Showing 48001 words to 51000 words out of 191310 words

Chapter 17 - ABU CIKIN DUHU BY MAKAWA By abooks.com.ng.txt

ta.
Umm, umm inda wanan da wanan gaskiya amma hakan ai ba zai jawo wanan tsanar haka ba a tsakanin ku tunda mami bata ragesu da komai ba su din ma tana nuna ita ta haifemu ga baki daya ai ga nawa ganin.
Anyway koma dai meye ki kara nisa dasu duk da nasan kina hakan zangan su inyi warning din su ba tare da zancen yakai kunnen mami ba.
Nagode Anty Aisha nace a sanyaye koba komai ta nuna min kaunarta a gareni ai tunda na samu kula a wurinta.
Muryan tane ya katseni tana fadin ke din ce zeey da shegen kyau wallahi kila hakan sukewa kyashi kin san mu mata ai yadda muke.
Nima kaina shigarki ta jiya saida naji kamar karna baki kayan nan don ban dauka haka suke da kyau ba.
Saida nagan ki dashi a jiki nasan yadda sukewa mutum kyau ashe idan ya sakasu don jiyan nan gaskiya kin dauki hankalin mutane da yawa gaki kuma tare da big boss da yan mata da yawa a wurin suke son kasancewa tare dashi.
Sai kawai aka ganki dashi by surprice kin ba kowa mamaki a wurin sosai don ba wanda ya zata hero zai tsaya duban wata mace ko wacece .
Saidai bamu san sirin ba don abin ya bawa kowa dai mamaki gaskiya har mami kanta tayi maganan haka.
Tausayina yaji shine kawai anty Aisha kin san irin ku irun tausayin na kasa dasune .
Kafin tayi magana wayan ta yai kara ta dauka sai naji tana fadin gamu a falo tare da ita yasa nayi saurin dagowa ina duban ta.
Kije mami na neman ki a daki ina jin haka na mike da sauri zuwa amsa kiran mami din yayin da Anty Aisha ta bini da kallo har na shige dan lungun da zai sada mutum da dakununin gidan.
Zaune na samu mami tana duban wayan ta, na shigo da sallama ta dago tana fadin duba min ko masu girki sun gama a kawo min nan don bazan fita dakin nan yanzu ba hutu nake so yau.
Da sauri na tashi zuwa kitchen din inda na samu anty Aisha tabar falin ita ma na shiga kitchen na fadawa madu aikin sakon mami din.
Nan danan suka shiga hada hadan hada nata abincin cikin wani katon try na dauko na kawo mata .
A dakin na samu anty Aisha tare da uwar suna magana shigowana sai sukai shiru mami na kula da tana bina da kallo kafin nace ga abinci mami.
Yau ajeshi nan don har ruwa da drinks sun saka a ciki na juya zan fita take fadin zo nan zeey na dawo da sauri zuwa gareta.
Nakai kasa take fadin yau zeey yaya akayi na ganki tare da jafar jiya a gurin buki ?
Da sauri na dago kai ina fadin Jafar mami a, a bani bace nikan da yayan nan da yazo na tafi koshi an barni ni kadai a gida sai tsofi na fita waje na zauna shine da zasu wuce yace inzo mu tafi shine na bishi mami.
Ok mami tace yayin da take saukowa saman gadon don wani lokaci mami a kasa take zama taci abincinta.
Saida na tsaya na zuba mata ta fara ci tana fadin oya dauki wanan sauran kije kici don nasan bakico komai ba yanzu haka.
Na dauka tare da fadin na gode mami na fita da ture din a hannu na ina murna zan sha ferfesun kai yau har in bari duk da ina ci sai dai diban tsoro nakanyi wa abinci wanan kuma an bani shine kai tsaye.


ZAINAB IDRIS MAKAWA








🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅


1️⃣5️⃣


ZAINAB IDRIS MAKAWA


IDAN NACE NA KUDINE INA NUFIN IDAN KIN KARANTA BAKI BIYA BA INA BINKI BASHI KO ?



Ranan nasha dadi don a dan lungun shiga dakin mami na zauna a kasa na kwashi garabasa na a wurin ina tsotson kanshi ne su yaya mamud suka shigo zasu shiga dakin mahaifiyar su su uku babu jamal a cikin su.
Kunya ne ya kamani yadda suka sameni ina gwigwiyan kashin kafan saniya ina kuma tsotson ruwan miyan da ya lake a cikin sa don dadi.
See dis village girl jalal ke fadi dubeki don Allah a kasa kika wani zauna kamar wata kazama can.
Dan kallona yaya mamud yayi ya kawar da kanshi gefe daya yana fadin wai a ina mami ta samo wanan yarinyar ne ?
Haka yayi daidai da shigar su dakin mami din inda direct wurin da mami ke zaune a kasa Jafar ya nufa ya zauna a kasa tare da karban cibi a hannun mami din.
Kallo shi mami tayi kafi ta mayar da kallon ta ga mamud tana fadin me naji kana tambayane ?
Sai jalal din yace dis your village girl mami kinga yadda tawani zauna a kasa tana cin abinci kamar wani zai daka mata tsawa ta sheka a wurin.
Ina ruwan ka da ita mami tace tana kawar dakai zuwa kallon Jafar da yakai ruwan miya a bakin shi ya fara taunawa da kyat kamar an sashi ci dole.
Yanzu haka nasan baka karya ba tun safe maimakon yai magana sai cikin shi ya shafa yana lumshe idanuwan shi a hankali.
Yaya jalal zainab tana da gaskiyan ta ta fita falo kuma a zageta shiyasa ta labe nan nasan tana ci hankali kwance.
Waye zai zage ta mami ta fada a hasale ciki ko in kulla kai tsaye tace your daughters don dazun nan na raba ta da Rufaida a falon .
Wai kawai ta zauna a kan kujera in kaga yadda Rufaida kewa yarinyar nan abin ba kyau wallahi .
Shine na zauna da zeey din ina tambayanta take fasin bata san abinda tayi masu ba suka tsane ta ita zagin ne ke ci mata rai dasu ai sosai.
Wanan Rufaidan badon mahaifinta ba da nake jin nauyin shi a yanzu wallahi akan yarinyar na dana mata tsiya sosai a gidan nan ko ta koma gidan su.
Mami akan wanan yarunyar har kike fadin haka yarinyar fa ba yar kowa bace balle har ki fadi haka nasan shi, , , ,
Karbi nan jalal mami ta jefa mai dakuwa da hannun ta tana fadin uwarka ma kaji ance ba yar kuwa bace face dagacin kauye.
A haka kuma mahaifin ku ya aureni har muka haife ku ka san mai Allah zai mayar da ita gobe ita kanta Rufaida data sani da batai mata hakan ba don Allah yasan goben ta.
Yaya mamud yace ni ban ma san yarinyar ba shine yanzu nake tambaya ko wacece ita ina dai yawan ganin ta gidan nan all d time idan na shigo.
Ina zaka sani tunda ba a gida kake zaune ba itace yanzu mai koyawa diyan ka karatu a gida .
Yace so tasan abu ke nan sosai ma mami ta fada tana budan baki ta karbi abincin da jafar ya debo ya bata.
Ni dai bana son takurawan da su rufaida ke mata Allah mami yarinyar tana cikin damuwa haka sosai wallahi.
Ido ya runtse kafun ya bude ya juyo yana fadin you are too talkative now kin fadi wanan maganan tun farko yake cewa Aisha.
No mami ta tsawata masu su daina muzanta ta don yarinyar she is beautiful sosai sai dai tsiyar abin yar tallakawace ita.
Mamud ya fada yana gyara zaman shi oh shi tallaka ba mutum bane ko don kawai tana tallaka sai akace a muzantata.
Is OK mami ku bar zancen nan don Allah ya fada rai bace yana kai mata cibin abinci a bakin ta ta karba.
Sai mamud ya kwashe da dariya yace mami ba fa nufina ke nan ba kin sani so iam sorry for dat ta dago tana hararan shi kawai.
Hummm hummm in dai a kan wanan maganan ne mami zatayi fada da kowa ai a gidan nan na rasa me wanan yarinyar tazowa mami dashi haka.
Anyway naji suna fadan wai sun asirce mami ne ita da , , , ,
Jalal getout bana son yawan zuba haka tin dazun nayi warning kan zancen nan kun kama magana kan abu daya haka.
Yana gamawa ya mike tsaye zai bar dakin mami tace ina kuma zaka zansa a kawo maku abinci kunci yanzu a gabana.
But mami , , , shiru yayi don hannun data daga alaman yai mata shiru dole ya dawo ya zauna waya ta daga ta kira wani layi tare da bayanin abinda za ai mata.
Kafin wani lokaci an hada dining din tashi sukayi tana gaba suna biye a bayan ta a falon dai nake sai dai ba a zaune ba ina gutfane raben jikina na saman kujera hankalina yana gun kallon tv dake aiki tun safe a falon gashi ban iya canza chenal din ba, don haka nake kallon dole hakana.
Zeey kina nan kina kallo mami ta fada saina dago da sauri don jin muryan ta danayi ina fadi cikin fara, a sannu da fitowa mami.
Namike tsaye tace no koma abinki ki zauna don me baki zauna da kyau ba ta fada kamar bata san abinda ya faru ba tsakanina da Rufaida da rana ba.
Dan murmushi nayi ta nuna min kujeran tana fadin zauna sama daga yau duk abinda kike son yi a gidan nan kiyi shi kamar kowa kinji abinda na fada ko ?
Na gyada kai ina kaiwa zaune Nazifa dake fitowa daga kitchen a gaban ta mami ke min fada ta juya zuwa dakin su nasan zata fada masu abinda mami ta fada min ne yanzu.
Mami basu bar wajen ba sai da magariba ya kawo jiki suka mike don zuwa sallah lokacin har na fita naje waje don yin alwalani.
A wajen suka sameni sai dai ban samu gaidasu ba suma ba wanda ya kula dani kuma sun ganni din wurin ina alwalan.
Na dawo na samu mami ta shige dakin ta nan falo na tayar da sallah sai da na idarne Rufaida ta fito tazo ta tsaya a kaina tana fadin.
Sai kin bar gidan nan munafukar yarinya kawai don nayi maki fada kan hawa kujera dazun shine kika fadawa mami ko ?
Da sauri na dago kai tare da fadin wani bamuyi wanan zancen da mami bani .
Rufamin bakin nan naki mai warin tsiya zaki cikani da surutun tsiya to bari kiji tunda nan ba gidan ubanki bane sai kin barshi walla, , , ,
Ke menene haka me tayi maki keki zaginta haka kawai don cin zalin zaki saka yarinyar mutane da zaki haka.
Yaya mamud ne tsaye daga bayan mu yake fada da Rufaida ta dan tabe baki tana fadin wallahi yaya yariny sai yace wanan ba daidai bane ya juya ya nufi dakin mami rai bace.
Yana shiga yake fadin mami gaskiyan Aisha yaran nan sun matsawa yarinyar nan haka ashe yanzu na same su a falo rufaida na shirin dukan ta badan Allah ya kawoni ba data kai ga dukan nata ma kila.
Innalillahi me yaran nan suke nufi newai kan yarunyar nan a to mami indai zamanta nan tare dasu zai zama matsala gara dai ki sallameta yace tare da mika mata ledan maganin daya sayo mata.
Ranan ma a dakin mami na jena kwanta a kasa kamar yadda na kwana a jiya a takure don gani nake idan nayi dogon motsi zan dameta a dakin ta.
Washe gari tunda na tashi nake jin kamar zazzabi a jikina hakana na daure nayi duk wani aikin da zanwa mami nayi shi cikin daurewa.
Inda Allah ya taimakeni mami ta fita tun goma na safe na samu na shige dakinta na kwanta ba tare da nasha magani ba.
Har lokacin da mami ta dawo daga unguwa data fita ta zauna falo bataji motsina ba kota ganni da ido sai tambayan mutane take suna fadin suma tun safe basu ga giccina ba.
Aka kama fadin ina na shiga hankalin mami ya tashi ranta kuma ya baci dani sosai kan hakan don dai tasan ban san kowa ba a garin.
Saida mami ta shigo dakine ta ganni a kwance na dunkule cikin hijjabina ina rawan sanyi.
Ja tayi ta tsaya da mamaki tana fadin ke zeey lafiya ko kin shige daki kin kwanta kin tayarwa mutane da hankali.
Jin muryan mami sama sama a kaina yasani bude ido da kyar na buda baki jikina na rawa zazzabi mai karfi nake fadin massarara nake ji mami tunda na tashi da safe.
Jin haka yasa ta karaso inda nake kwance tana fadin saiki shige daki ba tare da kin fadawa kowa ba ki rufe kanki a ciki don rashin wayau ko me ?
Da kin fada da an samu wanda ya baki magani ko a kaiki asibiti kinzo kin shige hijjab kina rawan sanyi haka kinki jan bargo saman gado ki rufe jikin ki dashi.
Tana wanan fadan takai hannun ta a jikina tana tabawa taji zafi radau da sauri naga ta juya ta fita dakin.
Sai gasu da jamal da Jafar sun shigo dakin da saurin su jamal ne ya kai hannun shi saman goshina yaji zafin da jikina yayi da sauri ya cire hannun shi yana fadin mami dis is serious fa jikin yayi zafi sosai.
A hankali yaya jafar ya tako zuwa inda nake kwance saman rough shima ya taba jikin nawa wani irin shock ne ya ratsa jikina lokaci guda duk da yanayin zazzabin da nake ciki haka bai hanajin wani yanayi da ban san na meye ba lokacin.
Idona na runtse daga inda nake kwance nunfashina har yana sarkewa yayin dashi har lokacin yana duke a kaina ya dago yana fadin les take her to the hospital dis is serious mom.
Mamice ta dagani daga kwancen da nake sai na kasa tsayi tsaye da kyau jamal kamata da kyau a kaita wurin mota mami tace.
No barta a kira wasu daga cikin yaran nan su taimaka su riketa zuwa motan ya fada yana juyawa ya fita daga dakin.
Fita yayi ya tsaya yana fadin matar dayaga tana falo ta kira masa sisters din shi dakin su don baisan dakin da suke bama.
Sai gasu sun zo suka same shi tsaye inda kowa sai mamakin kiranda yake masu sukeyi don da farko da matar tace shine basu yarda ba saida suka fito suka same shi a tsaye yana jiran su din.
Bai tsaya kallon su ba ganin sun fito ya juya yana fadin help dis girl please kallon juna sukayi don basu gane wace yarinya yake magana a kanta ba lokacin.
Ganin ya nufi dakin mami suka bi bayan shi sai ga mami ta fito tana ganin su tare dashi tace yawa don Allah wata ta taimakawa zainab zuwa wurin mota mu kaita asibiti.
Jin an ambaci sunana yasa Nazira ta fara ja da baya Rufaida ko ko motsi batayi ba a inda take sai salma ne tace mami bata da lafiyane dama.
Wallahi salma ki san yarinyar nan bata da hankali bata jin dadin jikinta ta shige daki ta kulle kanta a ciki haka.
Salma ta matso tana dafani tare da fadin sannu zainab tana kokarin tayar dani zaune.
Haka ta dan rikeni har zuwa wurin mota data ganshi tsaye shida jamal an bude kofar motar.
Mamine tacewa salma shiga salma muje tare don Allah da sauri tace to mami ko mami ta dauka driver ne zai jamu sai ji tayi yace jamal shiga muje tare.
Turkish hospital ya nufa damu da kwantace har ya gane wurin munyi sa, a akwai likitoci bamu dade ba muka shiga bayan yankar katin da jamal yayi baisan sunan baba na ba dole sunan mahaifin su yasa a katin don sauri.
Tare da mami muka shiga ganin likitan ya dubani bayan yan tambayoyin da nake amsawa da kyat gareshi.
Allura da maganguna aka ban sunso wai su dan kwantar dani mami tace aimin dai allura mu koma gida washe gari sai indawo in karbi sauran allura.
Haka muka juyo muka dawo gida zuwa lokacin har na fara dan jin saukin jikina haka muka shigo gidan a falo muka samu wa yanda suke gidan a lokacin.
Da ganin su akwai maganan da sukeyi a lokacin don yadda suke gaida mami da dawowa ba wanda ya tambayi yaya jikina daga cikin su.
Dakin mami ta kaini ina jin anty salma na fadin ku baku iya gaida mara lafiya bane ?
Ta fada tana shigewa dakin ta suka bita da fadin Amebo Olopopo suna hararan inda tabi zuwa dakin Nazifa tace waya sani.
Ko taje ta daukowa mutane ciki ne a gida Rufaida tace ko cikin wa yan nan katan na waje wani ya taushe yar iska yafi karfin ta ba.
No ku daina fadin haka don

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login