Showing 135001 words to 138000 words out of 169868 words
Chapter 46 - MAR'ADAM'S BOOK 2 COMPLETE DOCUMENT by Aisha Bagudu .txt
toyawa ba amman haka nan yake jin matsanancin bugun zuciya da kuma 'bacin rai mara misaltuwa "any way kiyi sauri ki shiga kiyi abinda ya kawoki dan mai gida baya wasa da lokacinsa ,akan lokacinsa zai iya aikata komai kafin ta bashi amsa yaya sadam yayi murmushi ya matso kusa daita sosai tare da zuba hannuwansa duka cikin aljihu wondonsa fuskarsa a sake "karka damu yanzu zata shiga kuma zata maku abinda kuke so "ya fad'a masa haka sannan ya maida hankalinsa kan maryama kamar zai mata numfashi"k'anwata kuma amaryata karki wani damu da jiran da zan miki ni kad'ai abinda nake so dake ki natsu sosai kiyi abinda ya kawoki ina sonki ina kuma alfahari dake na kuma yarda dake a duk inda zaki kasance nasan zaki kame min kanki da kuma mutuncina "nan take idanuwanta suka cicciko da ruwan hawaye "yaya sadam na gode sosai ,na gode da yarda daka min ya allah ka yarda dani kamar yadda mijina ya yarda dani "ameen ya hayyu ya qayyum "ya fad'a tare da ciro handkey fari daga gaban aljihun rigarsa ya goge mata hawaye then ya kai bakinsa yayi kissing foring head dinta yana mai karfafa mata gwiwa murmushin gamsarwa ta sakar masa sannan tayi gaba tana d'aga masa hannu ."
bayanta yabi da kallo cike da tausayawa take taka kasa kamar bata son takawa yana tsaye har sai daya ga ta tura kofar office din ahankali ta shiga kusan second biyar ya d'auka tsaye yana kallonta ya kasa d'auke idanunshi akanta ,ATA wanda yake rike da waya a daidai bakinsa da hananu d'aya yayinda d'ayan hannunsa ke rike da wata farar takarda yana magana yana kai kawo acikin office din hakazalika segun na tsaye a gefe guda cike da girmamawa bai kalli inda take ba .”
ahankali yaya sadam ya juya ya fara taku zuwa kasa jikinsa a matukar sanyaye ya bud'e mazauninsa na direba ya shiga ya zauna yana sauke wani irin naunayen ajiyar zuciya sannan ya d'auki wayarsa ya rike yana dubawa missed call's din nadiya ya gani rututu ya sauke numfashi sannan ya kirata tana d'auka ta fashe masa da kuka "menene kuma abun kuka ?"na fad’a miki zan cika miki alkwarin da nayi miki bazan ta’ba cin amanarki ba nan da wasu watanni masu zuwa zamu kasance tare amatsayin ma’aurata ,oh my god dan an d'aura aurena shi yake nufi me ?kinga nadiya banason abinda kike min wallahi kukanki yana mugun 'bata min rai ."
"a natse ATA ya juyo mata fuskarsa sosai tare da tsayawa ya tokare hannunsa dake rike da farar takardar a makeken table din gabansa yana cigaba da wayarsa ."idanun maryama suka sauka kan kyakkyawar fuskar ATA wanda zuwa lokacin ya runtse idanunsa gam zuciyarshi da bakinsa ne kawai ke aiki ,ta tsura masa idanuwanta sosai tana cigaba da kallonsa " tabbas ba gezo idanuwanta suke mata ba shine shararren d'an kasuwan nan data d'auki tsawon lokaci wajen zanashi wanda a qarshe ta kai zanensa ma'aikatansa babu wata gamsashiyar magana mai dadi daga ma'aikatansa ."tayi shiru tana dubansa a tsanake tana shakar kamshn turarensa mai sanyi da ratsa zuciya "tun daga ranar data kai masu zanensa suke nemanta a waya "to mai yasa suke bibiyarta ?"mai yasa suka jawota zuwa nan ?"
ta yiwa kwakwaluwarta tambyr da bata da mai bata amsa wani irin mummunar fad'uwar gaba take ji babu abinda kwakwaluwarta bata hasko mata akansu ba amman tai qoqarin sharewa ta cigaba da tsayuwar jiransa ."bakinta na furta hasbiyallahu la ila a illahuwa alaihi tawakkaltu wa huwa rabbul arshil azim sakamakon wani sabon tsoro da ya shigeta ."
maryama na tsaye har kusan mintuna shabiyar ATA bai gama wayar da yake ba haka zalika bai bud'e kwayar idanunshi ya bata umarnin zama ba haka ma segun na tsaye bai zauna ba adaidai lokacin da qarfe d'aya na rana ta buga wanda a daidai lokacin wasu masallatan sun tada sallarsu dan haka ranta ya soma 'baci ta soma tunanin an janyota ne kawai dan a sake wulakantata a karo na biyu ji tayi kamar ta juya ta wuce shi da segun ta kama gabanta ,ta kalli inda segun yake tsaye shima ya kalleta haka nan ya tsinci kansa da shafa mata qirjinsa alamun tayi hakuri "segun !yes sir ya fad’a cike da girmamawa ya mika masa farar takardar dake rike a hannunsa batare daya bud'e idanunshi ba "ina bukatar copy's dinsu "okay sir ya amsa ya fita da sauri ."ko bayan fitar segun ata bai bud'e idanunshi ba bare yayi mata magana sai kuma taga bai kamata ace tana jiran sai shi ne zai fara mata magana ba dole dai sai itace zata fara masa magana kafin ya saurareta ,dan haka ta qara taku d'aya ta tsaya daidai saitin kunnensa cikin muryar dake nuna alamun gajiya "ta gaishesa bai amsa ba sai ma ya matsa baya ransa a 'bace yayinda zuciyarsa na tafasa dan ya tsani yazo jira duk abinda zaayi masa dole shi zaa jira karo na farko kenan daya zauna jira jiran ma akan itace zata qaru dashi .”
wulakanci da yayi mata yayi mata ciwo, dan ta tsani disgi da wulakanci kamar taja masa tsaki ta fice daga office din sai kuma tayi wani tunani su manyan nan haka halinsu yake kafin kayi nasara akansu dole sai ka kwantar da kai dan haka ta sanyawa zuciyarta hakuri tayi kasa da muryarta da kanta tana wasa da yatsun hannunta "ranka shi dade lokaci na tafiya yana da kyau abani aikin daya kawoni nayi ga kuma lokacin sallah yayi ina buqatar nayi sallah "sake jin sautin zazzakar muryarta ya sanyashi bude idanunshi ahankali tamkar mai tsoron ganin wani abun agabansa ,ya zuba mata tsumammun idanunshi masu mugun rikitarwa yana kallon cikin qwayar idanunta dake d'auke da zara zaran gashi ido itama shi take kallo tana jira daga garesa ".
shiru yayi yana cigaba da kallon cikin kwayar idanunta gabansa na wani irin luguden bugu da karfin gaske,kallon da yake wa kwayar idanunta kallon né na sani "jiki a sanyaye ya nuna mata wata kofa dake manne da office din "ki shiga kiyi alwala "yana gama fad'ar haka ya juya mata baya .”
shiru tayi kafin ahankali cikin sanyin jiki ta juya ta shige toilet ta d'auro alwala ta fito ta tada sallah a natse yana zaune yana kallonta yana waya ,ganin har ta idar da sallah bai tashi ba bare shima yayi tunanin ya tashi yayi sallar yasa tayi zaton ko ya manta daita acikin office din ne hakan yasa ahankali ta matso kusa dashi ta motsa labbanta"sir abani aikin da zanyi bani da ishashen lokaci da gefen idanunsa ya kalleta a d'age sannan muryarsa ta biyo baya a dake "kece kika zana ni? muryarta a sanyaye tace "eh nice sir !kinsan ko ni waye ?"shiru tayi har kusan mintuna goma tana nazarin maganarsa sannan cike da girmamawa tace "eh sir !
"Waye ni ?ya sake tmbyrta a dake tamkar bashi yayi maganar ba "kai ne shararren dan kasuwan nan da kasar nan dama duniya gabad'aya take ji dashi "tana gama fad'ar ya juyo a matuqar fusace ya fuskaanceta yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa "shine dan iskanci kamfanina ya buqaci yin aiki dake amman kikayi rejecting?ya qarasa maganar a matukar tsawace yana zare mata idanunshi .”
nan da nan hankalinta yayi matseefar tashi tayi saurin matsawa baya jikinta na kyarma "aikin banza kawai yanzu haka ke din ba diyar kowa bace amman kin d'auki girman kan tsiya kin d'aura wa kanki nonsense" yana gama fad'ar haka ya mike ya barta tsaye sake da baki "nice nonsense? ta tambayi kanta cike da mamaki jin abinda ya fad'a mata “nonsense!ta sake maimaitawa a fili tana mai jin d’acin kalmar domin tunda take ba’a ta’ba dangantata da kalmar ba .tana kallonsa ya nufi wani d'aki tana mai jin wani irin tuttukin bakinciki tare da damuwa mai tarin yawa har ya tura kofar zai shiga sai kuma yaja ya tsaya yana jan tsaki "give me ten minutes "
yana gama fad'ar haka ya qarasa shigewa .”
runtse idanunta tayi "wannan kuma wani irin sabon salon wulakanci da 'bata lokaci né ? ya kuwa san me ake kira da zane ?"abu ne da yake bukatar isashen lokaci "ita bama kanta take ji ba kamar yaya sadam mutumin daya sadaukar da farincikinsa ya biyota cike da zafin zuciya ta juya zata fita daga office din sai ga mr segun , ya tsaidaita yana cewa "ina zuwa kuma ?zan wuce ne dan bana tunanin aikin nan zai yuwu "calm down madam ki samu natsuwa kiyi abinda ya kawoki baqaramin sa'a kika taka ba da mai gida ya bukaci yin aiki dake "yana 'bata min lokaci gashi tare da mijina muke "nasani yanzu me yace ko tunda na fita bai yi magana dake ba ?"Yayi a qarshe wai na bashi ten minutes ."tayi mgnr kamar zatayi kuka "ok kiyi hakuri ki bashi lokacin dayace kin 'bata sama da awa acikin office din nan sai mintuna goma né kawai zai gagara watakilla ma bazaki yi aikin a yau ba ,zai baki ne kije gida kiyi idan kin gama sai ki kawo cike da jan hankali ya dinga karfafa mata zuciyarta dan haka ta cigaba da tsayuwar jiran ATA ."
kusan mintuna goma sha ya d'auka sai gashi ya fito tare da furta "kika ce kice kika zana ni? Kamar tace masa a'a dan taga abun nasa akwai rainin hankali ciki .amman sai ta tsinci kanta da jin tsoro dan haka ta maida kwayar idanunta ta lumshe masa tana wasa da agogon tsarka hannunta wanda ya qara wa zanen lallenta kyau ,lallen yabi da wani shu'umin kallo tun da yake bai ta'ba ganin zanen lallen da yayi masa kyau har ya d'auki hankalinsa ba sai nata yaji kamar ya kamo yatsun hannunta ,ya d'ago idanunshi a natse ya kalli fuskarta nan da nan idanunsu ya tsarke cikin juna wannan karon sauri cire kwayar idanunta cikin nashi tayi tana mai kawar da fuskarta gefe tare da danne bugun zuciyarta "shi kuwa wani yanayi ya tsinci kanshi ciki mai sarkakkiya da wuyar misaltuwa sakamakon idanunsu da suka sake tsarkewa cikin juna abinda ya lura atattare daita itama tana da jin kai da miskilanci"a natse ya sake bin zanen lallenta da kallo wani irin kallo ta watsa masa gabanta na fad'uwa wanda ta rasa dalilin jin haka ."
Ahankali ya samu waje akan kujerun kushin dake office din ya zauna batare daya bata umarnin zama ba "bata zauna ba sai ma idanunta data tsura masa tana kallonsa tana sauke numfashi dan itama taci alwashin bazata yi mgn ba har sai yagaji dan kansa yayi . abinda batasani ba shi ko ajikin ATA da zasu kwana a haka ma bazai damu ba abinda yasani ne ba zai barta taje koina ba har sai tayi masa abinda yake buqata daga gareta ."ya lumshe tsumammun idanunshi yana jijiga kafarsa d'aya yana jira daga gareta ."a qalla sun kusan minti talatin yana zaune ita da segun suna tsaye ta kalli agogon dake d'aure a hannunta a karo na kusan biyar a kasan ranta taja qaramin tsaki bata san me ya janyota zuwa wannan aiki ba nan take kwakwaluwarta ta shiga aikin neman mata mafuta ."kafin ahankali ta samo zance zuci"maryama dole ki ajiye komai ki qarasa gabansa Kiyi masa magana idan aikin nan zai yuwu ayi idan bazai yuwu ba ya sallameki ki kama gabanki tun kafin hakurin mijinki ya qare"da sanyi jiki take qarasowa zuwa inda yake ahankali ahankali har ta iso ta zauna a kujerar dake facing dinsa "wani irin zane zanyi "? tayi tmbyr cike da sanyi murya "ahankali ya motsa lip's dinsa "ina kayan aikinki ?da hanzari ta bud'e jakar kayan aikinta ta fito da kayan aikinta tare da janyo kujerar gabanta zata ajiye ta jiyo sautin muryarsa "ba'a nan zakiyi ba” ya fad'a tare da mikewa tsaye "biyoni ! "
fitowa sukai daga office din yana gaba tana biye dashi haka ma segun yayinda gbdy hankalinta ya rabu gida biyu wani yana gurin mijinta wani yana gurin ATA ."wani office ya shiga daita kai tsaye gaban wani farin baod yaja ya tsaya tare da jingina jikinsa da bango segun yayi saurin janyo kujeru guda biyu daya a gaban baod din dazaayi zane d'aya kuma a inda ATA zai zauna "sir ka zauna ! ya zauna tare da daura kafarsa d'aya akan d'aya jiki a sanyaye maryama ta zauna tana jiransa sai daya gama shan kamshinsa sannna ya sallami segu ya fara mata bayani tana jin ya fara magana ta d'aura hannunta akan boad ta fara fidda kyakkyawar shep din jikin zanen da yake buqata , yana mata bayani tana zanawa lokacin data zana karan hancinta taji wani mummunar tsoro ya shigeta cak ta tsaya ta kasa cigaba da zanen da take ta tsurawa baod din gabanta ido kwaayr idanunta ta zana da hancinta har ma da yanayin jikinta babu abinda yazo zuciyarta kamar zanenta data gani a office din m . malik “ nan da nan gumi ya shiga tsatsafo mata a goshi da karan hancinta.shi kuwa gyara zamansa yayi sosai yana kallon zanen lallen hannunta da yadda take tafiyar da aikinta bai san ya'akayi ba yaji saukar hannunsa akan hannunta yana shafawa ."
Cikin gigita gangan jikinta ya kama rawa wanda yasa ATA ya dawo haiyacinsa sai dai ya kasa d'auke hannunsa ajikinta da kwayar idanunshi wani irin tsoro da matsanancin firgici ATA yaga ya bayyana afuskar maryama ,yayinda zuciyarta ta shiga bugawa da karfi numfashinta ya soma barazanar d'aukewa, cikin sanyin jiki ta sabule hannunta cikin bacin rai tace "meye haka ?"dan allah aiki nazo yi banason irin
wannan wasan iskanci mai barazana ga rayuwata wannan ya zamo karo na farko da qarshe karka sake kuskuren sake kai hannunka jikinta "ta fad’a tana jan tsaki" ajiyar zuciya ya sauke tare da kafa mata tsumammun idanunsa cikin sayin murya yace "look at me “ta kallesa Kmr yadda ya buqata babu wasa acikin kwayar idanunshi "Kinga nayi miki kama da dan iska ?sosai kuwa dan gashi naga alama daga zuwa aiki sai ka bige da kai hannunka jikina batare da kayi laakari da ni din matar aure bace ko kuwa budurwa bace ".hakan nan yaji ya tsinci kanshi da adduar allah yasa single ce ba matar aure ba ya sake kai hannunsa tsintsiyar hannunta tayi saurin zare hannunta har agogon dake d'aure a tsintsiyar hannunta ya zame cikin nashi “wai meye haka dan allah nifa matar aure ce kuma tare da mijina nazo aikin nan “ta fad'a hankalinta a matukar tashe shiru yayi yana qare mata kallo qirjinsa na wani irin bugawa da matsanancin karfi wanda baya jin haka akan kowace mace sai akan mafarkinsa.”
ahankali ya motsa labbansa "ko zan iya ganin fuskarki ?"ya tmbyeta yana qara gyara zamansa
"no !ta bashi amsa a matukar tsorace ya sauke numfashi tare da mikewa tsaye ta sake ja baya tana cewa "karka matso kusa dani domin bazan ta'ba kasancewa cikin wawayen mata masu cin amanar mazajensu ba ganin tana nema ta fice daga hayyacinta ya sanyashi kamota hadi da zaunar da ita "lokacin daya kamota wani irin socking ne ya ziyarci zuciya dama gangar jikinsa nan take bugawar da zuciyarsa take ta qaru fiyye da kaida sai dai ya kasa magana a fili sai a zuci "ki natsu wallahi babu abinda zan miki ni kaina bansan meke damuna ba yau , tun da kika kasance tare dani naji komai nawa ya sauya .”
Yayi shiru tare da tsura mata ido ita kuwa banda bugawa babu abinda zuciyarta keyi, neman hanyar guduwa take daga garesa ."yayinda wasu irin hawayene masu azabar zafi suka taru a kurmin idanunta "wallahi ka cuceni tun da nake babu wani nmj daya ta'ba kai hannunsa jikina tun ina matsayin budurwa sai yau dana kasance mallakin wani tana gama fad’ar haka ta fashe da wani irin kuka "okay ki zauna ki qarasa min aikina na sallameki and ki yafe min bisa kuskurena kafin ya gama mgnrsa har ta soma tattara kayan aikinta ta zuba cikin jaka ta fice da sauri ."da sauri ya fito ya biyota yana kiranta "ke!!!
"ita kuwa da sauri sauri gudu gudu ta shiga lift ta danna grand segun ne ya fito da sauri sakamakon jin sautin muryar mai gidansa , cikin gigita segun yace sir meke faruwa ne ?"karka bari yarinyar nan ta wuce ka tsayar min daita !ka tsayarda ita segun amman ina cikin kankani lokaci maryama ta sauka kasa tana goge hawayen fuskarta cike da tashin hankali ta nufi inda motar yaya sadam yake a pake jikinta na wani irin kyarma ta bud'e ta shiga ta zauna kallo d'aya yayi mata ya fahimci tana tattare da damuwa nan da nan ya rud'e ya shiga jera mata tambayoyi "ka taimakeni yaya sadam ka bar garin nan dani akwai matsala "wacce irin matsala ?zan maka bayanin komai idan mun isa gida daga haka bai sake cewa komai ba yaja motarsa a guje suka fara qoqarin ficewa koda segun ya fito har motarsu ta fice daga ma'aikatan ."
Wani irin gudu yaya sadam ke falfalawa akan titi yana cikin gudu ya hango wasu motoci gudu uku abayansu suna biye dashi idan ya rage gudu suma sai su rage gudu haka idan ya qara gudun motar zasu qara "maryama kamar ana binmu ki fad’a min meke faruwa ? ta kasa magana kawai ta fashe masa da kuka dan bazata iya fad'a