Showing 120001 words to 123000 words out of 169868 words
Chapter 41 - MAR'ADAM'S BOOK 2 COMPLETE DOCUMENT by Aisha Bagudu .txt
shi kasuwanci tattalinsa ake. bana son kabar wata kofa da wasu zasu samu damar janyo mana asara dan bazan ɗauki asarar ganganci ba” “shikenan zan haɗa taron gaugauwa ranar monday zan yiwa P.A ɗina magana, zamu san abin yi kafin matsalar tayi nisa” ATA ya jinjina kai sannan ya buɗe wani file ya duba bayan ya gama dubawa ya miƙe “ni zan wuce” ammar ya jinjina masa kai a sanyaye atare suka fito .”
Can ɓangaren maryam kuwa kuka take sosai abun ya haɗe mata tana kallon nana hauwa'u ta miƙe ta yafa mayafinta tana yiwa Mami sallama “kema wucewa zakiyi ?” “eh Mami yaya hisham yana jirana” “to ai Shi kenan Allah ya tsare hanya” mami ta fada ranta a dagule saboda ganin ya’yanta sun hadewa mrym kai ,nana hauwa’u bata kalli in da maryam take ba ta nufi ƙofar fita, takun maryam taji abayanta tana magana cike da raunin maryam tace. “sister kema fushi zaki yi dani bayan kinsan kece ƙarfin gwaiwata” juyowa tayi ido cikin ido suke kallon juna “kiyi haƙuri sister nayi kuskure” nana hauwa'u tayi murmushi tana kallon cikin idanunta “shi kenan komai ya wuce Allah ya inganta mana babynmu” jiki a sanyaye sukai sallama tana jin kamar zata rasa rayuwarta ne dan gbɗy jin tana ɗauke da cikinsa bai saka zuciyarta samun natsuwar ɗari bisa ɗari ba ta dawo kusa da Mami ta zauna “ki rabu dasu karki wani ɗaga hankalinki akan ɗan wannna abun” Maryam tace. “allah Mami hankalina a tashe yake su aunty shahida sunyi fushi dani” “zan kirasu babu abinda zai faru ni dai fatana ki kwnatar da hanaklinki kar wani abu ya samu cikin jiknki”
Numfashi ta sauke sannna tace. “Mami dan allah karki faɗawa yaya batun cikin nan tukun Kinsan halinsa” Mani tace. “kai babu abinda zai yi sai farinciki aj wannna cikin sai ya kawo miki sauy arayuwarki Maryam tace. “ walalhi yadda yaya baya sona bana tunanin zai so abinda nake dauke dashi Shiru mami tayi tana sauraronta “ai kuwa da Adamcy bai kyauta mata ba idan yaki abinda mrym take dauke dashi “ko kuma za'a iya ƙin fad'a masa har ya gano da kanshi” kai kawai mami ta gyda mata ahankali mami ta dinga janta da hira sai dai jikin Maryam a mace yake kana kallonta zaka fahimci hakan.
A galabaice ya shigo parlour'n mami ya zauna tare da runtse idanunshi gam mami dake zaune ta tsura masa ido ruwan bala'i take son sauke masa amman yanayin yanda ya shigo yasa tayi tunanin kar ta masa faɗan sai tasa aka kawo masa abinci buɗe idanunshi yayi ahankali yace. “gani sweetheart ina son na wuce gida na kwanta na huta” mami tace. “kaci abincin da akawo maka tukun sai muyi magana” kaɗan yaci abincin sannan ya tsurawa mami ido yana son yaji kiran me take masa suna zaune sai ga maryam ta fito daga ɗakin mami jiki a sanyaye ta zauna kusa daita wani mugun ɓata rai yayi “Adamcy!” mami ta kira sunansa ya ɗan kalleta tare da faɗin. “ina jinki sweetheart” mami tace. “me yasa kaci zarafin Maryam a gaban ƴaru'warta?” baƙaramin fusata yayi ba shi kam bai san randa mahaifiyarsa zata barshi ya huta da maganar yarinyar nan ba “amma ajiye wannan maganar ma tukun, ka fita ka bar matarka cikin wani hali baka kira kaji a wani hali take ciki ba bare ka mata sannu da jiki” daga haka ya miƙe ya fice daga parlour'n dan bazai zauna ya cigaba da jin magana akanta ba “maza tashi ki bishi kuje zan zo wani sati sai na daukeki muje scan din “to mami na gode allah ya qara girma “Allah ya tsare da ɗan saurinta ta ɗauki mayafinta ta fito alokacin tuni ya shiga mota ta zagaya da sauri ta bude bangaren da yake ta shiga ta zauna suka wuce gida ."
Bayan kwana biyu da misalin ƙarfe goma kiran Ni'ima ya shigo wayarta tana kallo kiran na shigowa taƙi ɗauka sai a karo na biyar ne ta ɗaga tana ɗauka tace “lafiya Ni'ima kiran me kike min bayan kin kusan jefa rayuwata cikin uku bala'i ? babu ruwanki da duk halin da nake ciki zan gargaɗeki da babban murya karki sake zuwa mijina yace baya son ganinki a gidansa idan kuma kinyi taurin kai zaki gane ke ƙaramar mara mutunci ce” shiru tayi tana sauraron Ni'ima “ni dai nace karki shigo tunda kince saƙo ne daga umman zuru ki tsaya a wajen get idan kinzo zan fito na karɓa amman karki zo ” washegari kuwa da misalin karfe bakwai Ni'ima ta kirata ta fita cikin sanɗa kasamcewar ranar tun safe ATA na gida bai je koina ba wanda alamunsa Ke nuna tafiya zai yi taje ta karɓo saƙon umma zuru irin tukunyar farko da aka aiko mata dashi ne. cikin sauri ta shige ɗakinta dashi ta fito parlour'n ta zauna , tana zaune ATA ya shigo ya haye sama bayan Kamar mintuna talatin ya sauko yana fita, ta miƙe da sauri ta haye sama kamar a mafarki taga kofar ɗakinsa a buɗee wani kyakkyawan murmushi tayi da sauri ta faɗa ɗakinta ta ɗauko tukunyar ta dawo ɗakinsa ta tsaya tare da buɗe tukunyar tsafi ta soma ambatar sunanshi da abinda take son yayi mata kamar yadda aka fad’a mata bayan ta gama ta ajiye tukunyar ta ɗaga katifa ta ajiye a gefe, ta ɗauko tukunya zata saka taji taku tare da tafi daga bayanta ai da wani mugun sauri ta juyo ganinsa tsaye yasa ta saki tukunyar aiko nan take ta fashe sai ga wani mummunar hayaƙi ya shiga fitowa daga ciki .
Cikin zare ido yace “Meye wannan?” tambayar daya jefa mata kenan bakinta da jikinta ya kama rawa “kina son kashe ni saboda bana sonki ko?" Girgiza masa kai tayi tare da faɗi. “a'a ba kashe ka zanyi ba.." cikin daka tsawa yace. “shut up with your dirty mouth! you want kill me?” zatayi magana ya sake buga mata tsawa “shut up how dare you enter my room kuma riƙe da tukunyar tsafi?” nan da nan jikinta ya kama rawa “daman naji ajikina kina son kasheni” sake girgiza masa kai tayi jikinta na wani irin rawa “why you this girl ?me nayi miki da zaki kashe ni ? duk da bana sonki duk da yanda nake ji araina kamar na kashe ki na sha faɗa miki ni ne ajalinki amman na taɓa ƙoƙarin kashe ki?” jikinta na rawa ta girgiza masa kai “why you want to kill me ?” cikin rawan murya tace. “Wallahi ba kashe ka zanyi ba, ka fahimceni wallahi ba wata illa zan yiwa rayuwarka ba kawai dai..” sai kuma tayi shiru ta kasa ƙarasa maganarta “baki da abinda zaki iya kare kanki kije na sakeki saki ɗaya " .
mutuwar tsaye tayi cikin tsananin tashin hankali da matsanancin gigita jin furucinsa, yayinda hawayen idanunta ya ƙaru suka shiga kokuwa da juna gurin silalowa ga wani irin ƙyarma da jikinta ke yi, sai dai rawar da jikinta ke yi ya sanyata saurin durƙusawa a gabansa domin ƙafafunta sun tabbatar mata bazasu iya cigaba da ɗaukar gangar jikinta ba, baya ga haka ma ga wani iri jirin tashin hankali dake ɗawainiya da ita .Wani irin bugawa kanta ke yi tamkar zai rabe gida goma , cikin wani matsanancin rashin Hankali muryanta na rawa tace. “da gaske ka sakeni yaya adam? dan Allah ka janye sakin zan maka bayanin komai domin idan kana tunanin zan...” dakatar da ita yayi ta hanyar faɗin. “shiiii na sake ki kuma babu wanda ya isa ya sake takurani nayi rayuwa dake, dan haka ba abinda ya rage miki a gidana gari ya waye ki bar min gidans kuma bance kije gidan mahaifiyata ba, ki wuce gidanku gidan ubanki tunda ke ɗin ba shegiya bace” shiru kawai tayi tana dubansa cikin tsananin faɗuwar gaba domin dai a kallon da take masa ta rigada tasan bazai taɓa daina tsananta ba a cikin zuciyarsa” maganar sa ne ya katse mata tunaninta. “bazan taɓa daina tsanarki ba, abinda kika kasa ganewa shi so halitta ne..” cikin matsanancin kuka ta dakatar dashi da faɗin. “yanda yake halitta nima haka nake ji akanka me yasa zaka rabu da zuciyar da batasan sanda ta fara sonka ba ?sonka shine mafarin kasancewata a karkashin mahafi....” cikin daka tsawa yace. “bar ɗakin nan stupid! tun kafin nayi losing control , dan ina jin baƙin cikin kasancewata dake ahalin yanzu yayi maganar a zuciye cikin tsananin fushi da tashin hankali mara misaltuwa.”
bata bar ɗakin ba kamar yanda ya furta sai rarrafawa tayi ta koma gefen doguwar kujerar kushin ƙwaya ɗaya dake ɗakin ta rakuɓe , tana kallonsa ya miƙe ya shiga bayi batare daya cire kayan jikinsa ba saukar ruwa a bayin yasa ta fahimci wanka yake a hankali ta rike gefen kanta dake sara tana haɗeye wani ƙululun baƙin ciki tare da share hawayen dake tsiyoyo mata, ta tattara tukunyar tsafin ta kai dakinta ta ajiye ta dawo ɗakinsa ta zauna dan babu in da zata aurenta dashi mutu ka raba ya saketa amman bata saku ba dan tayi imani mami naji zata maidaita."Da mamaki ya fito ya isketa kallon mamaki da naci irin nata yake “zaman me kikewa mutane a d’aki ?” ya faɗa Yana kallonta “babu fa inda zani har sai ka maidani ” wani mugun kallo yayi mata sannan ya ɗauki jug din coffee da zafinsa wanda ta kawo masa bai sha ba ya dawo inda take ya juye mata tsab a jikinta wata razananniyar ƙara ta saka da sauri ta shiga kakkaɓe rigar dake jikinta , cikin faɗa wanda bai hana zazzaƙar muryarsa fitowa ba yace. “banace ki bar min ɗakina ba ?” Ya faɗa yana ware mata idanunsa dake cike da bala'i jikinta na rawa sosai ga kuma zafin coffee da yake ratsa illahirin fatar jikinta wanda har cikin naman jikinta take jin zafin, babu shiri ta bar masa ɗaki zuwa nata tana zubar da hawaye .”
ranar Maryam bata runtsa ba kuma tayi dauriya domin dai bata kira kowa acikin ahlinsa ba washe gari kuwa tun da asuba tabi mota zuwa abuja taso shiga jirgi amma saboda bata da kuɗin jirgi kamar ta tambayi mami kuɗin ticket amma tasan hakan zai sa ta gane akwai matsala shiyasa ta shiga motar haya
Tunda suka ɗau hanya kanta na kife ,rufe ido tayi sosai tana zubar da hawaye masu zafi sannan acikin ranta tana ƙissima yanda zata hana rayuwar adam samun kwanciyar hankali yadda bata ji dadi agidansa ba bazata bari Ya kawo wata yaji dadin rayuwarsa daita yadda gallazawa rayuwarta wallahi tayi alqawarin sai ya gallazawa duk wacce ta rabesa zatayi komai akan yanke masa duk wani jin dadin rayuwa .” ɓangaren ATA shima tana barin gidan ya bar ƙasar zuwa hollond .”
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 22
Kwanaki hamsin kenan da ATA yasa anemo masa kwararrun masu zane wanda yayi daidai da sauran sati uku daurin auren maryama da yaya sadam acikin lokacin nan babu abinda maryama take sai zariyar zuwa AGC domin gabatar da zanenta, haka zalika ta saki jikinta sosai da yaya sadam domin ta fara cire rashin son da bata masa tana ta qoqarin dasa soyayyarsa mai karfi acikin zuciyarta ,shima kuma bangarensa yana qoqarin kyautata mata shiyasa a yanzu damuwarta ad’auketa aiki akar ka shin AGC ne .” idan kaga maryama da yaya sadam a yanzu zaka d’auka tun asali masoya ne wadan da suka d’auki tsawon lokaci suna son juna, abu d’aya ne kawai dai har yanzu yake damun zuciyar maryama shine yawon shiru da shiga tunani mai zurfi da yaya sadam din yake ko suna tare ko yana shi kad’ai ko ayita kiransa a waya baya d’auka agabanta wanda ita hakan na damunta, kuma haka nan take ji ajikinta kamar akwai wani abu dake damunsa wanda yake boye mata , tayi iyakar qoqarinta tasan meye damuwarsa amman abun ya cutura domin dai abu d’aya ne kullum yake fad’a mata babu komai al’amuran aiki ne .”
mami na zaune a had’ad’den parlour’nta na farko idanunta na kallon tv yayinda hannunta Ke rike da casbaha tana ja ahankali kira ya shigo wayarta, tasa hannu ta d’auki wayarta tana dubawa sunan d’anuwanta data gani yana yawo a screen din wayar ne yasa tayi saurin kara wayar a kunneta bakinta d’auke da sallama “wani irin mikewa mami tayi jikinta na rawa tare da furta kalma “inna lillahi wa inna ilaihi rajiun ,ya hayyu ya qayyum bi rahmatika astagisu aslili shaani kulluhu wala takilni ila nafsin d’urfata’ai “kace yau kwana biyu kenan da faruwar sakin ?ta tambayesa cikin tsananin damuwa da shiga tashin hankali “yayinda cikin tsananin fushi d’an uwanta ya cigaba da sheida mata abinda ya faru .”“wallahi Abdul ban san komai akan sakin nan ba”
ta fad’a jikinta na wani irin ‘bari haka ma zuciyarta
bayan ya katse kiran kuka mami tasa tare da jin wani kullin bakinciki ya tsaya mata a qirji yaki gaba yaki baya wayarta ta lalubo ta soma neman layukansa amman shiru bata shiga dan haka ta kira Amar nan ta samu labarin tafiya yayi zuwa hollond abun yayi mata ciwo fiyye da tunanin mai karatu ammar din ma yana tambayarta ko tana son wani abu amman tuni ta katse kiran .”
batayi sanya a gwiwa ba ta kira ya’yanta a waya ai kuwa washegari gabdayansu suka hallara a gidan cikin tsananin tashin hankali aiko mami tasa masu kuka tana kiran “adamcy zai kasheni shikenan ya zama sila shiga tsakanina da d’anuwana muna zamanmu gwanin sha’awa, kana ganinmu kasan akwai shakuwa da soyayya a tskaninmu, muna ta qoqarin had’a kanmu dana ahlimu, mun rungume juna babu kyarma muna tsananin son juna amman yau sanadiyar adamcy ran d’anuwana ya sosu yayi min abinda bai ta’ba min ba .Abdul ra’uf bai ta’ba min magana cikin fushi ko ‘bacin rai ba sai a jiya “ni zulai na shiga uku nah me yasa na had’a auren nan ?”wallahi dana san abinda zai biyo baya kenan da ban had’a ba dana bar adamcy ya cigaba da rayuwarsa haka babu aure dan duk abinda zai lalata zumuncina da yan’uwana bana qaunarsa”.”
“kiyi hakuri mami ki daina kuka haka Allah ya qaddara kowani bawa da kalar qaddararsa wannna rabon dake tsakaninsu fa idan baa yi auren ba ta ina zaa samu ?inji cewar aunty shahida ,”kuka fa ya zamammin dole abdul’rauf na min biyayya duk abinda nace shi yake yi bai ta’ba sa’bawa umarnina ba "wai mami zaginki yayi ne ko me ?zabiba ta tambayeta “ko d’aya zabiba abdul bazai ta’ba zagina ba amman yayi min magana cikin fushi abinda bai ta’ba min ba sai jiya” nifa na kasa gane abubuwan nan na yaya adam mutun kamar babu tausayi a cikin zuciyarsa gsky mami yakamata ki san yadda za'ayi da yaya ga ciki ga saki dame sister zataji wallahi ni tausayi take ba ya dawo daita kawai .”nana hauwa’u ta qarasa mgnr tana sheshekan kuka aunty shahida ta numfasa kana tace “karki d’aga hankalinki auta kinga kema bake kad’ai bace za'a haukatar dashi bari ya dawo daga hollond lafiya amman dan dolensa ya maidaita ta haihu a gidansa idan ba haka ba wallahi wannan karon zai had’u da tashin hankali da bai ta’ba gani ba “ku dai bi komai a hankali domin dai acikinku babu wanda bai san waye yaya adam ba kusan yafi buqatar rarrashi da lalama muddin da tashin hankali zakuje masa wallahi bazai maku abinda kuke so ba .”
“da mamaki aunty khadija ta kalleta “abinda muke so kuma ke banda ke ?”gsky banda ni abinda kuke so am sorry to say dani yanzu bazan sake goyawa zaman aurensu baya ba ,ya kamata zuwa yanzu abarsu haka kada a takura masa ku kyalesa ya huta idan yayi ra’ayin maidaita da kanshi zai yi idan kuma iyakar zamansu kenan Allah yasa ya zama alkhairi ,sun d’auki lokaci suna tautaunawa a tsakaninsu sai dai zabiba ta tsaya akan raayinta wanda bai yi masu ba har mami .”
Bayan kwana uku ahankali oga ATA yake saukowa daga cikin jirki tare da yaransa mutu biyu kai tsaye in da driver da masu tsaronsa ke jiranshi suka nufa, ya qara kyau aciki kwanaki uku kacal farinsa ya sake fitowa ga cigaba da ya samu da nasarori akan business ,yana sanye da royal blue three piece suit daya daga cikin yarasa na sak'ale da bak'ar jakarsa daka ganshi kaga wayayye wanda yasan duniya ko nace duniya ke