Showing 9001 words to 12000 words out of 191310 words

Chapter 4 - ABU CIKIN DUHU BY MAKAWA By abooks.com.ng.txt

mi hannun ka mai sanda.
Dan hira muke jefi jefi mukaji muryan saliha ta dawo tana tambayan kitson ina jin tana kwada sallama lantana na fadin wai waye haka ke damun mu da sallama ne.
Fitowa nayi daga dakin inna ina amsawa tare da fadin saliha shigo dama yanzu inna ke gaya min kin zo ai ina barci.
Saliha race wallahi nazo ko zan samu ki kwashe min kai zamu birni wurin bukin dan uwan maigidan mu ne.
Nace bissimilah shigo bari na dauko tabarma na juya zuwa dakin innan mu na dauko mata tabarma muka zauna zaman kitson.
Na koyi kitsone akan yan kanne na don yawan yawon neman kitso da kashin kudin da inna takeyi kan kitson mu.
Wanan yasa har na koyi kitso ina zama in masu har na hannu na iya ba wevean ba kawai don ina dake son kitson hannu wanan kuma a kanta na koya.
Yanzu kuma in muna makaranta nakan koyi kumshi a pepper har na fara zanawa kannena sai dai ba sosai na iya ba.
Wasa wasa tun daga ranan da naiwa saliha kitso mutanen unguwan namu ke shigowa wurina yin kitso ko su turo yaran su in masu.
Sai ya kasance har na fara mantawa da zancen hanani karatun da umma tayi yanzu.
Ga kudi baya katse muna dan abinda zamu kashe a kauye baya buwayan inna yanzu.
Don a wuni akalla muna dan rike dari biyu ko dari uku tundai idan akave weekend ne don ba wani kudi bane mai yawa kudin kitson kauye talati hamsim ne wani a kyauta zan mai ya tashi.
Ga Abba abin kara lalacewa yayi mai tun shigowan Lantana gidan shi abinda zamuci ma yana batun gagaran mu a gidan.
Don haka muke dan dora karamin tukunya mu dafa dan cimar da zamuci iyamu damu don Asabe ta fara a gaban mu zata dan dafa abu.
Saidai muji tana kwalawa Lantana kira tazo ta karba idan lantana ta karbo a gaban mu zasu zauna suci har tana santi don muji haushi.
Wani lokacin yan kannen mu sai su sa ido suna son ci sai inna ta doke su ko Asabe ta dinga fada ita ba zata iya ciyar da taron yan mata ba uwar mu data haifo mu ta nema ta bamu muci.
Da ku mazane ai da bamu kai haka ba a gidan nan da yanzu kuna wurin nema kuna taimakawa mahaifin ku.
IIrin wanan maganganun na kakar mu yasa muka dan fara dafa tukunyar gefe don kada kannen mu su koyi daukan ido ta wanan dalili.
Ranan inawa wata makwaciyar mu kitso kanwa saratu tana dafa fate don shi zamu gyara muci don Abba bai kawo komai a gidan ba tun safe.
Girkim ya dauko kamshi duk ya dume gidan da kamshi saratu na bakin murhu tana faman fita wuta don iccen baya ci sosai.
Sai ga lantana ta fito lungun Asabe gurin kwata inda muke wanke wanke kakarin amai ta fara da karfe da yaji.
Sai duk mukayi tsaye cirko cirko muna kallon ta da mamaki don bamu dade da jin dariyan su ba da asabe kamar ba sarakuwar ta bace lantana.
Sai ga Asabe da sauri ta fito tana salati tare da fadin yau may zangani haka Lantana lafiya meya same ki ?
Asabe ke tambayan ta a rude sai ga inna ta ma tafito daga dakin ta tana fadin Lantana meya faru.
Ganin Lantana na nuna gurin da saratu ke girki da hannun ta alama dai warin girkin namu wai ya jawo mata aman a yanzu.
Ja inna tayi baya don ta fahinci makircin da Lantana ke shiryawa a kan girkin da mukeyi din don muci tun safe bamu karya ba.
Wani guda mukaji Asabe ta sake wanda bamu fahinci ko na menene ba sai da tace .
Ahhaye nanaye Allah nagodema yau magaji ya bayana a gidana da yardan Allah.
Ta juya wurin saratu tana fadin ke kashe wutan nan ki bar girkin nan kada kija min hasara a gida don ku ba damuwan ku bane tunda bata son kamshin dahuwan naku.
Saratu ta mike tsaye ta fara buga kafa tana yaya zan kashe wuta kina ganin tun safe bamu karya ba.
Kada ki kawo min diban albarka nace a kashe wutan ku mutu idan bakuci ba mana waya damu daku wanan matsalan uwarku ce.
Wallahi bazan kashe ba tunda bai dahu ba saratu ta bata amsa saiga inna ta laiko daga daki tana fadin saratu jaye itace don Allah banson gardama da manya.
Tamayi gardaman dani Asabe ta fada tana nufar wurin randan ruwan mu ta debo ruwa a roba tana zuwa ta lemawa itacen da garwashin wuta lokaci guda wutan ya mutu.
Aiko saratu ta sake wani uban ihu tana fadin wallahi ban yarda Asabe tunda ba bamu abinda zamuci zakiyi ba tana magana ta nufi wurin murhun tana hawaye.
Muryan innace ke fadin karkiyi barshi hakana kuci ko bai dahu ba idan zai ciyu.
Wallahi inna bandade da zubawa ba tazo ta kashe wutan matar makwabtan mu da nakewa kitsone tace dauki dahuwan ki shiga gidan mu ki karasa girkin naki don Allah ku bar wanan magana.
Saratu tana sharan hawaye take fadin wallahi Asabe saina rama don ba yarda zanyi ba kun dafa naku kunci zaki hanamu dafawa yanzu.
Ranan dai sai gidan makwabciyan mu saratu ta karasa dafa abincin da zamuci ga Abba bai dawo ba har dare don haka da bafon faten ba haka zamu kwana da yunwa a ciki mu.
Saida safe ne nake jin muryan Abba cikin jin dadi yana fadin masha Allah abu yayi kyau Allah ya raba lafiya.
Ma,ana dai watau lantana ta samu ciki a gidan mu ke nan ni banji komai a raina ba a lokacin .
Don ban gama mallakan hankalin kaina ba da zan gane may hakan ke nufi damu sai can naji muryan Abba nawa saratu fada don me tayiwa Asabe rashin kunya kamar Abba zai doki saratu din.
Ban san ina Asabe ta tafi ba wai ashe ta fitane zuwa gidan wata mata mai bada magani ta ansowa lantana maganin baki kada innan mu ta zubar mata da cikin jikin ta.
A daidai wanan lokacin saratu ta shige lungun Asabe ta fasa mata babban randan ruwanta ba wanda yasan da shigan ta har ta fito daga sashen.


ZAINAB IDRI MAKAWA










🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅


4️⃣


ZAINAB IDRIS MAKAWA


LITTAFIN KUDINE DARI UKU NE KACAL GA MAI BUKATA TARE DA IMANI DA SANIN AKWAI HISABI GOBE KIYAMA.
DON ALLAH YAN UWA MUJI TSORON ALLAH GA DAUKA HAKKI A KAN MU TA WANAN HANYAN SAYAR DA LITTAFI A ONLINE MUKE SAMUN CIGABA DA RUBUTUN DA MUKE MAKU KADA KIJI HASARAN BAMU HAKKIN MU KODA KADAN NE .


Sai salatin Asabe mukaji a tsakar gida tana ta faman rabka salati da fada tare da zagi ga duk wanda yai mata wanan aikin.
Babu wanda ya tanka a cikin mu har innan mu saiga Lantana ta fito tana fadin meya farune umma ?
Meye ma bai faru ba randar ruwana tun tele tele na samu a fashe yau sai nasan wanda yai min wanan ta,asan a gidan nan ta fada tana zare ido.
Lantana tace kema umma da wani zance kike ai wa zaiyi wanan banda yaran gidan nan ko Akuyar ki ta fada mata.
Badai Akuya ba su din daine zasu aikata min haka saboda bakin ciki da mugun hali yau dai ai za,a yita ta kare ko a biyani randan ruwana ko kuma yasan inda zaiyi dasu nagaji wallahi .
Ta karasa tare da juyawa wurin randan ta nufa tana hada guntayen sakainan da suke wurin a warwatse a kasa.
Ranan wuni jininin wanan abin tayi babu wanda ya fito yace shi ya aikata hakan sai lantanane ke taya ta fadan.
Abba na dawowa da wanan zancen aka tare shi kira ya kwalawa innan mu dake daki ta fito.
Cikin yaran nan wayaiwa umma wanan barnan ya tambaya yana kallon fuskan ta.
Malam ina zan sani tunda ba yawo nake dasu ba balle duk cikin su babu wanda ke yawan shiga wajen umma ko tana nan balle bata gidan yau tun safe.
Asabe tayi caraf tana fadin waya sani ko ita dince tayi wanan abin don kawai tsaban bakin ciki dake cinnta.
Aure daine na karawa dana ga kuma abin arziki har an samu saidai bakin ciki ya kashe mutum din sai anyi ma yayan ki dan uba a gidan nan.
Wanan bai taba damuna ba umma kin sani in ma za a karo mai biyune rana guda su shigo su haihu a rana daya bai taba damun rayuwana.
Kana dai jin wuyan matar ka yayi kauri har tana fada min bakar magana haka a gaban ka.
To kisha kurmin ki wanan din ce dai guda na aura mai kuma baki so hakan ba dake da diya matan naki da suke tayaki kishin.
Allah ya baku hakkuri umma randan ruwa ne dai ban san wanda ya kashe maki shiba .
Makirci daine kiyi tayi aiga diya mata nan maki zube a gida har yau babu wanda ya sallama da sunan kiran su.
Shiga dakin inna yayi daidai da soma fadan Abba Asabe na fadin in fito da miji cikin samarina Abba yace kwarai kuwa da gara dai in fara rage su nima zaifi min sauki tunda har sunyi wayau yin hakan yanzu.
Idan ma bata da tsayayyene akwai wanda zan hada ta dashi ai shi a shirye yake ko yanzu idan har na bashi.
Abba yace a, a umma gara dai a bari ta kawo din da kanta zaifi tunda kin ga yadda yar gidan muddi suka kare kan hakan yanzu.
Gashi kullun maigari maganan shi ke nan a bar yara su zaba da kansu da ai masu dole.
Ai ba dole bane tunda shidin wanda zan hadasu din yana son ta ai itama zata so shi tunda bata kaishi gata ba.
Koma dai menene umma don Allah kada a soma hakan banda zarahin zuwa birni sharia tunda kinga can ake kai mutun kai tsaye.
Jin hakan yasa Asabe tabe baki tana juyawa zuwa wurin ta tare da fadin ni banga ranan haihuwan diya mata ba a rayuwana ko kadan.
Inna dake daki kuka take darza a hankali batare da fitar da sauti ba balle wani ya jita.
Alwala nayi na nufi dakin ta sanin Abba ba dakin yake ba na samu inna zaune tayi tagumi a wurin data idar da nata sallah.
Inna kada zancen su Asabe ya tayar maki da hankali har ki shiga damuwa tunda bake kika ba kanki diya mata ba ai.
Meye laifina a cikin wanan zance yar mairo don kawai na haife a mata yasa umma ta dauko tsangwama ta dora min ni meye nawa a ciki.
Su suke raina diya mata ina saboda in kin kula Asabe ba da bukatan ilimin addini ko kadan ne matar da ko alwala bata tsaya ta koya ba .
Idan kuma za a gyara mata tace ina mutum ya fito ta kashe shi ai kinga fadin hakan daga bakinta ba abin mamaki bane jahilcine ke damunta daga ita har yar koran nata.
Bashi yafi damuna ba yar mairo yadda yanzu mahaifin ku yake kokarin juya min baya tun lokacin zancen cikin matanshi da umma tayi.
Ina kallo zai sayo mata abu a gaba zai bata idan nayi magana yace min tana da lalura dole a lalabata ai.
Inna kema idan kina son abin ai sai ki fitar da kudi ki saya idan baifi karfin ki ba kiyi hakkuri ki saka masu ido Allah ba azzalumin kowa bane ai.
Sallah nayi har na idar tana zaune tana faman tunane kafin ince niko inna sai nake ganin kamar saratu ne tayi wa randan ruwan Asabe ta,asa don abinda tai muna ranan .
Don dazun naga sanda ta fita zuwa lungun Asabe bata dade ba ta dawo daki tana dariyan kyata.
Amma idan itace ta aikata hakan sai na bata mata rai yau inna ta fada a hasale.
Da sauri na tare inna ina fadin a, a inna idan kin doke ta zasu gane kiyi mata fada kawai don Allah idan ta shigo.
Kwafa innayi ba tare da kara furta komai ba ta mike tsaye ta tada sallah don isha,i da ake kira lokacin.
A daidai lokacin saratu ta shigo gida tana wakan ta mai kama da habaici a fakaice .
Gamu munzo taron dangi, bama tsoro kugafar bama tsoro har zuwa karshen wanka tanayi tana rawa kafin sallama ta shigo dakin inna kai tsaye.
Ganin muna sallah yasa itama ta juta ta suri buta ta shiga bandaki ta dade a ciki kafin ta fito tayi alwala lokacin har sauran sun shigo dakin ko suna sallah.
Nice na fara idarwa don Inna ta tsaya dogon adduan da takeyi bayan sallah.
Fatima ki tashi kuci abinci kada kiyi barci bakuci abinci ba cewa da yar karaman kanwar mu data kwanta tana shirin barci.
Mikewa nayi don in raba muna abincin da mukayi tunda rana tuwo ina tayi muna da miyar ganye da gyada shine mukaci da rana sai koko da take cika roba ta aje don mai yara bata yarda ta rabu da koko a dakinta a kauye.
Saratu na shigowa take fadin yanzu ma tuwon ne zamu kara ci nace idan kin tanadar muna wani abin ba sai kici ba.
Sallah ta tayar har ta idar daga inda take fadin Abu bani abinci na zanci in kwanta ne yau barci nake ji.
Ba zaki biya karatun ki ba ke nan yau barci zakiyi tace na gaji ne yau sosai na dibar muna abincin sai da muka faraci dakin hayi tsit a lokacin.
Don inna ta horemu da hakan tun muna yara har muka gama kowa yaje ya wanke hannu muka dawo tana gyara wurin kwanciya inna tace.
Saratu may yakaiki wurin inna har kika fasa mata randar ruwanta yau don kawai ki jawo min sabon masifa cikin gidan nan ina fama da kaina.
Juyowa tayi inda nake ta dan kalleni kafin tace wani inna wallah, , , , bata karasa ba don tsawan da inna ta daka mata da rufe min baki tun kan na mareki wurin nan.
Shiru tayi har inna ta kare mata fada bata sake magana ba don fada sosai inna tayi mata tana shiru har inna din ta gama.
Ina jin tayi shiru nace ni inna gaskiya gobe zanyiwa Abba maganan karatuna gashi har zamu fara exam din shiga wani zango ban tafi ba.
Idan kinga zaki iya ai gaki gashi nidai babu ruwa na tunda kikaji umma tace kin daina boko to ki barwan nan zacen a hakan.
Har muka kwanta ba kara magana ba sai faman tunane nake a raina don ba abindake damu kamar rashin karatu da ban fita yanzu na riga da na kwallafa rai ga boko nace ni nurse zan zama idan na girma.
Washe gari baba bai fito dakin lantana da wuri ba har kowa ya gama shiri ya fita don sauran suna zuwa makaranta basu fada kangin Asabe.
Hankalina yana wurin fitowan baba daga daki lantana sai wuran goma ya fito tare da ita tana mai rakiya don kawai kada yace zai biya wurin innar mu su gaisa.
Har yasha dan kwanan fita daga ciki gida na fito da sauri na same shi ina fadi Abba ina kwana.
Ya tsaya tare da juyowa yana fafin yar mairo kun tashi lafiya ina kannen naki sun fita ko ke nan ?
Nace a sanyayaye sun tafi baba sai na fara hawaye daga inda nake tsungune ina dan gogewa da gefen hijabi na.
Me ya sameki kike kuka haka da safe Abba ya tambayeni cikin kullawa kasa bashi amsa nayi sai sharan hawayen da nakeyi a lokacin.
Lantana dake tsaye gefen shi kamar bodyguard din shi ta tabe baki tana fadin ya wuce dai zancen auren ta da umma ke fadi.
Kai haba lantana wani zancen aure kuma yanzu gun yar mairo adaiyi hakkuri ta karasa karatun nan datasa a gaba har kwana nawa yarage ta karasa idan muna raye.
To ai naga kai umma take tausayawa a cikin zancen nan kamar rage maka nauyine umma ke kokarin yi ga hakan.
Ya juyo wurina yana fadin kinga yar mairo kije kiyi hakkuri har in zauna da umma in fahintar da ita ko Allah zai bamu sa,a a kanta.
Lantana dake jin mu ta karyar da kanta gefe tana fadin gamu gani ai indai umma ce a gidan nan.
Na bude baki da kyar ina fadin don Allah Abba ka taimaka min na karasa karatuna ko iya secondary din ne in tsaya.
Taysayinane ya kama Abba lokaci guda sanin yadda gun ina kankanuwa nake son boko har irin dagewan da nakeyi kan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login