Showing 138001 words to 141000 words out of 169868 words

Chapter 47 - MAR'ADAM'S BOOK 2 COMPLETE DOCUMENT by Aisha Bagudu .txt

06 Nov 2024

10888

masa abinda mai kamfanin creation yayi mata ba ,ya zama abun kunya gareta ace ta fad'a masa wani kato ya ta'ba mata jiki ya zai dauketa ina yarda da yayi mata ?"kuka ta cigaba da yi shi kuma yana falfala gudu akan titi shi kansa kana kallonsa kasan a matukar tsorace yake sun yi tafiya mai dan nesa sannan suka nemi motocin uku dake biye dasu suka rasa sai daf daa zasu fita daga ogun state kawai sai ga motocin guda uku sun sha gabansu."cak yaya sadam yaja burki ya tsaya cikin tsananin fargaba wasu tika tikan murd'ad'd'un mutane suka shiga firfitowa daga cikin motar d'aya bayan d'aya har suka fito gaba d'ayansu sanye da kaki wanda ke nuna alamun sojojin nigeria ne wani irin matsanancin tsoro da firgici ne ya kama marayam tayi saurin riko hannun yaya sadam gam cikin nata jikinta na kyarma shima ya riketa gam bai yi tunanin ko yan fashi da makami bane sakamakon kakin dake sanye ajikinsu zuciyarsa tafi bashi wani abu dabam ,mutun uku daga cikin sojojin suka qaraso da sauri suka bugi kofar motar da karfi batare da 'bata lokaci ba kofar ta bude basu tsaya wata wata ba suka fito da yaya sadam tare da buga masa bakin bindiga nan take ya zube kasa .”




maryama ta saki qara mai sauti ta fito ta durkushe gabansa cike da matsanancin tsoro yaya sadam ya janyota zuwa jikinsa ai kuwa ta kamkamesa dan gabad'aya a tsorace take hawaye né ya soma bin kuncin maryama cikin sheshekar kuka maryama ta soma magana "bayin Allah laifin me mukayi maku ?dan Allah karku cutar da ni da mijina ,dan allah ku barmu mu wuce tunda nasan bamuyi maku laifin komai ba "ke ce bakiyi mana laifin komai ba amman shi wannan bakin munafikin yasan abinda yayi mana "inji cewar daya daga cikinsu da sauri maryama ta tsurawa yaya sadam idanunta tana kallonsa "wai kai dan rainin wayo ko ?mu zaka rainawa hankali ?".a d'an rud'e yaya sadam yace "Nifa duk ban fahimceku ba hasalima ban san laifin da nayi maku ba ,su waye ku ?meye hadina daku ?laifin me nayi maku ?ya jera masu tambayoyin yana sake riko maryama jikinsa "kai karka nemi ka rainawa kanka hankali dan ubanka kayi tunani laifin daka aikata acikin satin nan wanda kai kanka kasan dole zaa iya bibiyarka?".




yaya sadam yayi shiru yana nazarin maganr shi dai asaninsa bai aikatawa kowa laifin komai ba baya ga auren maryama da yayi "har kusan minti biyar yaya sadam bai ce uffan ba yasa suka cigaba da magana "me taurin kan tsiya kawai amman tunda baka tuna ba idan kaje lahira zaa maka bayani dalla dalla akan taurin kan da kayi ,kai jojo ku daukosa mu aikasa lahira yadda yayi taurin kai dan son more duniya bazai zauna a duniyar ba "nan da nan suka rufe masa ido da bak'in kyalle ,suka d'aure masa hannayensa duka abayansa kafafunsa ma a d'aure ,suka rufe masa baki suka ciccibosa suka watsa shi acikin mota "itama yarinyar kuyi mata kamar yadda kuka masa ku sata acikin mota ku had'a daita batare da 'bata lokaci ba aka rufe fuskarta aka tasa keyarta cikin mota tunda tashiga motar take rutsa kuka mai ta'ba zuciya tare da kiran sunan Allah yayinda yaya sadam yasa hannuwansa duka ya dafe goshinsa yana zurfafa tunaninsa alokacin da motocin suka karya kwana cikin wani kungurmin daji mai cike da duhu da ban tsoro suna sharara gudu."




tunanin duniya yaya sadam yayi amamn iya tunaninsa bai ga wanda zai iya masa haka ba idan safiya ce yasan baa akansa zata huce ba sai dai akan maryama tunda tasha fad'a masa muddin taganta sai ta aikata lahira ."nadiya kuwa yasan kwata kwata bazata masa haka ba shi kuwa wa yayiwa laifi ?"idan ma laifi ne to sai dai akan auren maryama da yayi ne to waye wanda zai masa hk ?bai samu amsar tambayarsa ba yaji motocin sun ja wani irin burki sun tsaya a daidai karshen dajin tare da bubbud'e kofofin motocinsu a zuciye, na karshen ne ya fito rike da kwalar rigar yaya sadam wanda babu halin yin kwakwaran motsi ballantana yasamu damar yin ihun ceton ransa da'ake barazanar raba shi dashi, ahankali suka shiga jansa a k'asa suna tafiya dashi cike da tsansar rashin imani , wanda kallo daya zaka masa kasan a rikice yake d'aya daga cikinsu ya rike hannun maryama ."




Basu tsaya akoina ba sai a bakin wani katon rami suna huci "ku binnesa da ransa jin haka yasa maryama ta rikice ta gigice tashiga wage wage tana kiran sunan yaya sadam "dan girman allah karku kashesa karku binnesa da ransa gara ku kasheni wallahi banason na rasashi yana da matukar mahimanci arayuwata na bada rayuwata fansa, gara ku dauki raina ku barshi dan Allah karku kashesa duk wani abu da zaku masa kuyi min ni daman nafi bukatar mutuwa da rayuwata dan bana jin dadin rayuwar nan na rasa komai karku bari na rasa mijina tausayinta ya kamasu "d'aya daga cikinsu ya jawosu gefe yace "me kuka ga zaa yi ?"ya tambayesu "kar mu batawa kanmu lokaci wajen tausayi mu cika aikin daaka ba mu "shikenan a wuce gurin .”




aiko suka dauki yaya sadam suka jefa cikin rami suna shirin jefa maryama mutun daya acikinsu wanda shine yafi jin tausayin maryama yace mu barta tunda daman shi kadai aka bamu aiki "okay! suka amsa. a matukar gigice take batasan ya’akayi ba ta zare kyalen da suka rufe mata ido dashi tana gama bude idanunta yaya sadam dinta ta gani acikin rami suna zuba masa kasa zuciyarta ce ta tsaya cak ta daina aiki a lokaci har suka rufesa da ransa ."
Bayan sun gama suka hau jijigata a gigice ta dawo haiyacinta idanunta na zubar da hawaye wani razananniyar qara ta saki da karfi tana kiran "ina mijina yake ?idan har kun kashesa ku had'a dani ku kashe dan allah karku barni a raye dan bazan iya rayuwa babu shi ba haka ma mahaifiyarsa ." numfashi suka sauke atare "aikin gama ya gama yarinya tuni mijinki mai taurin kai yana cikin nan suka nuna mata inda suka binnesa, an gama da labarinsa sai dai uwarsa ta haifi wani idan an sake haifosa a duniya bazai sake kinjin magana ba "ai tana gama jin maganarsu numfashinta ya soma barazanar d’aukewa "me yasa ?me yasa zaku masa irin wannan hukuncin inna lillahi wa inna ilaihi rajiun me yasa zaku kashesa tayi taku biyu zata isa inda suka binne mata miji kafafuwanta suka gagara daukarta ga wani irin nauyi da kanta yayi idanunta suka fara rufewa jiri take gani nan take ta zube kasa sumammiya ."




Mmn Sudais


💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗




*AYSHA A BAGUDO*


WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim


Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.




Page 26


Ran ATA a matukar 'bace yake zaune acikin jirginsa yana tunanin maryama ,wani irin ciwo yake ji a zuciyarsa dan bazai iya misalta yanayin bugun zuciyarsa ba ,ga wani sara da kanshi ke masa har baya iya bud'e idanunshi sosai yayinda kowani second 'bacin ransa na sake nunkuwa wanda baya raba d'ayan biyu damuwar maryama ce bai san dalilinsa na kai hannunsa jikinta ba ."mai yasa yaji sauyi ajikinsa adalilin sake d'aura kwayar idanunshi akanta ?"mai yasa yaji yana buqatar ganin fuskarta a zahiri ?
yana jin wani irin sauyi akanta lallai yana buqatar ganin halittarta a zahiri zuciyarsa ta amsa masa kuwan haka ." da wannan tunanin ya isa gida alokacin da magariba ta kawo kai .jirginsa mai saukar ungulu na gama tsayawa a haraban gidansu rai a 'bace yake tattaka matattakala yana qoqarin saukowa , kai tsaye ya shiga bangaren mami sosai yake jin damuwa acikin zuciyarsa qoqarin danne damuwarsa yayi dan kar hankalin mami ya tashi sai dai kallo d'aya tayi masa ta fahimci akwai damuwa atattare dashi ."






"muryarsa a kasalance ya gaishe da mami ."kamar ko yaushe ta amsa masa tana mai tsura masa kwayar idanunta kamar wacce taga wani sabon halitta ,cike da kulawa tace "sannu da zuwa adamcy ya hanya ka dawo lafiya ?da sauri ya amsa mata da "lafiya !"yana qoqarin hayewa samansa hannunsa d'aya soke acikin aljihun wandonsa .bayansa tabi da kallo "shigowarsa cikin wannan yanayin yasa duk mami ta d'an rikice kasa samun kwanciyar hankali tayi ,cike da tashin hankali ta mike tsaye tabi bayansa .
ahankali ta tura kofar parlour'nsa ta shiga duhu falon dan haka ta kunna wuta nan da nan haske ya haskaka koina a parlour'n sai dai bata gansa ba dan haka ta nufi hanyar bedroom dinsa ta shiga nan ta iskeshi tsaye ya jingina jikinsa da bango d'akin yayi sama da kanshi hawaye ne kwance acikin idanunshi yana jin yadda zuciyarsa ke tafarfasa ya rasa meke masa dadi arayuwarsa bai san ta ina zai fara ba ,komai ya rigada ya tsaya masa gabad'aya baya jin dadin rayuwarsa ,ya kasa fahimtar kansa ko kuma yace yau tazo masa da abubuwa da yawa wanda duk tarin damuwa ne akan wanda yake ciki ya dinga jin kamar ya kashe kansa ya huta da rayuwar da yake ."






lumshe tsumammun idanunshi yayi sai ga hawaye sharrr na bin kuncinsa "adamcy nah ! ".mami ta kira sunansa cikin tsananin tashin hankali har jikinta na rawa . amatukar firgice ya tsaida kwayar idanunshi dake cike da ruwan hawaye akanta qirjinsa na wani irin dokawa da sauri dan bai ji motsin shigowarta ba sai sautin muryarta wani irin zazzafan numfashi ya sauke yana sake maida kanshi sama tare da ciro hanky ya shiga d'auke hawayensa"lafiyarka kake zubar da hawaye adamcy ?ta tambayesa cikin tsananin tashin hankali dan duk abinda zai sashi zubar da hawaye baqaramin abu bane da muninsa ya wuce misali. shiru yayi ya kasa magana dan bai san me zai fad'a mata ba "kayi min magana mana adamcy dan kasa har zuciyata ta fara tsinkewa."
da yatsan hannunsa ya nuna mata daidai saitin zuciyarsa dake bugawa fiyye da kaida ."sake matsoshi tayi sosai tana cewa "meke damunka "?"zuciyata sweet.." yana kai wa nan yayi shiru ya kasa cigaba da maganar idanunshi na sake cikowa da ruwan hawaye"me ya samu zuciyarka ?" ta sake tambayarsa hankalinta na qara tashi "I don't know what's wrong with me sweetheart amman dai nasan zuciyata kullum ciwo take min"."inna lillahi wa inna ilaihi rajiun " allahumma rahmataka arjun fala takilni ila nafsiy d'arfata'ai wa aslihli shahni kullahu la ila a illa anta "abinda mami ta shiga furtawa kenan tana sake maimaitawa " i know something is wrong with my heart wallahi sweetheart akwai ciwo mai zafi acikin zuciyata wanda zai iya kasheni nan kusa .."






nan da nan fuskar mami ta qara sauyawa hankalinta a matukar tashe tace "ka dinga sausautawa kanka adamcy da yawon tunani ,ka dinga addua akan duk abinda ya dameka addua tana canzawa bawa qaddararsa kuma tana saka natsuwa acikin zuciyar bawa "numfashi ya sauke da karfi yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa ,magana yake son yi amman zafin da zuciyarsa keyi ya hana shi cewa uffan "kasamu natsuwa adamcy ka dinga furta wannan adduar zaka samu natsuwa da sausauci a wajen Allah zai yaye maka dukkanin damuwarka "allahumma rahmataka arjun fala takilni ila nafsiy d'arfata'ai wa aslihli shahni kullahu la ila a illa anta ahankali ya sauke idanuwanshi ya tsura ma mami kawai yana kallonta cikin yanayi na tsanani damuwa "ka sani idan wani abu ya sameka nice farkon wacce zata fara shiga damuwa ga kuma d'an cikin jikin maryam wanda bamu san abinda zata haifa ba karka bari muyi maraicinka. adamcy kasan yadda nake sonka idan na rasaka zan shiga damuwa a kullum adduata na mutu na barka a duniya ba ka mutu ka barni ba tunda ta fara magana bai ce mata uffan ba sai ma ciro wayarsa da yayi ya soma neman layin likitansa muryarsa ce ta katse mami daga maganar da take masa ahankali yake magana tamkar mara lafiya "doctor kazo ka dubani please ".daga haka bai sake cewa komai ba ya katse kiran d'akin yayi tsit tamkar babu mutane acikinsa ."






Ahankali ya soma d'aga kafafunsa zuwa Kan gado ya fad'a ya kwanta flat ransa duk babu dadi yayinda idanunshi na kallon saman d'akin babu abinda yake gani sai kwayar idanun maryama da yatsun hannun ta da sautin zazzakar muryarta mami tazo ta zauna kusa dashi tana daura hannunta saman kansa tana masa sannu "bayan mintuna shabiyar sai ga doctor ya shigo tare da sallama tashi yayi ya zauna ya jingina bayansa da abun gado yana sauke numfashi da kyar tare da yiwa doctor bayanin yadda yake ji batare da 'bata lokaci ba doctor ya fara masa gwaje gwaje bayan doctor ya gama yayi masa allura sannan yace "ranka ya dade jininka ne ya hau kad'an yana da kyau ka dinga saukakawa kanka wasu abubuwa dan zuciyarka na bukatar hud'u yanzu dai nayi maka allurar bacci in sha allahu kana tashi zakaji daidai Allah ya baka lafiya ya ajiye masa magunguna yace zai wuce ."mami tayi masa godiya adaidai lokacin da doctor ke had'a kayansa yayi mata sallama ya wuce ."




"Ka tashi kayi sallah magriba kafin bacci ya d'aukeka sannan me za'a kawo maka coffe ko tea "any one sweetheart." ya furta tare da mikewa da kyar ya shiga bathroom ita kuma mami ta fita kawo masa coffe dan tasan shi yafi bukata wanka ya fara sannan yayi alwala ya fito ya cire kayan jikinsa ya canza zuwa jallabiya brown colour mai ratsin baki ya isa inda abun sallarsa yake ya gabatar da sallah bayan ya idar ya koma Kan gado ya kwanta lamo tare da janyo bargo ya rufe jikinsa koda mami ta dawo d'akin ATA na bacci ta zauna gefensa tare da zuba masa idanunta tana jin wani irin qaunar d'anta na ratsata bata iya dogon fushi dashi hakazalika bata son ta rasa shi. hawaye ne ya fara bin kuncinta ji take a duniya data rasashi gara ta rasa komai dan idan ta rasashi ta ina zata cigaba da rayuwa?" ina bazata iya ba bazata iya jurar rasashi ba gara ita ta bar duniyar tun kafin taga mutuwarsa ahankali ta mike tana goge hawayen idanunta ta qarasa ta rage masa karfin ac sannan ta canza masa wutar d'akin zuwa mara haske ta duka daidai fuskarsa tayi masa addua sannan ta fita daga d'akin ."




Washgari tun da yayi sallah ya koma bacci har karfe goma bai tashi ba yana kwnace yana sharar bacci shigowar mami yafi sau uku dubashi yana bacci sai dai ta kalli fuskarsa ta fita sai wajen shadaya da wasu mintuna ya tashi hanyar bathroom ya nufa ya fad'a yayi wanka ya fito yana goge sansar jikinsa ya sanya kananan kaya masu matukar kyau he look very attractive kullum ka kallesa qara kyau yake ya d'auki kwalbar turare yana feshe jikinsa yana fesa turare kwakwaluwarsa na tunanin maryama da sauri ya ajiye kwalban turaren hannunsa ya qarasa inda ya ajiye kayansa na jiya daya cire ya dauki dogon wondonsa ya shiga laluba wondon cikin kankanin lokaci ya ciro agogon sarkarta .yayi shiru yana kallon agogon yana ganin tsinysiyar hannunta aciki "mai yasa zuciyata ta damu akanki ? zuciyarsa tace "kasani ko ubangiji ne ya turo maka ita cikin rayuwarka da wata manufa a boye kayi duk yadda zakayi tayi aiki akarkashinka sosai ya dinga jin damuwa akan abinda yayi mata abu ne da bai tabayi ba .wai ya kai hanunsa jikin wata mace da sunan ta burgeshi ya dauki kusan mintuna goma yana kallon agogon tsarkar sannan ya bud'e durowarsa ya jefa ciki ya fito yana taku . "






cike da isa yake taka step, tun daga kan step yake jiyo sautin muryar baba qarami yana tafiya da kyar har ya sauko kasa ya tarar da mami zaune a inda ta saba zaman a parlour'n gabanta kuma baba qarami ne zaune yana magana cikin tsananin fushi tunda yayi masa kallo d'aya ya dauke kanshi bai sake kallon inda suke ba ya wuce dining ya dibi abinci da kanshi ya a zauna akan kujerar dake kallon step bayansa kawai zasu iya hangowa haka zalika duk abinda suke fad'a yana jinsu bayan ya gama cin abinci ya d'aga kanshi yana kallon agogon dake manne a parlour'n dake walwalin haske karfe 12:00 na safe ne yanzu mikewa yayi ya qarasa gurin mami yace "sweetheart ni zan fita mami tace "kai da baka da lafiya ina kuma zaka ka dinga hutawa dan Allah ?" numfashi kawai ya sauke batare da yace komai ba "ka zauna akwai maganar da babanka yazo dashi shiru yayi yaki zama "banason musu kayi abinda nace "a natse ya samu waje ta zauna still bai kalli inda baba qarami yake ba bare ya gaishesa "magana ce yazo daita akan hindu me kasani akai ?zuciyar ata a dake ya fad'a mata komai game da abinda ta aikata ."






baba qarami ya kalli ata yana jin haushi irin haushin da mutun zai iya kashe mutun "na dauka ko wani ka ga yayiwa hindu haka sai inda karfinka ya qare kuma zaka taimaki rayuwarta amman wulakanci ka bar min 'ya a tsare har tsawon watani sannan aka

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login