na neman kadashi......
*WANAN LITTAFIN NA DUHU 300 KACAL ZAKI BIYA KI MALLAKI NAKI IDAN BAKI BIYABA KIKA KARANTA MUN BANYAFEBA*
07042277401
08036953516
*SLIMZY*✍🏻🥱
49
zama daddy yayi a gefen gadon hajiya zainab yana rungume da jariri guda daya kallo Daya zakai masa kasan yayi kololuwa cikin bacin rai da tashin hankali dikda yadda hajiya zainab ke jawa daddy aji wanan karon zama tayi gefensa ta ruko hannunsa yayi saurin kallonta ya janyota jikinsa da hannu daya ya rungume yana sauke ajiyar zuciya sunajin kururuwar hajiya rabi a daki ta dauki wanan ta fasa ta dau wancen ta jefar tamkar zararra girgiza kai momy tayi tace "Alhaji meyasa ka dauki mataki cikin bacin rai?da baka saki wanan matar ba da ka barta"hararar da daddy ya wurgo mata yasa ta kama bakinta jikinsa na rawa yace "ke zainab banason shashanci kwata kwata ke kinsan ban taba raayin auren wata maceba sanan in rasa wadda zan aurama sai rabi matar kanina ?"cikin bacin rai yake maganar cikin tattausan lafazi da sigar lallashi momy ta ce "kayi hakuri tunda dai ka rigada ka saketa shikenan yanzun dik be kamata kayi wanan bacin ran ba Alhaji kamata yayi yanzun aji da muneeba dake cikin wani yanayi na ban tausayi yarinyar na bani tausayi sosai koba komi muneeba yarka ce kuma matar yaseer dan amininka"jinjina mata kai yayi yasa hannu ya shafa mata kai yace "Allah yayi Miki albarka"ta jinjina masa kai jijjiga kofar dakin hajiya rabi keyi a fusace daddy ya dire jinjirin dake hannunsa ya fita hajiya zainab ta mara masa baya yana bude kofar ta zube a gabansa "daddy daddy Dan Allah ka maidani kada ka sakeni idan ka rabu dani ina zani ina matukar kaunarka inaso inzama matarka shiyasa dik na aikata abinda nayi"mari daddy ya shararawa hajiya rabi yasa kafa ya hankadera gefe yana nunasa da yatsa "ke mahaukaciyar inace?kinsan abinda kike fada kuwa idan baki gacemun daga gidaba wallahi rabi sainayi mummunan saba miki shashasha kawai jahila"ya maida kofa ya rufe nan hajiya rabi kamar zararriya take magana "Baka isa ka sakeniba ban sakuba kayi kadan Alhaji badamasi koka sakeni ban saku ba haka kawai ina matarka kace ka sakeni tayaya ma zaka sakeni bayan boka ya fadamun cewar dani kadai zaka zauna dole karabu da zainab"ta hada kai da gwiwa tana rusa kuka "wallahi bazanbar gidan nan ba"take fadi tare da mikewa tabar wajen tana maganganu kamar mai tabin hankali.....
a hankali husnah ta ruko muneeba da ta daga cup Zata wurga gefenta na dama tana zaune dakin yayi kaca kaca da ruwan daketa zuba ta gabanta juyowa tayi shabe shabe da hawaye tana kallonsu tsura musu ido tayi dukkansu yaseer idanuwansa sunyi jajir tsananin tausayin muneeba kalaman da takeyi ke yawo a kwakwalwar kansa ya rasa Inda maganganunta suka dosa tana ganinsa ta yinkura zata mike yayi saurin karasowa ta fada jikinsa tana fadin "yaya yaseer kaga yadda Allah yayi dani ko? kagani ko ummahna batasona taki kaini a rabani da abinda ke cikina yaya yaseer inaso in rabu dashi kada na mutu banaso na mutu yaya yaseer ancefa ba d'a bane a cikina"ta rushe da kuka yaseer ya rungumeta tsamm hushah dake tsaye ta tsura musu ido tana hango tsantsar kaunat da muneeba keyiwa yaseer a kwayar idonta shima tana hango tausayin muneeba a idonsa yana shafa bayanta yace "ki kwantar da hankalinki banason kukanki muneeba idan kina kuka kara tadawa kanki hankali zakiyi damu kanmu ga abinda ke cikinki kisawa kanki hawan jini"tq kafesa da ido wasu zafafan hawaye ke zubo mata husnah kuwa karnin da takeji yasa amai ya Shiga yunkuro mata ta daure ta cije harshenta ta kallesu cikin dakewa tace "Bari na gyara mata cikin dakin ko?ko ina yayi kaca kaca gashi ta fasa wadanan kofunan kada taji ciwo dasu"ra nufi kitchen yaseer yayi saurin rukota Yana kallon yadda tayi da fuska yasan dauriya takeyi akwai abinda ke damunta "kibari nayi kawai karki damu ki koma gida "langabe kanta tayi gefe guda ta makale kafada cikin shagwabarta mai daukar hankali tace "kabari kawai inyi insamu ladan yar uwata koba komi ai abokiyar zamana ce inaso insamu lada"muneeba ta saki baki tana kallon husnah mamakine da al'ajabi ya kasheta tabbas husnah ta warke rayuwa kenan yauga husnah ta warke ita kuma ga halin data tsinci kanta ta kwantar da kanta a kafadar yaseer tana hawaye yaseer na bubbuga bayanta cikin sigar lallashi husnah nata gyaran wajen momy da daddy suka turo kofar dakin suka shigo daddy ya kalli momy ganin yaseer da husnah tare da muneeba husnah na gyaran wajen momy ta jinjina kai cike da farin ciki taji dadin ganinsu tare da muneeba,
muneeba na ganin momy ta fashe da kuka tace "momy ke ki taimakamun in rabu da abinda ke cikina kinji?mahaifiyatace ta cutar dani"damm gaban momy ya fadi ta kalli yaseer ya kalli momy tare sukace "ta cutar dake?metayi ta cutar dake muneeba ki fadamun karki boyemun komi"ta kalli yaseer cike da takaici da tsananin son da takeyi masa da tausayi daya bata ta kasa magana sai hawaye da yake zuba a idonta kamar famfo daddy yace "muneeba ki fada mana meyafaru kinsan damuwarki dama?"girgiza kai tayi ta cije baki ta kalli yaseer daya kafeta da ido tayaya zata kalli tsabar idon yaseer ta sanar dashi cewar cikin dake dauke a jikinta ba nasa bane cikin boka ne?tayaya zata dubi tsabar idon daddy dayake matsayin mahaifinta da mijinta ta sanar musu da tayi zina da boka?ta fashe da wani irin kuka mai ciwo ta gagara magana mikewa tayi kawai ta shige bedroom dinta tana kuka mai ban tausayi yaseer ya mike yana fad'in"ki dawo ki sanar mana da abinda kike boyewa muneeba"dakatar dashi daddy yayi "yaseer ba haka akeyiba ka bita a hankali tunda tayi wanan furucin ka kwantar da hankalinka nesa tazo kusa zata fada maka sauran ma inaga mubarta ta kwanta dare yayi ko?"yaseer zaiyi magana take jiyo yunkurin Aman husnah a kitchen momy ta ruko hannun daddy jin husnah na amai "muje ko?mutafi mubar yaran nan suma zasuje su kwanta ne"ta jinjina mata kai kamar wani karamin yaro yasa kai ya fice tabi bayansa tana jinjina kalamai da maganganu da muneeba ta fada,
yaseer kuwa ruko hannun husnah yayi suka rufewa muneeba kofa suka wuce tsaye muneeba tayi a jikin window tana kallon yaseer rungume da husnah yana tarairayarta,ta gefen idonsa ya hango kamar mutum a windown muneeba ya juya da sauri ta saki labulen ya ganta ya girgiza kai cike da tausayawa da alhinin maganganunta da suke barazanar tarwatsa masa kwakwalwa haka suka shiga sashensu shiru sai karatun alkurani parlorn ma sun kashe wutar alamu sun nuna sun kwanta har sun wuce suka jiyo muryar ummah hadiza nayi musu magana "ya jikin na muneeba?ya kuka sameta"
yaseer yasa hannu ya kunna fitilar dakin haske ya gauraye cikin damuwa ya zayyanewa ummah hadiza komi dangane da muneeba da maganganun da take furtawq ta jinjina kai tace "tabdijan wanan abu akwai lauje cikin nad'i yaseer anya munafukar matar nan mai kama da shedanu batasa yarinyar nan gaba ta aikata wani abu da yazo yanzun yakeson zame musu masifa ba?"ajiyar zuciya da numfashi yaja ya sauke yace "yadda take maganganu ummah hadiza nafara ko kwanto akan wanan cikin nata"ummah hadiza ta jinjina Kai "gobe zaa zo da malam insha Allahu idan aljanune zai fada koma menene yana ganintw zai fada ka kwantar da hankakinka kaje ku kwanta rike matarka wanan laulayi nabata wahala kuje asibiti idan kun natsa saida safe"ta juya ta shige daki ya kalli husnah tadan zumburo baki tace "banason ganinka cikin wanan yanayin ina shiga damuwa nima banason damuwarka"murmushi yayi mata ya ruko hannunta suka shiga daki ya taimaka mata tayi wanka ya gasa mata jiki da ruwan zafi ya daukota ya koma yayi wanka yazo yasa jallabiyarsa ya gyara mata kwanciya ya tofeta da addua ganin tayi bacci yasa shima ya kwanta gefenta ya daga kansa yana kallon ceiling zuciyarsa cunkushe da tunani kala kala kunnuwansa har yanzun maganganun muneebw yakeji....ya mike ya shiga zarya cikin dakin yana kaiwa da komowa husnah ta motsa ganinsa yasa tadan tsorata ta kunna fitilar gefen gado "meya hanaka bacci?"tambayarta tasa yayi saurin juyowa ya hayo gadon yw rungumeta yana bubbuga bayanta "nakasa bacci ne maganganun muneeba ke barazana da kunnuwana da zuciyata cikin tattausan lafazi take lallashinnsa hade da kissa da har tajw raayinsa suka kwanta rungume da juna...
******
da sassafe hajiya rabi ta nufi sashen muneeba tana tafiya kamar akan iska ko ganin inda takesa kafarta batayi a kitchen ta jiyo motsinta da sallamarta can kasan makoshi tace "muneeba ya jikin naki?"jin muryar mahaifiyarta yasa taki juyowa tadai amsa amma ba a sake ba "muneeba fushi kikeyi dani muneeba?ni mahaifiyarki ko?wato wanan bakar dagar matar ta shiga ta fita tasa alhaji ya sakeni yanzun ke kuma kina gaba dani dubi yadda kika koma muneeba dik kin rame kin fige?"muneeba ta juyo a fusace ta kalli mahaifiyarta tace 'au kin damu da ganina cikin wanan halin ne ummah?bayan koma menene ya sameni kece sila?waye silar shiga tashin hankalina da rashin lafiyata?duba kiga yadda dakina yake karni da wari duba kiga yadda yseer da husnah suke shan soyayyarsu ni kuwa fa babu dama dik waye ya jawomin?"tana maganar muryarta na rawa idonta cike da hawaye ummahnta ta kalli cikin yayi kasa kasa can sosai dik ya rairaye kamar baa jikinta ba muneeba ta cigaba da magana "ummah saki kuma da daddy yayi mike kece sila ninayi nadamar binki da nayi muka sabawa Allah nayi nadamar biye miki da nayi kika jefani a rijiyar gaba dubu"ta fashe da kuka,
"ki kwantar da hankalinki ki shirya yanzun zamuje wajen wanda zai bamu magani yanzun kisamu lafiya ga kawata nan zuwa akwai wani boka tace idan mukaje bazamu dawoba batare da ya cire miki abinda ke jikinki ba"
ummah hadiza ne da hajiya saude suka nufo sashen muneeba da taxo da sassafe akan maganar zuwan malam kicibis sukayi da daddy da hajiya zainab zasuje ganin jikin nata suka rankaya,
muneeba cike da tsana take kallon mahaifiyarta tace "to bari kiji bazani ba koda zan mutu da cikin nan yanzun nan da kike ganina tuba nakeyi ina rokon Allah gafarar zina da kikasani na aikata da boka yasamun abinda ke cikina"cakkk daddy da su hajiya saude sukayi suna kokarin shiga ko wannensu cikin tashin hankali yake jin furucin muneeba na karshe ta cigaba da magana "tabbas kuma zan sanarwa dasu daddy cewar kece kikai silar samuwar wanan cutar a jikina ta hanyar saka boka yayi zina dani yasamun ciki in haihu shine yasamun ciwo"waigawa hajiya rabi tayi jin motsi a kofar kitchen din tsautsaye taga su momy hajiya saude da daddy da ummah hadiza....
cikin sauri yaseer ya shiga gidan tare da malam ya nufi cikin gida ya shiga bega kowaba sai sadiya dake fito da akwatunanta dana hajiya rabi yace "inasu momy?"a sanyaye tace"suna sashen muneeba"har yaser ya wuce ta tsaidashi "Dan Allah yaseer ka rokarmun alfarma daddy ya rikeni kaji?wallahi zan zauna dasu da amana"yaseer jin abun yayi banbarakwai ta zauna dasu dama korarsu akayi?ya kalli akwatunan bece komuba yace "malam muje sashen mara lafiyar dik suna can"malam yabi bayansu....
To mutanena masuso muyi savin number juna suyimun magana sanan akwai documents hudu nawa na zafafan labarai akan 1k meso tamun magana....
*WANAN LITTAFIN NA DUHU 300 KACAL ZAKI BIYA KI KARANTA IDAN BAKI BIYABA KIKA KARANTAMUN BANYAFEBA*
08036953516
07042277401
*SLIMZY*🥱
50
muneeba hawaye ke gudu a idonta bugun zucuyarta ne ya tsananta ganinsu daddy a tsaye dukkansu sun zuba musu ido hajiya rabi ja da baya tayi kafafuwanta sun kasa daukarta ta durkushe a kasa jagwab daddy ya kasa magana gumi ne kawai yake karyo masa kawai ya fashe da kuka yana nuna hajiya rabi jikinsa na karkarwa "Allah ya isa tsakanina dake rabi?yanzun dama shirkarki da rashin tsoron Allahnki har ya kai kisa yar cikinki da kika haifa tayi zina?rabi zina fa kikasa muneeba tayi da boka"yaseer wata juwa ce ta fuzgesa jin furucun daddy yana kokarin shigowa ganinsa sukai kamar an jefosa malam yayi sallama cike da natsuwa mazurai da idanuwa yaseer keyi idanuwansa sunyi jajir yana kallon muneeba ko kifta idonsa bayayi tamkar an dasashi yake tsaye itama shi take kallo cikin kuka ta sunkuyar da kanta kasa cike da nadama da tsananin tashin hankali ta durkushe akan gwiwoyinta cikinta ya zauna akan cinyoyinta tace "yaseer ka gafarceni na aikata babban laifi na aikata mummunan laifin da nasan bazaka taba yafemunba,dikda zuciyata da gan gan jikina basason aikata hakan amma zuga da kururuwa da busar iblis hade da wanan da nake kira mahaifiyata suka hadu sukai tasiri wajen karfafamun gwiwa na aikata zina da aurena na aikata mummunan aiki da boka matsafi, yaseer am sorry to say cikin jikina ba naka bane cikin boka ne wanda a yanzun haka bokan ya mutu ya mutu ya barni da cikinsa a jikina wanda banida tabbacin shin mutum ne ko aljan ko kuwa wata cuta ce?"tuni hawaye sun balle a idon yaseer dikda dauriya irinta yaseer da jarumta kuka yaseer ya balle dashi yana ja da baya hafeez ya rukosa cikin tattausan lafazi yace"comr on my friend bansanka da raunin zucuyaba kai jarumi ne wanan mummunar kaddara ce ta sauka a gareku wanda muneeba koba yar uwarka bace ta cancanci taimako da afuwa"
cikin kuka muneeba tace "ban cancanci afuwa da gafarar yaserr ba abinda yafi cancantata shine karbar hukunci daga garesa ko wani iri ne,dikda tsananin son da nakeyiwa yaseer ya zama dole in hakura dashi saboda Bai kamaceniba bai dace dani ba nidin ba macen data cancanci a zauna da ita bane,dik abinda ya sameni mahaifiyata itace sila ita ta jefa rayuwata cikin DUHU daga haske ta jefani cikin mummunan had'arin da na gwammaci mutuwa da Rayuwa"da sauri hajiya saude ta rike muneeba ta toshe mata baki tana kuka itama kukan takeyi "dik wadanan maganganun basu bane muneeba kidainayinsu ko a kalaman da mukazo muka tarar dake munsan cewar ba yin kanki bane uwace bakiyi dacen da ta gariba,tirrr da halinki rabi Allah ya wadaran halinki kin cucemu kinci amanarmu kuma sai Allah ya saka mana sanan kisan da sanin dik inda kike zamu nemoki mu mikaki hannun hukuma akan dik abinda yasamu muneeba kece "cikin kakkausar lafazi hajiya saude ta karasa maganar ummah hadiza tuni zucuya ta kawo mata wuya tana bude baki zatayi magana ta kasa kallonsu kawai tayi tw zare hijabin jikinta cikin fakon idonsu momy dake kuka a tsaitsaye sukaga ummah hadiza ta rufarwa hajiya rabi da wani irin duka ta hankada kanta jikin bango ji kake kummmm "matsiyaciya wallahi bazakicu bulus ba kafin kibar gidan nan kibar zuriar mu sai na canja miki kama"nushin hajiya rabi ummah hadiza keyi ta cukwikuye kanta cikin hijabinta ta danneta ihu hajiya rabi keyi cikin azaba "hadiza karki kasheni kada ki kasheni numfashina ki kyaleni ki rabu dani zainab kuyi mata magana kuna gani zata kasheni?"momy tana kokarin mikawa innah jinjiri daddy ya rukota "badai karbarta zakiyi ba ko?ai abinda ya kamaceta kenan dan idan nine wallahi na kamata kasheta zanyi har lahira kubarta ta canja mata kamanni kafin yan sanda suyi gaba da ita suyi mata nasu"cikin wani irin yanayi momy ta share hawayenta tana kallon yadda ummah hadiza ke kirbar hajiya rabi kamar Allah ya aikota tace"ummah hadiza ya isa haka dukan bashi bane maslaha"hafeez ya kama yaseer yana kuka ya fita dashi muneeba tabi yaseer da kallo tausayinsa ya lullubeta take taji wata tsanar kanta da tsangwamar kanta ta dira a zuciyarta cikin gyaran murya malam yayi wanda shi yasa ummah hadiza tana cafke da wuyan hajiya rabi ta dakata yace "dukan da koke koken bashi bane maslaha ki rabu da ita dukan bashi zai bawa yarinyar nan lafiya ba bashi zai goge bakin fyantin da uwarta tayi mataba dan haka kyaleta shine maslaha yanzun asan abinyi"...hankadeta ummah hadiza tayi bakin hajiya rabi ya tashi yayi zundundum yayi jajir idonta daya ya kumbura suntum fatar idon tayi baki goshinta kuwa jini ne kawai yake tsattsafowa fuskarta dikta kuje da jikin bango ummah hadiza wani bakin ciki ne ya tokare mata wuya ta fashe da kuka tace "fitar mana a gida zoki fita idan