Showing 78001 words to 81000 words out of 155384 words

Chapter 27 - YAR AIKIN KARUWAI 2 cmplt By Asma Baffa -www.sufinovels.com-.txt

19 Jun 2024

51316

yanzu ki karbi rabonki? Matar tace a'a ni wani ne ya aiko ni yace a kawo Miki wai naki ya fashe gashi,Cele ta karba sak irin na awararta,tana mamaki tace waye wannan haka ni ba mashinshini ba tunda nazo garin nan banyi masoyi ba sai Yan madugo,Matar ta bude baki tace Subhannallahi Allah ya shirya su ashe ba Neman kudi suka zo ba lalata suka zo yi kusa da dakin Allah wallahi irinsu ke bata wasu gaba daya ake mana kudin goro,duk sun bata gari ana kallon takari marasa daraja,Cele tace ai mutanen banza ne wallahi da dare haka suke lalubeni wata tsinanniya ma ta taba min albarkatun kirjina Ina bacci ai kuwa na tsine mata albarka zata gani Kuma,Matar tace Allah ya shirya wannan ba gidan zama bane in kin samu dama ki tashi,Cele tace so nake dukkansu na koya musu darasi gasu nan har tsofaffin banza.


Matar tace to ni zan tafi,Cele tace wai bakar fatar ne ya baki? tace ae baki ne yace a kawo Miki zaizo yace,Cele tace to maybe a masu siyen Awara ne na gode tsaya na baki tukwici mana ta zaro riyal biyar tace ungo tukwici,haba sai kace yarinya tace Kya ci ko Altuffa,ko Laban wa buskota wai biscuits,matar ta karba tana dariya da godiya ta tafi.


Washe gari Ahsan wanka ya sha cikin kana nan kaya yasa Driver ya kaishi inda Cele ke zama tana siyar da Awara,yayi parking yana mota yana kallon Cele tana zuba ciniki,kudi ya bawa driver yace yaje ya siye awarar duka ya rabawa masu siya kyauta,Driver ya fita yaje ya samu Cele da Hausa yace Hajiya nawa ne dukanta? Cele tace duka Kuma botiki biyu fa,yace ae sadaka zanyi naga ana siya zan rabawa alumma Cele ta fada masa ya bata kudin gaba daya ta tashi tana gyara mayafinta bata San da mutun a motar ba taje jikin mudubin motar da Ahsan ke ciki a zaune tana gyara mayafinta ta zaro lipgloss a jaka ta shafa ta gyara mayafinta da tayi rolling ta jingina da jikin motar tare da harde hannayen ta a kirjinta,Ahsan yana kallonta shi fes ta ciki bakinsa ya dora a jikin glass ta saitin bayan Cele yana ta zuba kiss bata sani ba ji yake kamar ita yake wa kiss din,sai kissing din glass yake.








Hammad shine driver Ahsan,duk Wanda Yazo siyen Awara kyauta ake bashi ta dai dai kudinsa da zai siya,sai data kare tas ya bawa Cele botikanta ta karba tace na gode ta juya ta wuce gidan Kaka,tana tafiya tana irga kudinta tana Wakar larabawa ta Nancy ba uwar data iya kawai haukarta take fada , Ahsan yana binta da mota bata gane ba har gidan Kaka a kofar gida ta tsaya gidan dogon gida wajen Hawa goma sha nawa amma Cele haka ta dinga kwalawa kaka Kira,Kakaaaaaaaaaa kamar me Kiran Sallah,Kaka ne ya dawo daga masallaci da gudu tunda Cele ta ganshi da gudu tace to shegun Suna bayansa muke nan kullum a gudu sabo da kana kasar mutane itama kafin Kaka ya karaso tayi cikin gidan da gudu,Kaka ne ya shigo a hankali,tace Kaka sun tafi? Yace wa? Masu kame wanne kame Kuma wasa jini fa nakeyi ni sabo da na Kara kwarewa a gudu,Cele tace wallahi kaban tsoro na zaci askarawa ne wannan gudu haka haba Kaka,Kaka yace yau naji yar jakar Uba Idan ban fara koyon tsere ba sai yaushe,kina ganin garin nan irinmu gaba daya mun zama Yan tsere ba yaro ba babba ni yanzu motsa jikina zan dinga yi kullum da safe,Cele tace Kaka,yace Naam tace Ahsan din yaki zuwa yaki dawowa bakin Dan Iska wlh Idan bai zo ba sai na masa rashin mutunci muna yin aikin hajji zamuyi tafiyar mu,ni yanzu Number din Umma ce bani da ita bani data kowa,Kaka yace Allah ya kawo shi yar nan Cele ko aure kike so ne yanzu? Cele tace ae yanzu hankalina yayi wajen aure Kaka,Nima inyi Auren nan na shiga gwagwarmayar rayuwa,in hau gadona ni kadai na kwanta,Kaka in dafa abinda nake so kana gidana dakinka daban duk zani muna tare ko? Kaka yace ke kadai ma zaki kwanta a gadon haka ake auren,dariya Cele ta saki tayi dage da kafafun ta tare da dafa kafadar Kaka kamar sa'anta tace na sani Kaka ai na sani wai irin yar kunyar nan.
Allah ya kawo na gari tace Ameen.


Cele da Kaka suka fito tace muje mu fara siyayyar tsaraba kafin muyi aikin hajji mu tafi Nigeria ko,Kaka ya bita hannunta rike cikin na kaka suna tafiya tace Kaka Allah kayi kumatu duk ramarka ji yanda ka Dan ciko,Kaka yace Madara wasa ce? Zaki da maiko ba wasa ba Yar nan baki ga nayi kiba ba,ke kuwa har yanzu kumburin nan bai barki ba Cele ko sai an Kara Miki jini ne? Cele tace Alla ya kiyaye inshallah zan murmure ai akwai abinci me kyau, Shagon da suka shiga suna siyayya Cele tana ta jidarwa Ummanta kaya da Yan uwanta sai gani suka yi masu kantin sun shigo sunce komai ya musu su zaba an biya kudin,Cele tace waye haka ne? Kaka yace oho ke bari na gwangwaje kaina nima cewar Kaka ya dinga jidar kaya Cele ma haka masu tsada tunda sunji ance komai su zaba an biya sai da suka gama sannan aka shirya musu a Leda suka tafi,Ahsan yana ta jin Dadi ya riga ya biya mu su,suna tafiya a hanya sunyi nisa wani balaraben ya tare su a hanya ya Mika musu kudi da dan yawa yace sadaka bayan Ahsan ne ya aiko shi ya kawo,Cele ta Kalli Kaka tace adduar mu fa ta karbu a dakin Allah,lokacin kudinmu Yazo cewar Kaka,yace muje mu sha abin nan me sanyi iskrim yake ko me,Cele tayi dariya tace Ice cream Kaka,yace kune Yara mu Kam bakin mu ya gaji da miyar kuka tun muna Yara,suna zuwa wajen Ice cream din sai da suka gama siya zasu biya kudi wani balaraben ya shigo yace ya biya musu su je,Cele daga ji an biya tace Kaka ai kadan muka siya mu Kara,yace mu Kara zasu biya Allah ne yake ciyar damu,suka Kara da yawa aka ce nan ma an biya,Cele tace anya kuwa babu aljani a harkar nan,Ahsan yana bayan su basu sani ba suna juyowa ya juya baya ya tafi,sun zaci kawai wani balaraben ne,amma Cele tace wlh kamar Ahsan wancan Dan banga fuskarsa bane,Kaka yace ke wannan da gani ko a kasar nan me kudi ne Kalli ma kalar jallabiyarsa Kalli takalminsa,Kai Kaka Ahsan dinma haka yake,Kaka ya sheke da dariya yace Cele kina takari Zaki samu kalar wancen ko ta baya ka kalle shi kasan ba karya, ke dai muje a bar zancen,Cele tace shike nan tunda baka yarda ba amma shi Allah ba abinda ya gagare shi zai iya hadani ma da sarkin garin nan.


Salma ganin Auta kullum yana motsa jiki Exercise itama sai ta sa hijab tazo tayi ta gudu a can karshen gidan inda Auta yake,Bai kulata bata kulashi kullum haka suke yi da sassafe.
Bayan sati biyu yau Salma ta sha wanka cikin kana nan kaya ta tsula uban kyau,jean dogo sai Riga me kyau yau ba school, tana zaune ta harde kafa tana kallo, Mami ta fito tace kin fasa girkin ne? tace zanyi mana ai indai Ina gida ki Daina girki Mami zan dinga yi miki dan Allah,Mami tace to ba damuwa Salma,ta mike ta shiga kitchen ta shirya girki,zuwa yamma Wise ta shigo sai ga Auta ma anci gayu an dawo daga Office,Salma bata San Office yaje ba ta Kalli Auta kawai tace sarkin Mata Ina kaje mata Ina zaka mata,Auta ya Jita duk da a kasa kasa ta fada,yace na tabbatar Baso ba shi kadai yake Shaye Shaye ba harda ke ya hankadeta ta fadi a kasa , ya wuce bedroom,Salma ta fashe da kuka Dan ba karamin zafi taji ba, Wise tace Auta mene haka kuma ko juyowa baiyi ba,Wise ta daga Salma tace bakya jin magana Salma most you fight?,baki da gaskiya me kika fada masa naji kinyi magana kasa kasa,dama naji Rabi ta fada min abinda kike ma Auta bafa sa'anki bane sai kace ba wayayya ba,yaran yanzu ma da suka waye ai anci gaba,Salma tana goge hawaye tace Baso na ni ya maidani wajen baso na,Auta ne ya fito yace kutmar ......Baso....durun....Baso ya dinga durawa Baso ashar dake da Baso duk kunci kutmar .....Auta ya haukace wa Salma yace Ina daga Miki kafa bakya gani wai ni an fada Miki sonki nake yi ko dan baki San ta ya na kawo ki nan ba,wallahi baki Isa kin kasheni ba,kinyi kadan bakin cikinki ya kamani ke din banza village girl,Wise tace haba Auta mene ne haka,yace wannan da aurenta gwara yar Babydoll ta wasan Yara yafi min,ko naje na auri teddy wallahi da naga dama sai na fatattaka yarinyar a bed tana ganin sa'anta ne ni,Duk fadan da Auta yake a banza domin Salma ba jinsa take ba fitowa yayi ba Riga ta tsura masa Ido ta shagalta da kallon surarsa,Wise tace Kai Auta zan Kira Mami,Auta marin Salma yayi kadan yace daina kallona Mannerless,kumatunta ta dafe ba zafi ma ya mareta amma ta dinga kuka tace baza ka samu aikin gomnati ba a kasar nan, ko waya sai dai a siya maka Idan Ina nan duk inda kaje nema sai naje na hana,ke kike tunanin aikin gomnati nake nema Wanda ya dogara da gomnati shine a wahale,daga wajen aiki nake dan kiji na fada Miki mugun nufinki ya biki,Salma tana Shure Shure tace baza a biyaka ko sisi ba zaka gani aikin banza kake zuwa,Auta daki ya shige ya bar Salma tana kuka Wise tayi tayi akan tayi shuru taki,gajiya Wise tayi tace ke kan uwarki nace yar iskar yarinya wlh yanzu na tattakaki wa Zaki rainawa hankali Dan...Wise ta zundumo mata ashar, tace ke Yan iska ne mufa na can ciki Idan ban ci uwarki ba shegiya nake wlh sai na Miki dukan tsiya na rantse da Allah,Cinnaka ce ni ba ruwana dana gida bar ganin muna mutunci akan Auta wallahi duk sai na tattaro su Miracle mu yagalgalaki shashasha wacce bata San me take ba,yar kauye Kya zo nan ki mana hauka,Salma tayi mukus Wise tace wlh kina magana sai na kwada miki Mari duk nan da kike gani lafiya muka samu mun fiki hauka da kwaya,bariki Zaki nuna mana keee lallai tab,kyaleki yayi shi yasa kike iskanci,Wise ta fisge wayar Salma tace bari na Kira Bason a fada masa shi ya dauki mataki baza mu lamunci wannan ba,ke ko kunyar mahaifiyarsa bakya ji,Kara fa take Miki tunaninki bata jin haushi ne? Kin san yanda take son yayanta kuwa tana kula dasu mussamman Auta,to ba a nan gidan ba wannan iskancin tasss zamu sauke Miki shi,Duban duniya Wise ta rasa sunan Baso tace me kika sa masa? Salma jiki ya dauki rawa tace Dan Allah karki fada masa wallahi zuwa zaiyi ya dakeni,ohhh nan Kuma an kyaleki shine kike baje mana iskanci fada min sunan ko na karyaki,tace My love,Wise ta bude baki tace da auren naki,ai Baso yace zai sakeni na koma wajensa muyi aure,Wise takaicin Auta ya kamata tace Shima Auta ko shashasha me zaiyi da wacce ba shi take so ba,ai gwara na gayawa Auta kawai ya nemo wata ya Kara aure,Salma da sauri tace better wooo ahhh a fada masa, Wise Baso ta Kira bugu Daya ya daga ya fara auno zagi yace ba nace ki daina kirana ba wai da aurenki kike kirana,Wise tace matar Babansa ce,Yace ahhh chansa ma chansa chansa dai,to ya kike ya akayi ne ko baki gane bane,Wise tace dare dare Oga yace ah Wallahi Dare sai barawo, wannan ai tamu ce to Dare Allah wallahi ashe kin iya gaisuwar mu,Wise tace Sa'a dai wallahi,Baso yace Ina gaida ki,na karba master,tace dama Salma ce yace ae,tunda aka kawota kaga dai tafi wata guda to wallahi tunda tazo ta buwayi mijinta gaba daya ci masa mutunci takeyi ba abinda bata fada masa, Baso yace bani ita Dan burar....aka mikawa Salma waya,jiki na rawa ta karba tace hello sai da Baso ya mata ashar tafi goma,yace abinda nace kiyi kenan? zanzo garin gobe Dan uwarki,wayyo na shiga uku tace ta kashe wayar,tace Dan Allah Aunty kiyi hakuri ki bashi hakuri, Wlh na Daina, Wise tace kije ki bawa Mijinki hakuri na fada Miki karamar yar iska,tsabar taurin Kai Salma bata je ta bada hakurin ba haka Wise ta wuce,Mami tana jinsu taki fitowa tace gwara ma Bason yazo a huta ta hana min Auta sakat.


Baso ranar motar dare ya bi,da sassafe ka rantse a garin ya kwana sai gashi,Auta yayi Shirin school itama ta fito Sumi Sumi sai ga Baso yayi Sallama Mami tana ji taki fitowa,Baso yana zuwa sallama yayi yace kuyi hakuri tana Ina,Salma ta saki ihu,Baso ya zaro belt din wandonsa ta koma bayan Auta Baso ya bita suka dinga zaga Auta, tana wayyo ka ceceni na shiga uku bazan Kara ba na tuba Dan Allah kayi hakuri ka yafe min iskanci nane ya jawo min,Auta kuwa Baso ya rikewa hannu yace kyaleta,Baso zai fisge yace Karka daketa,yace abinda nace tayi kenan,ke ni dake munyi Hannun riga,ba abinda na gaza yiwa yarinyar nan sabo da na fita hakkinta gata nan sabo da ita na hakura da sana'a muka siyar da gadon mu na siya mana Dan gida,Babu Wanda na bari yake zuwa zance wajenta sabo da kar ma a samu wani ya lalata ta,Ina so ta auri Miji na gari, ni ban cancanta na aureta ba,ban cancanta na aureta ba Ina ganin kamar na cuceta ne ma tunda ni nasan bana gari bane,shi yasa bana daga mata kafa Idan tace tana so na ni harga Allah a yar uwa na dauketa ba wacce zan aura ba sabo da ni ban cancanci Salma ba tana da hankali kawai tasa banzan tunani ne a ranta,Salma kiji da kyau ni bazan aureki ba ko kin kashe aurenki, bazan fada Miki ya mukayi da Auta ba amma Idan lokaci yayi zan fada miki,Idan Zaki zauna kibi Mijinki ki zauna ki yiwa kanki gata Allah yaga niyyata kuma ki sani nayi aure ma ni tuni sati biyu kenan amarcina nake ci,ya juya ya fice abinsa ko Sallama ba Wanda yayiwa.


Salma a wajen ta sulale a kasa tayi zaman Yan bori tare da dafe Kai,Auta yace tashi mu tafi school,baza'a je ba wayyo Allah na shiga uku na lalace Baso...Baso...Basooooo.....Auta dariya ta kwace masa ya dinga sheka dariya,tace Mugu azzalumi bazan taba sonka ba duk Kaine ka jefa ni a wannan Halin,Wise ce ta shigo fuska a murtuke tace Zaki tashi ki tafi school din ko sai nayi fatali dake,tashi tayi tana kuka wayyo Baso tana Jan Jakarta a kasa kiiiii wayyo Baso...wayyo...wayyo zuciyata zata fashe,Auta yace yar banzar zuciyar da zata fashe ma kowa ya huta jarababbiya,bata kulashi ba a haka ta shiga mota tace motar ma baza a rufe ba ta barta a bude,Auta ya fito ya zaga ya rufe ya shiga yaja mota har sukaje tana kuka tace wallahi bazan ji me Malamin zai ce ba bazan ji ba.


Ta fito tayi part dinsu idonta jajir ta zauna a class tayi zuru da Ido,Malami ne ya shigo Idan yayi magana aka amsa masa da yes sai aji Salma tace No Idan abin ace no sir ne sai tace yes wai ita bata ganewa bata ji ma,Malamin tambaya yayi a class aka daga hannu ciki harda Salma yana gama tambayar ta amsa tace is Baso,get out,ya koreta waje ta mike tace thank you very much sir ta fice,aka bita da kallo,har ta fice ta Bude kofa yace sorry sir I'm looking for Baso,are you mad who is Baso in this class akace babu,shi bai San ma suna bane,yace young lady what is Baso? Salma tace Baso Is Baso the most Handsome gentle man in the world,and also ...kafin ta karasa Malamin ya rufe kofarsa ma, fita tayi ta tafi can kusa da bangaren su Auta ta samu waje ta zauna tayi tagumi,Auta yana zaune ta jikin window yana kallonta,abu kadan zai juyo ya kalleta,kallon wajen window din tayi karaf suka hada Ido a hankali ya Kalli inda lecturer yake,taci gaba da kallonsa ita,sake juyowa yayi yaga tana kallonsa da sauri ta dauke Kai,shi yaci gaba da kallonta ta juyo kafin ta Ganshi ya dauke Kansa,ta tsura masa Ido Shima kafin ya juyo ta dauke Kai.


Auta yana aji ya Lula tunani har aka gama musu lecture Shima ya fito tana zaune taga sun fito yana tafiya yana kallonta ta dauke kanta karma su hada Ido,yana dauke Kai ta juyo taci gaba da kallonsa yana tafiya,wata macece glory tazo da gudu ta rungume Auta juyowa yayi yana balbale Glory da masifa yace Ina da mata na fada Miki ki faina min haka,zuwa tayi zata sake rungume shi ya zuba mata Mari ta dafe kumatu yaja tsaki ya juya yana masifa a ransa yace zata ja min wannan masifaffiyar yarinyar ta dameni ,Salma tana kallo baki ta turo gaba tace Ina za a hada wannan da Baso ai gwara Baso na mata ba wacce zata taba shi ta ja tsaki tace ballagajin Namiji me za ayi da irin wannan duk inda yake sai mata wlh bazai shafa min kanjamau ba,tashi tayi tana fushi ta fice daga Makarantar, Auta ya dakko motarsa ya biyota yana mata horn yace yar iska gardiyar banza sai wahalar dani take,aure Sam ba Dadi a ciki dama sai da Yaya Nawwar ya fada min ai gashi nan, da a baya Ina nasan wani tunani a rayuwa,na taba zaton akwai abinda zai iya hanani bacci a duniya,har na zauna Ina tunani sai wannan banzar, horn din duniya taki kulashi Idan ta koma Kuma ta fadawa Mami ayi masa fada.


Fitowa yayi da niyyar mammaketa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login