Showing 60001 words to 63000 words out of 155384 words
Chapter 21 - YAR AIKIN KARUWAI 2 cmplt By Asma Baffa -www.sufinovels.com-.txt
Sahar tana goge Kwalla ta raka su Mami har mota suka bata abinda suka kawo mata tayi godiya ta koma ciki bata da bakin magana iyayenta sun gama da ita.
Mami tana komawa Nawaf ya tareta a Palo yana tambaya Yaya? Mami ta Mika masa waya tace ji da kunnenka shi yasa na maka recording sabo da Karka dameni,Nawaf ya kunna ya gama jin komai a kunnensa Sultana tace sai kaga ma irin wulakanci da suka mana wallahi Auta amma Sahar bata da laifi,Nawaf yace sai na Riga yar tasu aure inshallah auren huce takaici zanyi,Mami tace ko kai fa kayi hakuri ka nemi wata amma tare da bikin su Sultana za a hada da naka tun wuri ka nemo mace wlh ko mu zabo maka ni da Baffanka,Auta yace yanzu Mami ai dai sai ku bari na huce ko ku sanda na hadaku kuka shirya haka nayi muku? Auta zaiyi hawaye yace Mami daga cewa ina son aure shike nan sai kuce ko ban samu wacce nake so ba zaku zabo min Hakan yayi kenan? Baffa Shima ai ba haka mukayi da shi amma Yaya Nawwar shi kuka kyaleshi ya zaba ya darje ni sabo da bani da kudi kune zaku min komai shine ni za a min auren dole,Shut up Baffa ya furta da shigowarsa kenan yana murmushi yace Auta kana bukatar aure bama so ka fada wani Hali ka nemo to mun baka zabi kafin bikin Su Sultana Idan ba haka ba mu munyi maka mata ma,Auta bedroom ya shige kawai abinsa ya bar Mami da Baffa baki Bude
Cele tunda ta sauka take garari tana zaga unguwar ta rasa ina zata shiga har gari ya waye inda taji Kiran Sallah nan ta nufa,masallacin bangaren mata tayi tayi fitsari ta fito tayi Alwala tare da Sallah sannan ta fito taci gaba da tafiya har rana ta fito mutane ana ta hada hada,Cele yunwa ce ta ciyota ta shiga wani Dan waje inda ake soya kwai da tea,tana shiga tace da me Kwan a soya mata guda biyar,shi dai yayi mamaki mutum shi kadai haka ya soya biyar ya cinye,tace a hada da dankalin turawa sai bread da tea aka zuba mata komai,inda aka tanada na cin abinci ga me ci a wajen, nan ta zauna taci ta koshi tayi tafiyarta,balaraben yana ta Kiranta da larabci Hajja amma ina tayi tafiyarta sai da ya fito da gudu ya riketa Cele tana juyowa ta mareshi gauuu ta fara masifa da Hausa aikin banza na zaci ma a kawo Kaduna nake,jiya ai ta malali na wuce na shugo ta unguwar sarki ashe nan a unguwar Rimi nake ma Dan wulakanci zaka rike ni Abuja zan tafi,ta kwaso kudi da yawa ta watsawa balaraben tana masifa tace ku dama yan kantin Kwari baku da mutunci indai aka zo sarin kaya sai kunyi wulakanci aikin banza kano dinma zan bari gaba daya tayi gaba,tana tafiya taga masu gasa kaji ta karasa wajen tace akwai kifi na sukunbiya? Ko yan gezu ba Wanda ya kulata,ta dauki hanyar harami tana Maheerah Kiji tsoron Allah,Kaka ya dawo daga masallacin kaabah ya kwana yana addua a hanya yaci karo da mutane sun rufe wani waje wai wata ce a Nigeria ta bata sannan bata da hankali mahaukaciya ce,Bai San Cele bace yayi tafiyarta yace su karanta sai naje askarawa suyi ram Dani yanda nayi kiba nayi jajir Dadi haka nada ni ba.
Mutane suna ta zuwa inda Cele ta fadi tana birgima da Shure Shure tace cewa wlh sai na soya Awara.
Haka ba Wanda ya saurari Cele sai wata mace wacce ta Dade a kasar ta dauki Cele tana zagawa da ita gidajen takari mata da maza ko an Santa har ta zo laying su Kaka,lokacin Kaka juya baya a layin yana siyen kwai dafaffe wajen takari suka ga Cele ta kwace da gudu ta nufi wajen Kaka ta rukunkume shi ta baya tana murna tana cewa Kaka, Cele da karfi Kaka sabo da bai shirya ba ya fadi a kasa wanwar sabo da karfin Cele gashi ta wani yi tsalle a jikinsa,kaka ya juyo yaga Cele dinsa, ya fara cewa a'a a'a Cele ta ya rungumeta suna murna,lokacin Cele ta dawo hankalinta kanta ya Bude kwakwalwarta ta dawo dai dai,tsalle take tana murna Kaka ma haka ta saki kuka Kuma daga baya da ta tuna da Ahsan.
Tace Kaka yace Cele kyale labarin nan mu koma ciki kawai ya rike hannunta suka shiga lifter zuwa bangaren kaka har dakinsa,Zama sukayi a gefen gadon kaka Cele tace Kaka ji yanda ka sake yin wani kyau da kiba kayi jajir, kafar Kaka ta kalla tace ina kaushinka kaka? Yace ya gudu Cele dole kiga nayi ja ga Zaki ga maiko kullum a cikinsa nake Cele ta,Kaka mu sake rungumewa suka sake rungumewa da kaka karo na biyu sannan Cele tace Kaka Ina yini tana washe baki murna ta isheta Kaka ya amsa yace lafiya kalau 'yata ta kaina,kaka Nawa Cele ta furta,kaka ya saki shewa kamar mace heeeeeeey wuuuuuu ya Mika mata hannu suka tafa,Cele tace Kaka na bayan hannu mu tafa dukkansu suka juyo da bayan hannu suka tafa,Kaka yace Cele ni sai naga kamar kin kunkunbura wallahi kamar baki da jini inda kisan haihuwa kika yi Cele kalau kuwa? Cele ta tuna dake kwakwalwa ta dawo tace Kaka labarin dogo ne Kaka bakin Abba ne ya bini da yace sai nayi ciki,Kaka kirji ya dafe yace Dan ubanki ba dai kafa kika budewa wani ba.
Cele tace to ka tsaya mana kaji labarin, ta kwashe labarin komai da komai tun sacewarta har zuwa yanzu data gudo karshe tace Kaka makuwa nayi kaina sai naga ya juye na rasa a Ina nake,gashi nasan kowa amma abinda nake gani daban sai na ganni a garin Kaduna,anjima na ganni a Kano jiya ni a cikin dajin falgore na ganni,dazu fa sai na ganni kamar a sambisa Allah Kaka amma yanzu sai naji Ina ganinka na dawo dai dai kaka za ayi burar....Dani,sai Kuma ta tuna Ahsan tace Kaka yau dai jikarka tana son wani a duniya,Kaka yace Allah jikalleta waye me sa'a haka? Ahsan mana yanzu Allah sarki na taho na barshi bai sani ba,Kaka yace Idan ma Bai nemeki ba sai mu koma,ita kuwa Maheerah matarsa Allah yayi mana maganinta ta cuceki jikata,Cele tace ba komai Kaka kaddara ce sannan bakin Abba ya bini yayi min ma da kyau da cikin ya zube,Kaka yace ai ni yanzu farin ciki ya samu jikata ta dawo,Cele tace kaka ka bani labarinka bayan mun rabu,Kaka ya furta Allah ya takaita ni da aka so ayi farfesu na sau biyu ana siyar Dani kaka ya bawa Cele labarin taji tausayinsa tace wallahi kuwa da sun samu nam me auki kanka kadai kaka ya Isa ya cika musu tukun ya,Kaka yace to abu ne kamar fanteka,Kaka yace yanzu akwai kudi ki huta sosai kafin ki fara sana'a,Cele ta zumburi baki tace gaskiya mu koma Nigeria zama a nan baida amfanin face wahala da zubar da mutunci kadan ne suke dacewa gaskiya.
Hakane Cele amma saurayin naki fa a Ina zai ganki mu Jira mu gani,tace to Kaka ba sai in yana so na ba,bafa cewa yayi yana so na ba nice kawai nake sonshi kadan,ni ko bai zo ba kawai muci gaba da rayuwar mu a kyale shi,yace to Allah ya zaba na gari,Cele duk ta kumbura bata da jinin kirki.
Ahsan bai Farka ba sai washe gari sai da ya gama Shiri fes ya fesa uban wanka ya fito ya zauna a Palo yana jiran Cele shuru,shuru har rana tayi nisa 12pm tashi yayi ya leka dakinta wayam,ya fito ya Bude daya dakunan amma shuru,gidan ya duba ko Ina wayam ba kowa,hankalinsa tashi yayi gaba daya mussamman da ya tuna fa a rude take bata da lafiya ga rashin jini a jikinta ga magungunanta ta barsu,hankalinsa yayi mugun tashi ya fito cikin sauri ya shiga bakar motarsa yana bin layi layi yana dubawa amma Babu alamarta,rasa inda zai sa Kansa yayi gaba daya,parking yayi a gefen hanya ya kifa Kansa a saman sitiyari ji yake kamar yayi hauka,Innalillahi wa Innayhirajun yake furtawa kawai kafin daga bisani hawaye suka fara sintiri a kumayunsa,hankali ya tashi a fili ya furta da larabci bazan iya rayuwar ba sai da ita, directly ya wuce gidan su Maheerah yana zuwa akace Maheerah tana wajen aiki iyayenta sun zaci biko Yazo sai kawai ya Mika musu takardar sakin da ya Dade da rubutawa bayarwa ne baiyi ba sai yau ya mikawa mamanta yace Idan tazo a bata,mamaki ya kamasu suna tambaya ko lafiya yace lafiya lau kawai na saketa bana bukatar sake ganinta a rayuwata na tsaneta,dama makantar karya nayi bayan na kamata da idona. Yana gama fadar haka ya juya ya bar unguwar,gidan abokinsa Husam ya nufa ya nemo shi yana bashi labari suka tafi can garin Makkah ko zasu dace.
Cele kuwa akwai kudi a wajen Kaka cewa tayi kawai Kaka mu koma gida Nigeria,Kaka yace a'a an kusa fita aikin hajji ki tsaya Idan muka sauke farali sai mu koma gida lokacin Idan saurayin naki Yazo shike nan,Cele tace ina sonsa amma ni wlh bana son zama a nan Sam ni bazan iya aurenshi ba gaskiya sannan Kaka jikinsa yayi ja da yawa kullum na dinga ganin Jan nama,dariya Kaka yayi yace yanzu akwai kudin da aka bani sadaka muci dadinmu muyi tsaraba ana gama aikin hajji mu gudu kasar mu,Cele tace gobe sai na samu gidan da mata suke na zauna a can ko? Kaka yace kwarai kuwa ai zamana a nan na Saba da mutane da yawa amma yau kwana zamuyi muna hirar haduwa,ai kuwa kwana suka yi suna Hira suyi bacci su Farka Cele tayi shimfida a kasa Kaka yana saman Katifarsa su biyu ne a dakin dama kaka kudin da ya samu daki ya samu shi kadai yana jin dadinsa.
Washe gari da yamma Kaka da Cele suka yi wanka suka fito gari Cele murna ta kamata yau gata ga kaka ta rike Hannun Kaka suna tafiya harda cewa Kaka ba'a wakar soyayya a Makkah ne? Kaka yace Ina fa akeyin soyayya kina kusa da dakin Allah sai dai wakar yabon manzo, Kai zan yiwa Kaka masoyina,wajen Taron askarawa suka karaso wajen da motarsu suna tsokanar Kaka da larabci sabo da kaka ba laifi ya iya da yawa sabo da yawonsa,tambaya suke yarsa ce? Yace ae,suka dinga cewa suna son Cele,haka da suka je ma kanti Cele zata siyi kayan sawa kowa yace ga kudi Dan Allah yana so a bashi ita zai aura,harda masu alkawarin Sarkokin gold ganin Yan Nigeria mayun kudi da Gold ne,suna hanyar dawowa wasu askarawan sun fito Kame cikin sirri,Kaka ya gane yace Cele gyara kafarki wancen kame sukeyi wlh,ai kuwa sai gasu sun biyo su Cele suka take a million Cele mamaki irin gudun Kaka yake ya fita gudu ita da take sabon jini ma,da mota suka biyo su Cele suka bi ta lunguna ga kaya Kaka ya rungume Wanda suka siyo,wani me shegen gudun tsiya ya kama abayar Cele tana juyowa ta masa wani shegen Elbow da gwiwar hannu ya saketa ba Shiri ya tsuguna a wajen yana Sosa hancinsa ya sake harzuka yace ba komai ai ana gama aikin hajji za ayi kazamin kame har gida gida bakake zasu shugo sai sun koma kasarsu,yace Cele zata ci ubanta Idan ya kamata ai sai an kaisu sijin inda ake cewa kurkuku Idan suka kama mutum sai an fara kaishi can kafin Nigeria to sai ya sa an gana mata azaba tunda ta masa wannan dukan.
Cele gidan su Samira Kaka ya samo mata wajen kwana su uku ne duk daki bai San Yan madigo bane,Cele ta tafi da kayanta gidan wasu manyan mata ne a gidan sunfi shekara ashirin a can suna matukar jin larabci su kansu takari dake gidan basa Hausa sai jefi jefi larabci suke yi,Samira ma zama a ciki yasa nan da nan ta iya larabci sosai, Cele tana zuwa tayi sallama wata Hajiya wacce itace ta samowa Cele wajen kwana ta amsa tace bakuwar alkhairi barka da zuwa ta nuna mata dakinsu da gadonta a gefe, dama sun biya kudin da komai.
Matan gidan sai kallonta suke suna lashe baki sai kace mayu,Cele tace wai Meye haka ne kamar karnuka sai wani lashe lashe kuke ba tsofaffi ba ga yaran kalau? Kafin ta rufe baki taga Samira dakinsu Daya,dama tare suka zo kasar,Samira tace Cele wai kece? Kin ganeni wacce muka zo kasar nan tare,na ganeki Kuma ai naga kin koma fara ne kinyi wata kiba,Samira tayi dariya tace uwar sana'a ke Kuma gani nayi kin Kara budewa kin Dan kumbura Kuma gaki fara kin Kara yin wani jakin fari tas anya kuwa Cele kina da jini? Cele tace naje asibiti suka ce jinina yayi kasa sunce na koma a rubuta min maganin na bar Riyad na dawo nan,Samira tace tab ai jini ba abin wasa bane akwai wata likita tana nan takari ce zan rakaki ta rubuta Miki magunguna ba a wasa da rashin jini,Cele tace na gode.
Tunda Cele tazo sai dai taji suna ta larabci sun San bata ji amma Basu mata Hausa ko ta gane ko kar ta gane sai dai tayi ta tambaya tana cewa me akace sai a fassara mata a haka take koyo,da Samira suka je wajen likitar ta duba Cele tace sai kace wacce ta haihu, Cele tace ko daya ta boye labarinta ta dai rubuta musu maganin suka je suka siya ta dawo tana Shan abinta.
Ahsan ya dira a garin Makkah tare da abokinsa a airport wani driver yaje ya dakko su Dan uwan Ahsan ne babban mutum ne amma shi a Makkah yake zaune, Hotel ya kaisu suka kama dakunan shi da Husam sannan ya kawowa Ahsan mota dalleliya me kyan gaske sabo da zasuyi amfani da mota dole sai da driver Wanda ya fisu sanin garin Makkah, shi yasa aka hada su da wani bakin fata bahaushe ne amma haifaffen garin Makkah ne yana jin both Hausa da larabci,mota suka shiga bayan sun sha Shiri Husam yana gaban mota Ahsan ya kame a baya ya wani harde kafa sanye cikin jallabiya fara Kal me tsadar gaske,takalminsa baki agogonsa baki me tsada sai uban kamshi da sheki yake,gashin ya sha gyara
Baso kuwa Salma ya kwalawa Kira ta fito jikinta yana rawa yace kinga bana son hauka ko baki ga gidan nan ba ruwa bane? tace na sani zan ebo ne,uban me kike yi da baza ki cika gida da ruwa ba,ki tafi tun wuri ki Tara ruwa banza shashasha wa ya sani ma ko tsuntoki akayi za a hadani dake ace na aureki,ke Dalla tafi can uban me zan ci dake bana sonki,Salma ta fara hawaye ta tsani ace Baso baya sonta ko da wasa,ba wulakancin da dukan da baya mata amma indai Baso ne ko a jikinta,baza ki wuce ki tafi ba kin tsaya kina kallonsa bakar yar iska ya kai mata wani duka Allah yasa ta fada daki da gudu ai kuwa ya rufa mata baya ya hau jibgarta yana cewa Dan uwarki ni kike yiwa kallon Soyayya? Salma tana ta ihu tana bashi hakuri tace wallahi bazan sake ba kayi hakuri.
Mahaukacin da suke taimakawa shine ya shugo dakin da rarrafe yana jan kafar Baso alamar ya bari,Baso juyowa yayi yaga mahaukacin ne dama ya Saba Idan yaga suna fada Yazo ya rike kafar Baso,Baso da maganar Yan daba yace na hakura na hakura Uban gidana ka fada mata kar ta sake yawwa bana sonta ni ya juya ya fice,Mahaukacin ma da rarrafe ya fito ya shiga harkarsa aka bar Salma tana kuka har ta gaji ta fito ta tafi ebo ruwanta tana hawaye ta gaji da aiki amma ya ta iya.
Yayan Salma wato Umar Baso kullum sai ya Kira Auta akan Business dinsu,Shi Auta ma karatunsa yake ko bi ta Kansa bai yi sai dai yace zaizo ne.
Cele kuwa tana kwance tana bacci fasikan gidan wata tsagera Meenal dakinsu Daya da Cele da Samira,ta lallabo jikin Cele tana shafa mata gashi ta gangaro Wuyanta,Samira ce ta Farka tace da larabci wallahi Idan ta Farka ta kamaki Zaki ci ubanki yar tijara ce na Santa sosai bata da mutunci Idan ka shiga sabgarta ki kama kanki tun wuri gwara ma ki dawo muyi abun mu yanda muka Saba,Meenal tace ni ita nake sha'awa yanzu Kuma sai na sameta ta juyawa tana shafa gashin Cele ta wani zaro harshe, kirjin Cele ta gangaro tana shafawa Cele ta zaci mafarki takeyi tana cewa Ahsan Dina ya Isa haka,farkawa tayi jin ana kokarin dage mata riga tana bude Ido taga ba mafarki take ba macece yar uwarta take taba mata jiki sabo da asara, Cele tashi tayi zumbur ta dura wata ashar ta mike tace yau za fitar da gawa a gidan nan....
Kuyi hakuri Fans jiya ban gama nutsuwa bane shi yasa ban baku ba, dole ce ta sa,ayi hakuri.
Duk naga masu tambayar ci gaba,masu tambaya ko lafiya da masu Text da masu Kirana na gode na gode Allah ya bar kauna
Mayyata MRS CHIEF Ina godiya kinji dai ME ASMA da kunnenki๐คฃ๐คฃ๐คฃ๐คฃ
Domin Karanta cigaban wannan labari ku danna bulun dake kasa ko kuma Hoton ๐๐๐
https://aihausanovels.com.ng/hausa-novels/yar-aikin-karuwai-book-2-page-76-80
๐๐๐๐
AsmaBaffa
08061929616[8/15, 9:28 PM] AMINA KABIR CAPS: ๐ผ'YAR AIKIN KARUWAI 2๐ผ
MATAFIYA
Book2
46-47
Official
By
AsmaBaffa
SADAUKARWA GA
ZAINAB USMAN
Page naki ne
MAMA GEE
godiya ta mussamman
BINTA UMAR ABBALE
Gingina ga me karanta Audio na books dina
HAUWA S ZARIA
*MISKI 3in1 Alfirdaus*๐น Albishirinku๐ original miski daga *Egypt* miskin da koda yaushe Kuna yabawa dashi yana dauke 1.*Musk oil* ana shafawa agaba