Showing 72001 words to 75000 words out of 106121 words
Chapter 25 - kanin Ajali Book Complete by Zee Makawa .txt
daki waje shi zai fita ya kwanta.
Ashe in ya fita ya rufo mu ta baya wai kada barayi su shigo muna sai ya wuce gidan Ruth ya kwana sai asuba zai dawo gida idan yaga gari ya waye.
Duk ban san wanan ba na dai dauka yawan jin zafin shi ne yasa bai iya kwana a cikin gida ashe munafuki dawata manufa yake min hakan.
Ranan ko da na fito da dare sauro ya damay mu sai ban gashi ba wurin da yace yana kwanci din abin ya ban mamaki sosai a raina.
Da safe daya shigo nake tambayan shi ina ya kwana an dauke wuta bamu da maganin sauro na fito da dare ban ganshi ba.
Yace cikin dakewa ai wajen gida ya fita inda samarin unguwa ke kwanci da dare can yake kwana tare dasu sai ban kawo komai a raina ba danaji ya fadi hakan.
Ranan ina zaune na gama girki da rana sai ga matan yayan shi din nan sun shigo gurina na tare su tare da basu ruwa da abincin dana gama.
Sunci sun sha nake tambaya su ina suka fito suke ce min sun fito duba watace a cikin unguwan nan sai ban mai da hankali in san ko wacece suka zo gani ba .
Wai ashe guri Ruth suka zo duba bata da lafiya sai bayan kwana biyu nake ji a gurin wata yar unguwan mu wai ta gansu ranan sunzo gaida Ruth tayi fama da zazzabi.
Abin ya matukar bata mi rai naga yadda muke dasu wai ace sun zo duba farka miji na kuma gashi banda gidan zuwa sai nasu idan na tashi fita unguwa.
Ban kyale su ba har gidan su na samay su suna faman yi min rantse rantse wai ba can suka fito ba ban wani tsaya ba na dawo gida.
Wanan abin sai da ya hadamu fada da jamil yake cewa wai bakin kishi zai kashe ni idan banyi hankali ba nan dai muka kwasa dashi ranan sosai.
Sai banda wani damuwa yanzu sosai don ban gama turmuje yan kudaden dake hannu na ba lokacin don haka yake bina a sannu.
Mijin yar uwana ya samu aiki koyarwa a university da ke kano don haka ya tafi ya barta a nan inda take dan zuwa wurina tana debe min kewa a gidana.
Nan take fadin ba zata yarda ya barta a garin mu ba bin shi zatayi idan ya samu wuri banga laifin ta ba, da take fadin hakan lokacin don zaman mace kusa da miji yafi.
Sai dai ida bata samu anje da ita din ba tayi hakkuri zuwan shi biyu yana komawa inda suke daukan rikici dashi.
Har dai ya yarda zai tafi da ita bayan iyayyen sun sa baki a cikin maganan nan ta fara shiri sai dai bamu fada a gida ba duk shirin da takeyi sai daga baya muka je tare muka fada masu batun tafiyan nata.
Sun yi murna da farin ciki sosai don sam babu bakin ciki ga alamarin su damu sai nuna kulawa da kauna a gare mu.
Wanan abin wani lokaci yana samu jin kunya har da muka fito muke maganan nan dai take fada min wallahi inbi yan uwa in daina bin zancen Jamil da yan uwanshi.
Sosai taimin magana a cikin natsuwa yadda zan fahince ta na kuma fahinta da abinda take nufi don banyi sanyi a gwiwa ba na fara zuwa kai da kai ina ziyaran su.
Tun kan Summaiya ta bar garin sai dai wani abu daya bata muna lamarin shine ita kanta summaiya tayi abinda har ni ya bata min rai da ita sosai.
Don kaya dakin ta gaba daya har kujerun da muka canza ta sayar ba tare da ta fadi a gida ba bayan munce gyara muke son yi a gurin baba kabiru da iyalan shi.
Don sun muna komai da akeyi a duniya nan gaskiya wanan abin da tayi ya bata ran mutanen gidan baba kabiru din sosai don ta fifita uwar mijin ta gare su.
Kayan dakin nata ma karshe akace uwar mijin nata ke amfani dashi kin san abu ga mai kishiyoyi su suka kwarmata ma gidan mu wanan zancen.
Ba yadda zasuyi damu dole sukai hakkuri suka bar zancen duk ko da ransu ya baci ga hakan da tayi masu din don sun fahinci dai bamu dauke su a maysayi iyayyen mu ba.
Mun fi fifita mazan mu a kan su dole kowa yanzu ya kawo ido yasa muna aga iya gudun mu da mazajen namu da muka dauka uwa uba a gare mu.
Sai bayan wucewan su magana ya fara tashi wai da kudin ta mijin ta ya nemi aikun daya samu wai wanan kangon da muka saye babu nata a halin yanzu.
Waya na nema na kirata na fara mata korafi sai bata bari nakai ayya ba ta hau fada tana fadin wai ni a ina naji wana zancen wanan magana ba gaskiya bane duk wanda ya fada mun kuwa.
Haka dai magana ke faman yawo kan mazajen mu sun cinye muna kudaden mu duk wanan maganan da ake fada baba kabiru baice damu kala ba kan zancen mazajen namu.
Kuma ya hana iyali shi suyi muna magana don haka ne zancen bai daga sosai ba yadda wasu suka so cikin dangi a dauki mataki akan mu.
Yakan ce kubar yaran nan inda kuka gansu idan masara taji wuta da kanta zatai kara ai ba sai an tambaye su ba duniyace.
Don yanzu ana magana zasu ce kuna son ku kashe masu aure ne don baku kuka haifesu ba sai yan uwa suce kwarai kuwa Alhaji kabiru.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
5/18/21, 11:57 PM - 🤔🤔🤔: Kamar yadda Jamil ya damu da isowan kudina haka mijin yar uwata ya damu da zuwan su shima sai dai bai yarda ya nuna zalaman shi a fili ba kamar yadda nawa mijin ya nuna .
Don ya fishi shekaru da ilimi da ma wayewa sosai don ni nawa mijin iya secondary ya tsaya shiko wanan har masters yayi a karatun boko.
Wasa wasa har aka share wata uku ba labarin kudin sai abubuwa suka fara canzawa ga matsi da yai muna yawa na talauci .
Mahaifin Jamil har gida yazo ya saka min magana wai sunji rigi rigi sakwat mana ance ga kudinan tafe sunji shiru kuma.
Nace baba lokacin zuwan su ne baiyi ba tukun aida sun sunzo abinda bana mutum daya ba ai sai hakkuri kamar yadda kowa yayi.
Allah karimun rahimun a ckin wata na hudu sai ga kiran baba wai kudi sun sauka muna a cikin dare ya kirani yana fada min haba kamar in jawo safiya a ranan.
Don lokacin Jamil baya gari na kirashi ina fada mai ya yanka wani ihu a waya yana jin dadi kamar wanda ya biyo dare sai gashi koda goma tayi yana cikin garin.
Ina tsaka ga gyara gida ya iso ina yana shiga daki yake fadin to yaya an raba ne nace har yanzu baba bai kirani ba yace kaji ko ?
Kin ga halin yaudara ko in ba haka ba kudi sun zo araba aba kowa nasa mana an tsaya jan rai sallon ayi yaudara da aka saba kuma.
Kallon shi nake da manaki yadda ya hakikance yana fada kan kudin da baida kaso a ciki koda yake shine mai kason nawa wanan zuzudin da yakeyi haka.
Misalin sha daya ya kasa hakuri yana kwance a daki ya kwala min kira na amsa na shigo yake fadin kije gidan nan kiga abinda ake da idon ki zaifi gaskiya.
Ke ma banda abinki an kiraki tun cikin dare an fada maki ba sai kiyi sakkon zuwa gidan ba amma kin tsaya kina shininiki irin wanda kika iya.
Ba abu mai wuya bane gare su su rage yawan kudin kuma nace a a gaskiya yaya za a rage yawan su abinda ke rubuce.
Sai fa baba yaba kowa waya munga yawan kudin ake fara rabawa yace ke dan Allah ja can ke may kika sani don Allah.
Haka ya matsa min dole na shirya na tafi gida naje na samu baba baya gida lokacin don haka na tsaya jiran shi har ya dawo ban raba dayan biyu tunda na tambayi kani Baffa akace sun fita da baba nasan banki sukaje tare cire kudin.
Komai na baba yana kokarin yaga ya fitar muna da hakkin mu amma huduban su Jamil yasa bamu ganin hakan da yake muna sai ma ganin laifin shi idan kudi sunzo da muke yi.
Nan na zauna ranan ba ko sakin fuska suma yan gidan sai suka share ni suna harkokin su kamar ban gidan.
Nakai kusan awa daya sai gasu sun baba sun dawo duk yayi zufa zufa dashi daya shigo, shima kani ya wani daure fuska a lokacin sai da gabana ya fadi na dauka ba kudin ne da sukaje banki ko kuma wani abin ya faru.
Ashe tsare gidane na irin kada aga walenshi ai muna rainin wayau kamar yadda aka tsara mashi din yayi.
Daga inda nake zaune naji hayaniyar su baba musa sun shigo ana bude masu falo ta baya na sauke ajiyan zuciya nasan kudi sun samu ke nan tunda suka zo.
Araina nake zagin su ina fadin ko kunya basu ji da angansu an san abinda suka zo amsa ke nan wai suce suna cin gadon mahaifiyar su.
Kanwata ta shigo da yar diyar ta suna gaisawa da mutanen gidan mu ana wasa da dariya da kowa sai lokacin naga wautana na gimtse masu danayi da farko.
Nan naso saka baki sai wata kanwata diyan baba kabiru mara kunya tace a, a anty hadiza ke da kika shigo kina daure fuska yanzu zaki ce zaki mana magana kuma.
In dai kudine karewa zasuyi mu zama daya kwana nawa ne ance ma mara mata gwauro raina ya baci sosai da maganan ta.
Ina ganin tun kudin basu shiga hannuna ba tayi min baki aiko nan na hau bakina da fada da ita sai inda na tsaya jin muryana da baba yaji ya kirani tana fadin ashe ma na zo don da ya shigo bai lura dani ba.
Nan muka mike muka nufi falo muka samay su kamar kullun baba musa ya bude da addua sai baba kabiru ya dora bayani kamar kullun tare da miko muna wqyan shi yana fadin.
Ga sakon saukan su nan ga fitarwa yana miko muna wayan ga wautana har zan karbi wayan sai kanina baffa yace ai tare mukaje baba ba sai sun karbi wayan ka ba aci gaba dai kawai.
Nan aka fitar da na mahaifiyar su sai aka fara kasafin namu kuma akayi lafiya aka kare kowa ya kama gaban shi don ko minti ashirin bamu kara a cikin gidan ba muka wuce.
Gidana muka yadda zango kamar yadda muka saba yi idan mun fito wurin su baba din nan muka shiga kullawa da warwarewa a tsakanin mu.
Muka gama shaci fadin mu da komai aka shiga kasafin abinda kowa zaiyi shidai karamin mu wanan karon ma cewa yayi duk yadda mukayi ya fita ya barmu nan.
Kamar hadin baki sai ga Jamil da adam sun shigo gidan a tare da Ahmed mijin kanwata sai wani washe baki sukeyi.
Nan mukai masu bayanin komai tare da fada masu yawan kudin da kowa ya samu da wanda aka fitar kason hajiya umma.
Ahmed din yace yanzu abinda za ayi a cire kudi da zai isa kowa sayen uncomplet building a samu a saya kada kudin su lalace muna.
Saura sai muyi lalurar mu dashi shawaran shi anyi na,am dashi sosai already dama ashe sun yanke hakan har sun cigiya muna ko an samu boyewa dai sukai muna kan hakan .
Sukai muna sallama suka tafi haba shiko gogan nawa kamar jira yake su fita cikin tsare gida yace ina kudin naki nace suna ciki na boye.
Ganin yana kallo na nasan abinda yake nufi yasa na mike na shiga na dauko mashi kudin na kawo mai ya karba yana juyawa tare da tambayan na tabbatar kudin sun kai yadda akace ?
Nace sun kai mana ko a na gida sai da baffa ya sake kirga min yawan su yace to may kike ganin za a saye dasu yanzu in an cire wanda za a sai gidan da ba a kammala ba.
Don dai data nice sai in ce kada asai wanan gina ki fara juya kudin har suyi tsoka daidai sayen gida ginane kinga sai ki zuba yan haya a ciki ko may kika gani ?
Ya tambaye ni yana tsure ni da manyan idanuwan shi nace ni dai ayi yadda yan uwana sukace kada ya zamo na fita daban a cikin su bayan mun shirya yin hakan da su.
Tun da yamman nan ya ware wasu kudi wai zai sayo abinci ya fita ban ganshi ba har dare ya dawo min babu kayan abincin wai sai gobe idan ya fita zai karbo.
Washe gari ko sai ga kanwata da mijin ta sunzo sunce an samu kangon gida jamil da baffa suzo suje su gani idan yayi masu.
Sun je sun duba kangaye nada dama sosai don gina da aka fara sun tasa sosai kuwa sukace sunyi masu sai Jamil ne yaso kawo rikici wai kangon yayi tsada ga yadda akace kudin shi.
Nan dai Ahmed ya kara fahitar dashi har ya yarda a saye din aka saye bado yaso haka a ranshi ba ba dai yadda zaiyi ne.
Bayan sun dawo sukai muna bayani har sauran kudi sun rage tun nan a gaban su muka fada masu shawaran da muka yake kan zamu gyara dakunan nmu ne.
Jamil bai so haka ba yana ganin an takura mai da yawa mijin summaiya yace zai tambaya muna set din kujeru masu kyau mu saya zuwa gobe.
An ko samu kijerun shi Jamil ya kawo shawara wai a na saka ties a falo na don shima kunyan azo aga dakin babu ledan kwarai yakeyi.
Shawaran shi ya karbu a waje na da tan uwana sukace tunda zanyi gyara ya kamata a sa ties din a falon sai a bar dakin .
Kamar wata amarya haka dakina ya koma ga ties ga tv plastma harda tauraron dan adam da fridge sabo ga su center kafet an saka a dakin.
Duk da jamil yayi na kasa wurin sa ties di dakin ya kara kudi ga abubuwa da dama sosai amma haka aka gyara dakin .
Duk ko da na bashi nasa kaso daga cikin kudin sai dai kuma bai hana shi yin na kasan ba a cikin dan abinda ya rage min din.
Labarin baba kabir kuwa tunda ya bamu hakkin mu bai kara bi ta kan mu nasan don tsage rancin da muka nuna masu ne lokacin rabon kudin da Baffa yace wai dole ne sai an cire na mahaifiyar su .
Sai kuma wanda baba ke bi a ciki na fafitikan neman muna kudin ya fito da yake kai cin hanci da sauran su wurin duk wanda ya dace ayiwa.
Kuma gashi mun sani baiyi shi kadai sai da sanin mu idan za a yi don ko an lalubu mu kudin bamu dashi balle mu bayar din.
Dole haka aka fitar mai da abin shi duk da ma bai cire na jigilan shi ba yace ya yafe muna su amma duk da haka sai da dan hakin shi ya tsone muna ido.
Kada kukaga laifina masu karatu gama in kun tuna na fada maku sai da suka raba mu da kowa namu sai su mazajen namu da kannen mu biyu kawai muke shawaran mu.
Do haka komai sukace sai muga ai sunyi daidai ba ba mu ganin rashin dacewan hakan a gare mu tunda yanzu su zama muna uwa da uban mu a yadda suke fadi ko yaushe.
Don haka muka dauke su da zuciya daya ban ko tuna saura saki daya fa tsakani na da Jamil din duk da dai ban fadi a gidan mu ba kowa ya sani.
Dakina yanzu har zuwa kallo akeyi koda yaushe tv na aiki a falon yan diyana suna zaune suna kallo basu zuwa dakin kowa na gidan da sunan kallo.
Yanzu zamzam muke da Jamil baison ko kuda ya tabani ko diyana a gidan sai dai ban sani ba ashe har lokacin suna tare da Ruth farkan shi.
Ba wanda zai iya fada min don ban iya boye mutum wurin magana shiyasa kowa ke tsoron fada min gaskiya koda an gani sai a kyale ni gashi wanan kawar tawa sun tashi tabi mijin ta can kasa ibo inda yake.
Don da tana nan data fada min idan ta san da hakan ba zata boye min ba kamar yadda mutane suke boye min yanzu.
Duk da na gyara daki yanzu tsiyan daya tsiro min shine sai yace bai iya kwanciya a dakin wai zafi yayi yawa a daki waje shi zai fita ya kwanta.
Ashe in ya fita ya rufo mu ta baya wai kada barayi su shigo muna sai ya wuce gidan Ruth ya kwana sai asuba zai dawo gida idan yaga gari ya waye.
Duk ban san