Showing 102001 words to 105000 words out of 169868 words

Chapter 35 - MAR'ADAM'S BOOK 2 COMPLETE DOCUMENT by Aisha Bagudu .txt

06 Nov 2024

10862

sanyaye ya fito yana kwallawa maryam kira yayinda mami tana nan zaune tana kallon tv tana cigaba da kora ruwan tea da sauri maryam ta sauko tana dubansa gabanta na wani irin bugawa da karfi muryarta a raunane tace “ yaya gani ?“meye haka ?me ya faru kuma ?itama tayi karfin halin tambayarsa har ya d’aga hannunsa ko me ya tuna ya sauke ya dafe goshinsa a fusace ya cire hannunsa ya d’an saci kallon mami ita kuma ta zuba masa idanu tana ji da ganin abinda zai faru maryam taja baya tana jin yadda zuciyarta ke rawa “meye wancan agaban mami ?ya sake wulla mata tmbya tayi shiru tana dubansa a tsorace ya zira hannunsa daya cikin aljihunsa yana sake yin magana a tsawace “meye haka ina magana kina jina ?abinci ne !”what ?!ya furta a tsawace .”




ta sake ja baya kar ya wanka mata mari dan a yanayin da yake kallonta babu sausauci “amman zaki iya bawa mahaifiyarki irin wannan breakfast din ? gabanta yayi wani irin mugun fad’uwa ya tsura mata ido hakan ya bala’i bata tsoro gbdy ya sake canza mata ya fara taku zuwa inda take tsaye tana yar kyarma tana baya baya yana biyota har sai data kurewa bango “wallahi ba da gangan nayi ba babu komai a store ne komai ya qare iya abinda muke dashi na bawa mami .” afusace ya d’aga hannu zai wanka mata mari cikin wani irin masifaffen tsawa yaji sautin muryar mami “wallahi idan ka ta’bata ban yafe maka ba .” cak ya tsaida hannunsa tamkar an dasashi zuciyarsa na tafasa cike da zafin zuciya ya sauke hannusa yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa sannan ya juyo ya soma taku cike da ‘bacin rai ya qaraso ya zauna kusa daita kamar mai neman gafara ya fara kame kame “umm umm ummm nace ba “kace me ?”shiru yayi yana kallon mami yayinda maryam tayi sauri ta haye sama tana wai wayensu “ina jinka adamcy ?”Kiyi hakuri sweetheart banji dadin yadda naga kina breakfast haka ba “ bana zama a gida bansan babu komai a gidan nan ba sannan wannan yarinyar bata fad’a min babu komai ba ya qarashe maganar kamar zai yi kuka.”




mami ta kallesa sosai ta gano halin damuwar daya shiga adalilin breakfast dinta, daman kuma tayi hakan ne dan ya gani numfashi ya sauke yana sosa keyarsa yana cigaba da kallon mami ahankali mami ta tabe baki “to ka bata damar da zata fuskanceka bare ta fad’a maka babu komai acikin gidan nan “?amman !”sai kuma yayi shiru yana runtse idanunshi .”amman me adamcy ?kai kanka kasan baka da wata kalmar da zaka fad’a min na yarda a matsayinka na magidanci baka bawa matarka wannan damar ba sam matarka bata da cikakken iko acikin gidan nan yadda kake nuna baka qaunar jamaa da yanuwanka haka kake nunawa matar aurenka ,kai kanka kawai kasani baka damu da damuwar kowa ba dan haka karka rainawa kanka hankali ka nemi daurawa yar mutane laifi “ta qarashe maganar cikin fad’a saboda halin adamcy baqaramin damunta yake ba ,shi mutun ne wanda babu ruwansa da damuwar jama’a sai dai kanshi da aikinsa ya kamo hannun mami ya soma rarrashinta “sweetheart Kiyi hakuri kema Kinsan yanayin aiki ne sai ahankali ,ni kaina bana samun time din kaina kamar yadda kika sani amman at least data fad’a min zan sa a kawo komai “ta bishi da wani mummunar kallo “wai yaushe ka bawa maryam wannan damar yarinyar nan haka take rayuwa cikin qunci acikin gidan nan ga rashin so ga yunwa dame zataji ?”allah sarki maryam baiwar allah allah dai ya qara miki hakuri amman na cuceki na hadaki da damuwa ,na hadaki da mutun mara kirki ,na hadaki da mutun mara zumunci wanda ko yan’uwansa baya so bare wata aba maryam wallahi adamcy baka da tausayi da amana nayi danasanin hada auren nan allah dai ya gyara maka wannan bakar zuciyar taka .”
Kuka yaci karfin mami .”




jikin ATA yayi mugun sanyi babu abinda ya tsana kamar hawayen mahaifiyarsa da bai da kamarta jin kukanta yake har cikin zuciyarsa ya sake matsowa kusa daita yasa kanshi akan cinyarta yana jin yadda zuciyarsa yake tafasa yana jin kukanta yana ganin laifinsa amman yafi ganin laifinta domin kuwa itace sanadin da yasa ya kasa sauke nauyin da allah ya daura masa sannan ya kasa mata biyayya ta matsawa rayuwarsa dayawa akan maryam ,shi kanshi baya jin dadin abubuwan dake faruwa ,jin kukanta yake aransa yana jin kamar yayi kuka .“
ahankali yayi amfani da karfin zuciya irin tashi ya fara bata hakuri da rarrashinta “sweetheart Kiyi hakuri nasan bana miki yadda kike so Kiyi min addua wallahi a shirye nake da na canza in zama mai faranta miki ,kuma wallahi ina son yan’uwana sweetheart wani dadi ne ya ziyarci zuciyar mami dan abinda tafi bukata kenan ta dade tana adduar ya canja .”




ya qara gyara kanshi akan cinyar sweetheart dinsa “sweetheart ki yafe min ko zan samu sausaucin abinda nake ji araina kada zuciyata ta buga sweetheart ,damuwa tayi min yawa wallahi ni kadai nasan halin da zuciyata take ciki a haka kamar lafiyayyen mutun ne amman sam ba haka bane mutun ne mai dauke da mummunar ciwo a qirjinsa da zaki barni haka babu nauyin kowa akaina zanfi ji dadin rayuwata sai dai zuciyata taji da damuwa daya amman yanzu damuwa tayi min yawa na rasa ya zanyi da rayuwata wallahi zan gwamaci mutuwa sweetheart akan rayuwar da nake .”mami tayi saurin saka hannu ta rufe masa bakinsa bata son taji batun zai mutu idan ya mutu tayi yaya ai ita babban burinta ta mutu ta barshi a duniya, tana shafa kanshi tana jin sonshi har acikin bargon zuciyarta “ki yafe min sweetheart “adamcy baka min laifin komai ba ban ta’ba rikeka araina ba kullum addau nake maka d’ana sai dai abu daya nake só kamo. ina son ka sausautawa maryam ka zauan da mace mafi cancanta ,maryam ta cancanta kowani nmj idan ya sameta zaka ji dadin rayuwa daita mace ta gari ya dago kanshi yana kallonta ya saka hannu shi ya rike kunnuwansa bazan iya ba sweetheart “but I promise you in sha allahu zan kawo miki matar da zan aura in sha allahu zan faranta miki zakiyi farinciki da zabina amman batun wannan yarinyar fa gsky sweetheart sai dai kiyi hakuri .he ending the talk with a smile .”




mami tayi shiru tana dubansa sam adamcy baya ganin girmanta baya tausaya mata duk son da yake ikirarin yana mata abaki ne bai kai har zuciyarsa ba .”shiru kawai tayi tana jin babu dadi ko kadan acikin ranta tana son zubar da hawaye amman data tuna irin matsifar da hakan zai jefa rayuwarsa da alamuransa sai ta fasa sai dai yadda zuciyarta take tukuki ta tabbatarwa kanta tana cikin tsannain damuwa akanshi, idan batayi gaugauwan kawar da hakan aranta ba shima wani bala’i ne ga rayuwarsa runtse ido tayi zuciyarta na shirya mata yadda zata kawo qarshen komai “Sweetheart me kike tunani haka ?”muryar ATA ne ta katse mata tunani , harara ta maka masa tana cewa “ina ruwanka da abinda nake tunani ?wayarsa ya ciro ya kira daya daga cikin yaransa ya bashi umarnin a shigo da komai na kayan abinci enough .”




Cikin kankanin lokaci aka dinga shigo da kayan abinci sai daaka cika store tab da kayan abinci babu abinda babu na amafani haka ma fridge tun a ranar komai ya sauyawa maryam sunci mai kyau ita da mami su sha mai kyua, sai abinda suka ga dama suka girka kuma basuyi wa ATA tayi ba shima bai damu ba tsabgogin gabansa kawai yake yi sai da yamma ne ya dan saci kallon mami yace “sweetheart ko zan samu irin coffee da kike min ?zaka samu mana amman a wajen matarka ba “tun da yaji ta fadi haka bai sake cewa um ba bare um um, ya cigaba da danna wayarsa maryam najin haka ta matso kusa da mami tace “mami dan allah Kiyi masa mana “wani kallo mami tayi mata na rashin zuciya irin nata ,mutun bai damu da kai ba amman kai kabi ka damu kanka akanshi “please mami ai kema kin iya kije kiyi masa ta rage murya sosai tace “idan nayi bazai sha ba amman muje muyi masa tare zai sha mami ta tsura mata ido kawai tana kallonta cike da tausayawa tare suka shiga kitchen din sukayi sai dai koda ta fito parlour bata gansa ba a d’akinsa ta sameshi zaune akan kujera yana amsa kira taja qaramin table din glass din dake tsakar dakin ta dora tray din akai ta tsiyaya masa acikin a cup tace “gashi !”ba tare daya kalleta ba ya dauka ya fara sha dan a bukace yake .”




ta juya ta bar dakin tana rufo masa kofa kwanan mami uku a gidan wanda hakan ya haifar da sukuni da kwanciyar hankali ga maryam har mamakin kanta tayi yadda yanayin jikinta ya canza, domin mami nayi mata duk wani abinda zai kwantar mata da hankali tare da kawar mata da damuwarta da zarar taganta cikin damuwa sai tayi duk abinda zata kawar da damuwar sannan hankalinta zai kwanta sosai take kula da cin abincinta mussaman ta dinga had’a mata fruit masu gyara skin da qara ni’ima ajiki most especially yankakkiyar ayaba da soyayyiyar gyada da kankana da madarar ruwa a had’a waje daya wannan kam kullum sai mami ta had’a mata ta bata ,wannan had’in mai dadi yana aiki abu biyu ne ajikin nmj ko mace yana gyara skin sannan yana qara ni’ima ajikin mutun. zaman mami a gidan ya dan kawo sauyi domin duk abinda ATA zai yi na rashin mutunci tana taka masa burki da fushinta domin dai idan ba fushinta ya gani ba baya kin abinda yayi niyya kuma yanzu babu laifi yana cin abincin gidan .”


Da misalin karfe shida na yammacin ranar da mami ta cike kwana biyar a gidan ATA ya tashi da rashin lafiya na ciwon kai mai tsanani wanda har sai da doctor dinsa yazo ya dubasa inda yayi wa doctor bayanin yadda yake jin ciwon Kan kuma koya sha magani baya masa sauki yadda yake buqata, doctor yayi gwaje gwaje ,a inda yace akwai kwayoyoyin da yake sha wanda sune suke haddasa masa wannan ciwon, dan shiru yayi yana tunani dan shi a sanin da yayi wa kanshi baya shan wata kwaya dama sigari yace itama yanzu ba koda yaushe yake shanta ba amman kwaya kam baya sha “doctor bana shan kowani irin kwaya amman ko zaa iya duba wace irin kwaya ce ?”eh zaa iya dubawa kuma zaa gano kowani iri ne amman dole sai kaajiye ayyukanka na gobe kazo hospital .” ATA ya gyda kai alamun zai zo .”




tun zuwan doctor maryam ta fahimci bashi da lafiya ne dan duk sanda kagansa to rashin lafiya ne bayan doctor ya gama duba ATA maryam ta shigo dakinsa hannunta dauke da tray ta sameshi zaune akan doguwar kujera yana sanye da singlet da gajeran wando kallo d’aya tayi masa ta dauke idanunta sakamakon yanayin data tsinci kanta d’an kwantaccen sumar jikinsa kawai ya isa tadawa mutun shaawarsa ,taja dan karamin table din glass din dake tsakar dakin ta dora cooler din abinci a kai ta zuba mishi a cikin plet tasa spoon tace “ga abinci shiru bai ce uffan ba ta sauke numfashi ta sake bud’e bakinta akawo maka coffe ?ya girgiza mata kai kawai alamun baya bukata wani sanyayyen numfashi ta sauke a boye a raina tace “alhamdulillah yau dai da alamun mutane kirki ne a kusa babu rashin mutunci,kamar baka jin dadi ?sannu allah ya baka lafiya meke damunka “?ba tare da ya kalleta yace “ki kama kanki dan naga kina wani jin dadi dan kinga sweetheart atare damu kisani ba tabbata zatayi a gidan nan ba zata wuce idan ta wuce kuma kema Kinsan me zai faru ?tace babu abinda zai faru sai alkhairi allah dai ya baka lafiya baby nah tana rufe bakinta daya daga cikin wayoyinsa ta soma ringin zuciyarsa cike da mamakinta karo na biyu kenan da ta kirasa da wannan banzar sunan kamar ya tashi ya gaugaura mata mari amman jikinsa babu kwari shine ma yasa ya qasa tashi kuma yana jin yadda zai ce tabashi wayar maryam ta fahimci haka, dan haka cike da sanyi jiki ta qarasa inda wayar take akan katifarshi ta dauko ta duba fuskar wayar nan take gabana yayi wani mummunan faduwa sakamakon ganin hoton wata kyakkwar yarinya a fuskar wayar mijinta .”




yarinyar kyakkyawa ce duk da fuskarta kamar zane ce aranta tace”ko dai wannna ce yarinyar mafarkin sa?kwakwaluwarta bata kai ga bata amsa ba “tajiyo sautin muryarsa can qasan makoshi yace “bani wayata “jiki a matuqar sanyaye ta kai mishi sañan tace bari na wanke maka toilet shi dai bai ce mata uffan ba har ta shiga ta wanke ta fito yana cin abinci yace “bani abinsha a fridge da sauri ta bude demsino na gwangwani ta dauko masa ta hado masa da ruwa nestle ta ajiye tana jin zuciyarta babu dadi duk da yarinyar mafarki ce amman abun ya damu zuciyarta zata cigaba tsayuwa ad’akin yace “please leave! simi simi ta fito daga d’akinsa yaja tsaki tare da cewa nonsense mace sam babu class ,to wani aji zatayi wannan ?allah na tuba ai isasun mata né masu aji shi yaji ajikinsa muddin zai had’u da princesa dinsa tabbas zata fita dabam acikin mata ranar da wuri ya kwanta bacci sakamakon maganin bacci da alluran da doctor yayi masa .”waahegari kuwa karfe biyu a office din doctor tayi masa duk wani gwaje gwaje anyi masa, inda doctor yace zai zo gida ya kawo masa abinda suka gani daga nan kai tsaye gidan mb yace a wuce dashi sun jima tare,bashi ya dawo gidan ba sai bayan ishai.”






Da misalin karfe goma sha daya na dare maryam ta fito daga dakinta sanye da kayan bacci iya cinyarta sai dai ta daura zani a saman kayan baccin kai tsaye d’akinsa ta shiga bata gansa ba dan haka ta sauko qasa cikin tsananin tashin hankali har zanin jikinta ya fita bata sani ba “yaya Adam kazo mami bata iya numfashi sosai ,ai da wani irin mugun sauri ya zabura ya mike yayi wulli da remut din hannunsa bai san yaakayi ba sai ganinsa a dakin maryam yayi har tsakiyar gadonta ya daga kan mami ya daura bisa kafafunsa yana qoqarin tallabota ya sauko daita ta girgiza masa kai “dan girman allah sweetheart wallahi baki san yadda naji a zuciyata ba “ke tsayuwar me kikayi kije ki dauko min wayata” yayi mgnr a tsawa ce yayinda maryam ta juya da sauri ta fita “haba adamcy ka dinga sausautawa maryam mana .tayi maganar da kyar”




furzar da iska yayi yana kamo hannun mami cikin nashi “adamcy nah! mami ta kira sunansa”na’am sweetheart sannu gobe gobe nan zan bar kasar nan dake “duk inda zaka kai ni bazai hanani mutuwa ba ,dan haka ma gara ka barni kawai a kasata idan mutuwar ce allah ya bamu ikon cikawa da imani ta qarasa maganar da kyar tana sauke numfashi “kinji abinda naji kuwa sweetheart da kikayi zance mutuwa nan dan girman allah ki daina fad’a min haka “to adamcy mutuwa ai dole ce maryam ta shigo ta mika masa waya ta hawo har saman gadon ta riko hannun mami cikin nata suka sakata a tsakiyarsu mrym tana mata sannu yayinda ATA Ke qoqarin kiran layin Aunty shahida “karka kira shida ka daga mata hankali sannan kiranta bazai hanani mutuwa ba idan mutuwar ce.” saurin runtse idanunshi yayi .”




Bai kula maganar mami ba ya cigaba da kiran layin shahida sai dai kiran na shiga bata d’auka daga adamcy har maryam duk suka zubawa mami ido hankalinsu a matukar tashe “maryam adamcy ku yafe min had’aku aure da nayi “haba mami dan allah kiyi shiru numfashi ki har yanzu bai daidaita ba kuma aurenmu da kika hada baki mana laifin komai ba inji cewar mrym “idan Ke ban miki laifi ba ai nayiwa adamcy “ki kwantar da hankalinki mami shima baki masa laifi ba muddin muna raye zai faranta miki har ma bayan ranki “shi kam ATA gabad’aya ya nemi natsuwar ya rasa dan har layukan mijin aunty shahida ya kira bai zuwa haka ma layin likitan dake dubasa yana qoqarin durowa daga kan gadon mami ta riko hannunsa ya dawo ya zauna cikin tsananin tashin hankali “dan allah sweetheart karki bari sanadiyar careless dinki na rasaki,wallahi bazan iya daukar zafin jarabawar nan ba “yayi mgnr kamar zai yi kuka “ haka rayuwa ta gada adamcy kuma ita rayuwa cike take da qaddarori da jarabawa iri iri sai dai idan baka cikin duniyar nan, yau dadi ne gobe kuka dukkanin rayuwa rubutattacen lamari ne daga rabbi da d’an adam yana gane wannan da bazai tsaya batawa kansa lokaci ba kamar yadda ka kasa ganewa “tana gama fadar haka idanunta suka juye numfashinta ya soma qoqarin tsayawa .”






“sweetheart sweetheart!! Kawa yake iya kira yayinda maryam ma ta dinga kuka tana kiran sunanta atare suka nemi durowa daga kan gadon suka jiyo sautin muryarta can kasa “maryam bani ruwa kishi nake ji .” ya dawo da sauri yana cewa “shikenan sweetheart mutuwa zakiyi ki barni ,dan allah karki min haka sweetheart, dan girman allah karki min haka ya allah ka d’auki rayuwata ka bar ta mahaifiya ta” ya fad’a yana damke hannunta cikin nashi gam wasu hawaye masu zabi suka gangaro masa “adamcy Nah kuka kake yi ?ya sauke numfashi yana kai hannunta bakinsa inda hawayensa ke diga “kayi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login