Showing 126001 words to 129000 words out of 169868 words
Chapter 43 - MAR'ADAM'S BOOK 2 COMPLETE DOCUMENT by Aisha Bagudu .txt
min haka ?duk qoqarina baki gani ?ta furta acikin zuciyarta "yaya hisham dake rike da yatsun hannun nana hauwa'u ya sakar mata hannu yana gaishe da mami numfashi ta sauke tana amsawa "mami karki d'aga hankalinki dan kin rigada kinsan halinsa ,kubishi ahankali har zuwa sanda zai sauko zai amsa ai mutun bazai ki jininsa ba "hisham ina jin tsoron zuciyar adamcy idan yace bai son abu to kamai zai faru sai dai ya faru ni yanzu ba sakin yafi damuna ba kmar yadda yace bai son cikin jikin maryam" ko yaso ko kar yaso jininsa ne abinda Ke cikin kuma dole ya amsa sunansa addua kawai zaa cigaba da yi masa Allah ya sanyaya masa zuciyarsa yana gama fad'ar ya tashi yana ma nana hauwa'u magana kasa kasa ."
Bayan fitar yaya hisham "ya'yan mami suka sakata a tsakiya "yanzu mami ya zaayi ?ya kuwa zaayi banda hakuri kowa ya kawo ido ya saka masa Allah ya kawo masa sauki ,zan kira Abdul rauf nayi masa bayani "allah yasa ya fahimceki " inji cewar aunty shahida to "ameen zai fahimceni in sha allahu "basu wani zauna ba kowace ta d'auki gyalenta da jakarta ta yafa atare sukai wa mami sallama suka fito kowacce ta shige motarta nana hauwa'u ce kawia ta saura tsaye tana kiran layin mijinta tana tsaye yayi parking tare da fitowa ya karbo jakar hannunta ya bud'e mata gaban mota ta shiga ta zauna tare da cewa "na gode zumana !"ya maida murfin mota ya rufe ya zagaya ya shiga mazaunin direba suka kama hanya gida ."yana tuki ya dan kalleta "baby me yasa kuka aikatawa ATA haka ?tayi shiru "kisani kunyi kuskuren aikata amman dai Allah ya kawo saukin wannna tashin hankali numfashi ta sauke tare cewa "amen ! ta kamo hannunta d'aya cikin nata tana massaging tun nan ya fara jin wani iri ajikinsa wanda ita ba wai tayi da wata manufa bane .
suna isa gidan d'akita suka shiga ya cire rigarsa ya ajiye sannan ya janyota ta fad'o jikinsa tare da ciremata mayafi sannan yace "habibty na yau dai baza'a hanani na shoshale ba koh" nok'e kanta tai cikin k'irjinsa sannan ta fara magana cikin shagwab'arta wacca take k'ara birgeshi take kuma k'ara sakashi ya rikice tace "kai yayana gaskiya ni yanzu agajiye nike kuma kasan fa kayiwa doctor alkawarin zaka dinga d'aga min kafa na kwana biyu biyu har cikin nan yayi kwari sosai "ai da kin daku yau a wajen wannan yayan naki da kin gane agajiye kike "tasa dariya tana sake makalewa ajikinsa tare da d'an cizon qirjinsa da" ai tunda naganka nasan bazan daku ba " tak'arasa maganar tana matsa kan nipples dinshi, "aaashhh....!!!" yai y'ar k'ara sannan
ya kalleta da sexy eye's nashi da ya dan fara canzawa
yace baby ni dana taimaki zaki ciza zaki " dariya tai sannan tace "ai kai naka yafi zafi sosai wannan ai ba zafi" wani kallo ya mata "ok ba zafi koh toh bara na maki kiji idan ba zafi" nan ya juyata ya maidata k'asa sannan ya fara kiciniyar rabata da rigar dake jikinta ganin da gaske yake kuma tasan halinsa ta fara kuka tana neman tuba bai saurara mata ba sai daya sucking brest dinta son ranshi sannan ya barta.”
Batun sakin maryam ya bazu acikin abdullahi estate masu murna nayi ,masu bakinciki nayi aunty abida kam tafi kowa murna faruwar wannna sakin dan lokacin da taji har wani tsalle da rawa tayi a bangarenta batare da kid’a ba tana cewa “shikenan nan sultana zaki dawo a saa, kece zaki maye gurbin kowace mace a wajen adamcy ,inganga inganga !!rawa tayi sosai tamkr wata zararriya a qarshe ta suri wayarta ta shiga neman layin mahaifiyarta sun d’auki mintuna talatin suna waya sannna sukai sallama ta kira sultana tana d’auka tace “wai zaman me kike yi ne har yanzu ?” Kiyi qoqari ki dawo dama biyu ta samemu ya saki matarsa ga kuma neman masu kwararrun zane da yake nasan yana ganin zanen Kanwata zai rud’e daga nan kuma shinkenan “okay to shikenan dan girman allah ki ajiye komai ki dawo kar murasa damarmu okay bye ta katse kiran tana cigaba da rawa yesmin ta fito daga dakinta tana kallonta murmushi ta sakar mata tana cewa “yesmin kin kusan zama cikakkiyar ‘ya a wajen babanki AD “‘ya kuma mum ?yes auntynki sultana zai aura ta qarasa maganar tana rungumeta“.tsabar murna washegari aunty abinda ta shirya walima gabdaya estate din babu wanda bata aikawa da snks da drink ba duk wanda ya kalleta zai fahimci tana cikin murna .”
nan da nan zance ya kai kunnen mami babu abinda tace face “allah ya shiryeta domin duk mace mai hankali bazatayi murna dan an saki yaruwarta mace ba ita yanzu bazata sake matsawa adamcy ba amman kullum cikin yi masa addua take idan da rabo allah ya daidaita su. .allah sarki maryam ta dad'e kwance akan gado tana sak'e-sak'e a ranta, dan ta ji zafin abinda aunty abida tayi ,tsaki taja tare da mik'ewa tsaye tana d'an zagaya d'akin "dole ne na nuna ma
abida kuskurenta,zan nuna mata baa kishi da irin mu yaran zamani, tunda na lura shiru baya mata sosai abinda aunty abida tayi ya 6ata ma maryam rai, zan nuna mata iskancinta wasa ne wannan karon a bayyane tayi maganar tana wani shu'umin murmishi.”
*********
Zaune yaya sadam yake a haraban gidansu akan daya daga cikin kujerun dashi ne ya ajiyesu saboda abokansa domin zama yana sanye cikin farin yadi idanunshi manne da farin glass idanunshi kar akan wayarsa yana karanta sakon Nadia a natse ta fito zuwa garesa ahankali ya soma ganin tahowarwata ta kasan idanu shi cikin tafiya ta Kamala sanye cikin doguwar riga yellow ya dago kanshi ya tsura mata ido tana kyau sosai dan maza zai had’ata da nadia ba har ta gama qarasowa garesa fuskarta dauke da murmushin farincikin ganinsa tace "sannu yaya dan allah kayi hakuri na barka zaune ka kadai“
murmushi ya sakar mata tare da lumshe mata idanunshi "karki damu ko zan kwana ina jiranki bazan gaji ba sauraniyar kyawawan mata duniya kuma zabin umma nan ki zauna ya nuna mata kusa dashi ta zauna a natse tana kallonsa cike da jin kunyarsa "ina yini ya aiki da fatan komai Lfy ?tayi masa tmbyr a jere tana sunkuyar da kanta kasa tare da kamo yatsun hannunta tana wasa dashi "maryama duk Alhamdulillah mun godewa allah ya mumcy take ?ta gyda masa kai kawai alamun lafiya a hankali ya soma janta da hira sai dai bata wani mgn daga uhm sai uhm take cewa "maryama ! Ya kira sunanta ta dago a natse ta kallesa na second daya ta sake maida kanta ta sunkuyar "ga dukkanin alamun kamar agajeye kike ? Tai murmushi batare data dago ba "nan da sati uku zaki kasance a gidana a yanzu nake jin na matsu naga kin kasance a gidana” ajiyar zuciya mai karfi ta sauke tana dago kanta ta tsura masa idanunta "ta so ya kurewar tamvayarta aikin da take fita nema kullum amman sai ya wani kawo mata maganar aure .”
ta fahimcesa sosai shi mutun ne da bai da caring me taci ko me tayi ko a wani hali take duk ba damuwarsa bace idan ma yazo gurinta ba wani hirar soyayya yake mata ba wanda zai dauki hankalinta zai kama gabansa shiyasa duk tsawon lokacin da mahaifiyarsa ta hadasu bata ta'ba jin komai akansa ba sai dai tana danne komai saboda mahaifiyarta da mahaifiyarsa .”yana ganin girman mahaifiyarta sosai yana kula dasu sosai tun kafin a had’asu aure "kinyi shiru kina kallona kice wani abu mana ?shiru ne dai Ya sake biyosa baya har sanda wayarsa ta dauki qara sauti Ya dauki wayarsa dake ajiye a gefensa ya duba sunan nadia ya gani yana yawo a screen din wayar cike da firgic ya dubi inda maryama take sannan ya sake maida idanunshi akan wayar da kyar ya sauke naunayen ajiyar zuciya yayi disconnecting din kiran ya cigaba da magana " a she dai ni ne wanda zanyi wuf da wannna kyakkyawar yarinyar magana yake amman zuciyar maryama ta kasa samun natsuwar allah sarki yusif ashe Ke din ba rabonsa bace ?naunayen ajiyar zuciya ta sauke “kina da kyau sosai na godewa ummah datayi tunanin hadani dake na gaji da ganinmu haka ina son na killaceki a gidana "kana son ka killaceni agidan cike da rashin yanci ba ?tayi masa tmbyr a zuciyarta .”
“maganar da nake miki yanzu haka komai da zan saka agidanmu ya kammala zamu yi rayuwa mai dadi ko kina son na ajiyeki a wajen umma ne saboda yanayin aikina.”? yana gama fadar haka Ya mike sakamakon wayarsa data sake daukar qara "excuse me! ya kamata ace kana duba yanayina yaya sadam har yanzu ban ji amincewarka akan aikina ba zaka yarda na cigaba da yiwa kafanunka zane ko kuwa ?.”“bana son sai bayan munyi aure kace bakasan da zance ba wannan aikin rayuwata ce kuma ina son ya kai ni matakin da ya zarta yadda nake a yanzu babban burina bai wuce na samu aiki kafanin AGC ba .taí shiru tana jiran taji mai zai ce amman yayi mata shiru saboda raayinsa amman dole yanzu kam ya amince dan yasan idan yaki amincewa zai ta’ba zuciyar ummansa ya tsura mata ido yana nazarinta a yanayinta zata iya komai akan aikinta ." ta mike a natse tana dubansa "kayi shiru yaya sadam kace wani abu mu kawo qarshen maganarmu banason muyi aure daga baya muzo muna samun matsala akan aikina "ka amince zaka aureni da aikina sannan zaka min hanya naga mai kafanin AGC ? ta fad’a hk sbd tasan su yusif nada hanya da karfin iko shiru yayi yaki cewa komai yana sauke numfashi da kyar, domin kuwa abu biyu né suka hade masa guri daya ga tambayar maryama ga kiran da nadia ta damesa dashi wanda baya jin zai iya duka abu biyu din ."
“Ina duba yanayi na zaman takewar aurene yaya sadam domin kuwa kai kana cikin mutanen da suka san koni wacce irin rayuwar gidanmu mahaifiyata da mahaifina taí mgnr tmkr zatai zubar da hawaye dan gbdy idanunta har sun canza kala daga fari zuwa yellow "ya kamata mu tsara komai yaya sadam domin kuwa banason damuwa arayuwar aurena ta qarasa mgnr tare da kai yatsun hannunta biyu ta dauke hawayen dake kokarin saukowa kuncinta ".
numfashi ya sauke da karfi sannan yace "shikenan zakiyi aikinki “bari naje ana nema zamuyi waya ya fada yana kokarin barinta tsaye tare da manna waya a kunnensa ya nufi kofar fita taí shiru tsaye tana duban bayansa "yanzu irin wannan mijin zata aura tai rayuwar aure dashi ?anya kuwa idan ta auresa zata ji dadin rayuwar aure kuwa yadda yake da rashin nuna caring ?” yanzu a halin da take ciki kowa Ya ganta yasan tana cikin damuwa dan gbdy komai nata Ya canza amman kalli yadda ya bar gabanta batare da Ya tsaya ya fahimci matsalarta ba bare ya kawo mata mafuta oh allah karkasa nayi Kuskuren aure irin wanda Mahaifiyata tayi ya allah ka taimakeni kasa ya canza duk da banason shi saboda rashin caring dinsa dan kusan matan duniya shine matsalarsu a gidajen mazajensu a yanzu, cike da sanyin jiki har ya bacewa ganinta tana tsaye a wurin rungume da hannunwanta a kirji jiki a sanyaye ta nufi kofar part dinsu ."
*******
motarsa na shigowa haraban ma'aikatan yaji gabansa yayi wani mummunar faduwa da karfin gaske shiru yaki fitowa daga cikin motar yana tunanin abinda yasa yaji hk byn tun a gida bai tsinci kansa cikin wannan yanayi ba sai daya shigo ma'aikatan iskar ya furzar ya daga kafadunsa alamun babu komai a hankali ya zuro kafafunsa dan tuni an bude masa kofar mota ya fito yana gyara zaman suit din jikinsa sannan ya soma taku a hankali qirjinsa na cigaba da luguden bugu yayi qoqarin kawar da yanayin da gangar jikinsa ya shiga ta hanyar tura hannusa daya cikin aljihun wondonsa." duk inda ya wulga maaikata ne Ke kokarin kawo gaisuwa sai dai kai kawai yake gyada wasu ,wasu kuma yayi masu banza har ya hau lift da zai kaisa sama na uku inda anan office dinsa yake yana sauka yaji wani sabon faduwar gaba wanda ya rasa dalili nan ya dan rage tafiyar da yake ya dawo yana daga kafafunsa da kyar saboda sanyin daya ziyarcesu alokacin daya tun daga nesa ya hango bayan wata yarinya suna magana da wasu daga cikin maaikata kamar ya tsaya sai kuma ya karya kwanan da zata kaisa office dinsa cak yaja ya tsaya sakamakon jiyo sautin muryar yarinyar shiru yayi yana cigaba da saurara maganarta tamkar dai mafarkin da daya saba yi “anya kuwa muryar tace ko dai mafarkin daya saba yi daita ne suna hira ?.
hannunsa ya kai yana shafa daidai satin zuciyarsa dake bugawa tmkr zata fasa qirjinsa tayo waje ya dinga jin tamkar yayi reves ya dawo ya shiga inda yake jiyo murayarta ya tabbatar ita din ce ko kuwa muryar ce kawai tazo daya amman sai zuciyarsa ta kwabesa wankakkiyar zuciyarsa ta sake yin magana dashi kaje ka duba ko itace wata zuciyar tace kai ba itace ba ,ba yarinyar mafarkinka bace, dan haka a natse ya daga kafarsa daya bai kai ga ajiyewa ba ya sake jiyo sautin muryarta"."ku ne fa kuka bukaci kwararrun masu irin aikinmu yau tsawon wata guda kenan ina zariya a ma'aikatan ban samu nasarar ma hawowa saman ba sai yau ,yau din tun karfe bakwai na safe nake cikin compaing dinku kafin ma ku yarda na hawo saman nan sai da kuka bata min lokaci na samu da kyar na hawo yanzu kuma kuna kawo min qabli da baadi kunsa irin wahalar dana sha kafin na kammala aikin nan kuwa ?"kunsa lokacin da yake daukar mutun kafin mutun ya kammala ,shikenan shikenan!! tunda bakwa bukata ku bari na wuce na kama gabana daman an fada min wahalar banza kawai zanyi byn hka bakwa girmama masu tallata kasuwancinsu tana gama fadar hk ta juya haka zalika fuskarta a rufe take "no madam bamuce bama bukata ba mutane dayawa sun kawo nasu zanen maganar da nake miki har yanzu mai gida bai duba ba bare ya tantance bazamu iya cewa komai ba a yanzu dole sai an agwadawa boss ".
Ta juyo ta fuskacensu sosai.” har zuwa wani lokaci kenan zaa gwada masa sannan zuwa yaushe zanji feed back ?zai iya daukar wata uku zuwa ..tsaki taja ta sake juyawa tana tafiya tana cewa "gashi nan na bar maku bana da bukata domin ko na koma dashi gida babu amfani da zai min ."snyayen Kamshin turarenta ya bugi hancinsa yayi saurin lumshe idanushi zuciyarsa na cigaba da mugun bugawa ta kusa dashi tazo ta wuce har tayi taku uku ta fahimci ba ta nan hayar fita take ba dan haka ta sake juyo wa ta nufi kofar da lift yake ahankali Ya juyo yabi bayanta da kallo yana kallon every step of her doguwa ce sosai kuma bakar mace ce yayinda tsayinta ya fito da ainin shape dinta na cocacola iya haka kawai ya iya fahimta domin hannunta da kafafunta abayyane suke haka hijab din dake sanye ajikinta qaramin ne hkn ne ya bashi damar dan fahimtar wani abu a tattare daita "
ATA yana tsaye tamkar gunki yana kallon tafiyar yarinyar da bai san ko wacece ba amman jin sautin muryarta da yanayin tafiyarta yasaka zuciyarsa jin wani irin tsoro mai tsanani da shiga tashin hankali shi gani yake ma babu tantama itace ba anya kuwa ba gizo tayi masa ba kamar yadda yake ganinta a mafarkinsa har yanzu kwayar idanunshi yana Kan hanyar databi ya kasa kwakwaran motsi wani irin ajiyar zuciya ya sauke tamkar ya dakatar daita ya daga black nikaf din dake manne da idanunta yaga fuskarta amman gangar jikinsa da komai nasa yayi rauni zuciyarsa kuwa sai bugawa take babu Kaukautawa ba shiri ya dafe daidai saitin zuciyarsa ya a manne jikinsa da bangon wurin dan yanayin da yaji akanta ya wuce misali hakan yasa kafafunsa suka kasa dauakarsa ."ya sake kurawa hanyar data bi ido har lokacin tafiya take mai hade da rasauya tamkar fure hankalinta kwance take taka kasa tana gyara zaman qaramin hijab dinta wanda akewa lakabi da haif sunnah, gyara tsayuwarsa yayi sosai tare da zura hannunwansa duka cikin aljihun wondonsa zuciyarsa na cigaba da bugawa da sauri sauri yayinda gabadaya ma'aikatan dake aiki a office din da maryama ta shiga suka fito domin binta da makeken hotonsa wanda ta zana ."
turus sukai gabadaya suna kallonsa kowannensu ya gyara tsayuwarsa yana kare masa kallon abinda basu ta'ba ganin ya faru ba, basu ta'ba ganin abinda ya dauki hankalin mai gidan nasu ba sai yau ya kusan miniti goma yana tsaye yana fama da zuciyarsa dake karkarwa" Wayyo allah ina ma zai iya da yasa an dakatar daita ko sau daya yaga fuskar ko mafarkinsa ce har ta shige lift bai motsa ba ,sautin gaisuwarsu ce ta dawo dashi hankalinsa a natse .kallo daya yayi masu ya juya batare daya amsa ba yana tafiya yana sauke numfashi a natse ya dinga daga kafafunsa tamkar mara laka a jiki jikinsa baqaramin sanyi yayi ba har ya shiga office dinsa ya wuce sectary dinsa zaune