Showing 174001 words to 177000 words out of 191310 words
Chapter 59 - ABU CIKIN DUHU BY MAKAWA By abooks.com.ng.txt
dan Allah.
Har zuwa lokacin baiyi magana ba sai na kara dukar da kaina kasa ina wasa da yatsun hannuna a hankali.
Hannu ya tura a cikkn aljihu yana fadin nasan matar malam ta gaji da zama a garin nan don haka gobe za a mayar da ita gida ita kuma halimatu tunda tana karatu sai a barta a nan tare dake .
Kai na dago da sauri ina kallin shi wanan karon nan kawar da idona ba daga kallon shi cikin murya mai dauke da son yin kuka nace.
Don Allah ka barta ta kara min wasu kwanaki kafin ta koma don idan ta tafi zan shiga damuwane sosai ga hjy har yau ban daina kewar ta ba a gidan nan.
Babu mutanene a gidan ko kinmata itama tana da aure ne kamar ki da zan aje matar mutane anan na wata da watannk ai sai a yaba min rashin hankali.
Hakan da naji ya kara sa hankalina tashi sosai ya juya kamar zai tafi yana fadin gobe ma zanso na roke shi arziki yai min ai.
Kinga yanzu ai gidan kine zaki iya zama ke kadai yadda kika girman a lokaci guda da sauri nabi kaina da kallon dan jin abinda ya fada min din.
Yes ya fada tare da sauke min wani irin kallo daga sama na har zuwa kasa yana fadin wa zai ganki a yanzu ya dauka kece zainab din mami a baya mai gudun mutane.
Baki na turo gaba ina fadin niban wani girma ba dan Allah ka barmin ita nidai mu zauna a nan tare na fada kamar zanyi kuka a lokacin.
A dan rikice yake fadin me akai maki kuma yanzu don shagwaba kawai daga magana kina shirin yiwa mutane kuka yanzu kuma.
Idona dago kamar zanyi kuka nace bakai bane kake shirin mayar da sai nayi shiru kuma dan na rasa abinda zan fada mai a lokacin.
Yace a cikin zaro idanun shi waje da akai maki me a hankali na furta zaka maida maizube gida mana.
What me kike fada dama nufin ki a nan zata tabba tare dake ko me kedai yarinyar nan da alama shagwababiyar mace ce ke .
Zama nayi a cikin fushi saman gadon na basa baya yasa kai ya fice daga dakin saina tsunci kaina da sake hawaye lokaci guda.
Shike nan yanzu maizube zata wuce ta barmu ke nan ba zan sake ganin wani dan gida ba sai yadda hali yayu ke nan dani duk da naji bada halimatu za,a tafi ba hakan bai hana hankalina tashiba a lokacin.
Karshe na mike zuwa dakin nata sai dai na kasa fada mata abinda nayi niyar fada har na shigo dakin a lokacin dan bansan yadda zance da ita kada ta tafi ta barmu ba tunda itama tana son zuwa gidan a lokacin duk da daulan da muke cikin sa kuwa.
Washe gari ba karamin mamaki nayi ba abinda ya hadawa maizube na tafiya kowa sai sam barka da ita da anty fadila da take hada mata kayan tafiyan a wuri daya don kuka ya hanani tabuka komai a lokacin.
Nasiha da bn baki nasame su gwargwado wurin boyar Allah nan sai kara jadda min kalman inyi hakkuri da rayuwa wata rana idan Allah ya yarda zan dara kan aurena.
A mota sukai tafiyan don har gida za a kaita ga tsaraba mai tarin yawa an hadata dashi ban tsaya naga tafiyan ta ba don kukan da yazo min a lokacin dole na koma gida na fada saman gado.
Duk dauriyan halimatu itama da taga zasu wuce saidai tayi hawaye a lokacin ranan haka muka wuni sukuku damu sai gidan ya koma muna shiru kamar babu kowa a cikinsa lokacin.
Ban fito ba wunin ranan ina daki rufe sai faman tunanen da nakeyi na gida wayana yai kara na dauka innan muce a layi ta kirani tana min godiyan abinda ya jafar ya aika masu dashi.
Saidana hade wasu hawayen bakin ciki tare da saita muryana nake fadin inna ai hakan yiwa kaine duk da bansan abinda ya aika masu dashi ba a lokacin.
Bayan mun gama waya da inna na sake wani irin kuka mai karfi ni kadai a daki babu wanda zai ban hakkuri dole na kyale naba kaina hakkuri.
Suna zaune da ya mamud a haraban gidan mami zaune suna shan iska yazo mami bata gida ta fita zuwa unguwa yasa shi fitowa haraban gidan ya zauna nan ya mamud ya saneshi suka zauna suna magana.
Ganin yadda yake ta bayani dan uwan yai shiru ya zurfafa a cikin tunane yasa ya mamud din dan kiran sunan shi a cikin kulawa tare da mayar da hankalin shi gare shi.
Jafar meke damun ka na ganka haka yau ko wani abu ya farune yana kallon fuskan shi cikin kulawa yake tambayan shi.
Ya sauke ajiyan zuciya firgigit yana kallon dan uwan nasa ya mamud din ya sake fadin meye matsalan kane jafar a cikin yan dakiku ya mamud din yake jera mai wanan tambayan.
Ido ya lumshe a hankali tare da sauke numfashi mai kama da ajiyan zuciya yana fadin watau mamud ina cikin matsala da damuwa dani kadai na sani.
Sai kuma wani abin mamaki shine a dawowan nan nawa da nayi sai na sake tarar da wani abin mamaki a gidana wanda shine ke kara ban mamaki a yanzu.
Shiru yayi na dan lokaci kafin ya numfasa yana kada kafa a hankali yayin da mamud din ke sauraren shi.
Ido ya bude yanaci gaba da kada kafan shi yace abin mamaki wanda ban taba tunane bashine waina dawo gida na samu wanan yarinyar gaba daya ta sake min lokaci guda.
Guntun tsaki ya mamud din yaja lokaci guda yana fadin yanzu akan wanan har kabi katada hankalin ka haka sai kace wanda yake cikin wani babban matsala.
Shi girman ya mace aiba wani abu bane duba ga irin rayuwan da a yanzu take a cikinsa ko kana nufin a yadda ka dauketa haka zata tabbata a gidan ka koda yaushe.
Kai ya girgiza yana fadin bashine nufina ba mamud sai ka jira kaji karshen zancen mana kafin ka yanke min hukunci kasan abinda ya sakani a damuwa akan hakan.
Ya mamud din yayi kasake yana sauraren dan uwan nasa tare da zuba mashi ido don a yanzu ya tabbatar da duk abinda kanin nasa ke shirin fada mai matsalace babba don ba akan girman nawa dayaga na masa bane lokaci guda.
Huci yayi ga bakinsa sai wani gumi dake tsarso masa a goshin sa tankar wanda ya watsa wa kansa ruwan zafi a lokacin.
Shikan mamud yana ganin yanayin dan uwan nasa yayi saurin fadin wai jafar meke damuwan kane haka ?
Nifa gaba daya duk ka sauya min kamar ba kaiba wanan wani irin damuwane akan zainab din wanda ya susutaka haka har ka tayar da hankalin ka haka wai ?
Mumushin karfin hali yayiwa dan uwan nasa yana fadin mamud kafi kowa sanin bawai na auri yarinyar nan bane don na zauna da ita irin na ma,aurata a yanzu.
Jafar wai wani irin magana kake kokarin fada min a yanzune wai don me ake aure a rayuwa badan mutum ya aje iyali ya haiyayya fa shima ya bar baya kamar yadda iyayyen mu suka barmu.
Yanzu fa jafar kana kokarin rufe bayan talatin da biyar ne a rayuwa don in ban manta ba wacan zuwan naka mami ke fadin kana talatin da biyu a duniya.
Me zaka jira da matar ka Allah ya baka mace ta gari da zaka inya controling dinta yadda kake so agidan ka tun a yanzu kan kanta ya karasa wayewa.
Nida aca tun farko irin matar da mami ta zaba min ke nan ba wanan ba da nake fama da ita a gidana yanzu don ban isa in tsayar da Nuriya wuri daya ta tsaya ba.
Shine abinda nake lurar da mami akan auren ka da yarinyar nan zainab a kullun do ko ita mami Nuriyan bata ragawa ba kasani.
Jafar din ya dukar dakai kamar yana sauraren dan uwan nasa abinda yake fada nan ko wani duniyan tunane ya fada a lokacin.
Can ya dago kai yana kallon dan uwan nasa kafin yace a cikin kyarmar murya kaman mai shirin kuka a lokacin, mamud mafita nake so a yanzu kan wanan auren nawa.
Shiru mamud din yayi don ya rasa inda dan uwan nasa ya dosa da maganan shi yaji jafar din na fadin bana son in rasa wanan yarinyar a yanzu mamud don ina matukar jinta a cikin raina rasa zainab a rayuwana tankar rushewan wani bangaren rayuwanane a yanzu.
Cikin mamaki ya mamud ya dago kanshi yana kallon dan uwan nasa da mamaki don har yanzu ya bai fahinci abinda dan uwan nasa yake nufi ba.
Can ya dago kai yana ftambayan kanin nasa No jafar ka daina fadan haka don Allah ko akwai wani abinda yarinyar nan tayi makane kake son ka boye min dai ?
Kai ya girgiza yana gyara zaman shi tare da lasa saman labben na sama yana mai shafo kanshi a hankali cikin damuwa.
To jafar wanan wani irin wullakanci kake son yiwa yarinyar nan haka koka mai damu mutanen banza a daukemu wawaye wadanda basu san abinda sukeyi ba .
Nace ka fada min meye damuwan ka da ita kana kawo min wasu dalilai marasa tushe a yanzu.
Mamud ba zaka gane bane amma gaskiya nasan bazan iya kula da hakkin yarinyar nan a yanzu ba ko nan gabama.
Innalillahi ya mamud ya fada tare da wani irin zabura daga inda yake zaune din kafin yakai ga cire hulan dake kanshi yana dan fifita dashi a hankali don ya samu iska a jikinshi.
Kafin ya iya buda baki ya furta a sanyayye jafar baka da lafiyane ko wani abinne ya sameka kake boye muna.
Kai jafar ya kada mai alaman a,a ba hakan yake nufi ga maganan shi ba da akwai dai wani zance can kasan zuciyar shi.
Jafar ka tuna koni wani abin ya shigewa duhu daya shafi rayuwana kai nake nema in fadawa ka ban shawara akan hakan don me kai a yanzu ba zaka fada min naka damuwan ba a gabana.
Mamud nasan da hakan shawara kawai nake son ka ban har lokacin da komai zai daidai min a rayuwa na fuskanci matata.
Wani irin ajiyan zuciya ya mamud din ya sauke lokaci guda tare da fadin anya jafar kana da lafiya kuwa ?
Yanzu dai na gama fahintar wanan yarinyar batai maka komai ba don haka koma menene yake damun ka a rayuwa ka lalaba matar ka ta hanyan kyautata mata a rayuwa ta yadda zaku zauna lafiya da ita.
Saidai ka tuna kada ka yarda ka cutar da yarinyan nan da yawa katuna ba a duniyan nan zamu tabbata ba har idan ka cutawa rayuwan wanan boyan Allah Allah zai saka mata ta ida baka zata ba.
Kai jafar din ya sunkuyar a kasa don baida abinda zai fadawa dan uwan nasa a yanzu saidai ina son wanan maganan ya tsaya iyani dakai kafin komai ya daidaita ya mamud din ya fadawa dan uwan nasa.
Da sauri jafar din ya dago kai yana fadin nima hakan nakeso bazan so mami taji wanan zancen ba don zata dauke shi da wani fassara na daban.
Kada kaji komai jafar ka tuna duk abinda ya same ka mekyau ko mara kyau kamar ya shafeni ne koni.
Saidai zan so ka maganan ta makakewa ya mamud din don motan mami daya shigo gidan zuwa parking spece yasa suka mayar da hankalin su gareta tare da mikewa suka nugi wurin motar nata lokaci guda.
Kujeran da nake zaune sama anty fadila ta kala kafin tace dani waini na tambaye ki mana zainab wai tunda maigidan nan ya dawo ya nemi ki a shimfidan shi kuwa ?
Kai na dago da sauri ina kallon ta don ban fahinci inda zancen nata ya dosa ba yasa nace a cikkn mamaki shifida kuma anty ?
Kamar ya shimgidan shi don ban fahinci mekike nufi ba wallahi kayya ta fada cikin daure fuska a gareni.
Tana fadin waike zainab wace irin yarinya ce haka mara wayau da hankali ke an fada maki haka zaman aure yake wai ?
Iyakar mace taci tasha ta saka mai kyau ajikinta ta kwanta shine zaman aure tsakanin mata da miji kawai a rayuwan su.
Idan shi bai neme ki ba bana fada maki hanyar da zaki bi ki ja mijin ki a jikin ki ba zainab kada fa tunanen da nakeyi ya zamo gaskiya a gareku gidan nan.
Me kike tunane anty na tambaya cikin marairaice murya don a zatona wani abin kuma ta hango a tare dani sai naji tace dani barshi kawai hasashen hakan kawai nakeyi akan ku bai zama lalai haka din bane.
Amma dai gaskiya zuciyana ya fara zargin wani abu a gidan nan yanzu, saidai abinda nake so dake shine koda shi bai nemeki ba zainab kiyi hakkuri ki daure ki kai kanki a gare shi mugani .
Da sauri nace ban fahince ki bafa anty ina mai kallon fuskanta don karin bayani a gareni ki dai gwada abinda na fada maki din ta fada tana mikewa daga wurin da take zaune din zuwa kitchen din gidan.
Nan ta barni zaune ina tunanen maganan ta ta yaya zan kai kaina da kaina wurin ya jafar din yadda take nufi din.
Sam hakan ba zai taba yuyuwa ba kenan nidin fitsarariya kenan take nufi ko ms sam hakan ba zai yuyu dani ba wallahi sai dai duk abinda zai faru ya faru na fada a raina ina masifa da ita cikin zuciyana.
Ni a wurins tun daga ranan da nashigo gidan shi har rana mai kama data yau nan taba tunanen wanan abinda take nufi ba a yanzu a tsakanina da yaya jafar din don haka sai maganan nata baiyi tasiri ba a zuciyana ko kadan.
Itama daga wanan ranan bata kara yimin irin wanan maganan ba ta kawo ido kawai ta saka min naci gaba da yan harkokina na yau da kullun duk da bawani abu bane illa zaman falo saiko dan fita haraban gidan da yamma wani lokaci musha iska a waje shine kawai abinda nakeyi a gidan.
Don shi kanshi ya jafar din bayama zama a gida ko garin kwana biyu zakaji baya kasan ya dan fita zuwa wano kasa na kwana biyu kafin ya dawo.
ZAINAB IDRIS mAKAWA
🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
5️⃣4️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
YAR UWA DA FATAN MUN WUNI LAFIYA UBANGIJI YA SADAMU DA ALHERUN SA AMIN,
KADA KI MATA DA LITTAFIN KUDINE KIBAN HAKKINA KO KI BIYA RANAN DA NADAMA BAIDA AMFANI GA BAWA.
DON KIRA ZAKI KIRA WANAN LAYIN KAMAR HAKA 08036959257 KO TURA KUDI BAKIN ZAKI TURA GA WANAN ACCOUNT DIN KAMAR HAKA 2254380105 NAGODE ALLAH YA BADA IKON BIYA AMIN, , ,
Shi hakki gaskiyane yar uwa zaki ban a ranan da nadaman hakan baida amfani a garemu baki daya don haka karatun wanan novel bai zama dole a gareki ba yar uwa ki barshi shine sauki a gareki da zaki gane gaskiyan hakan a gareki da fatan masu imani zasu fahince ni.
Ya mamud yana zaune sai faman tunanen zancen shi da dan uwanshi yake a zuciyan shi tun ranan da sukai wanan maganan ya kasa sukuni a zuciyar shi.
Don ya rasa dalilin dan uwan nasa na fadan wanan maganan haka dole akwai wani dalili nasa da yake boye mai a zuciyar shi.
Don haka ya zama dole yasa ido kan kanin nasa har ya fahinci halinda da dan uwan nasa yake boye mai.
Ta yaya zai iya fahintar hakan bayan ba agari daya ko kasa daya suke rayuwa dashi ba a yanzu koma dai meye zai gane a sannun wanan alkawari yai wa zuciyat shi.
Don haka ya yanke shawaran da zuciyar shi zai fara tunkarana ko zai iya fahintar wani hali daga gurin dan uwan nasa saidai kaico ta yaya zai iya fahintar hakan dadin mace mai mutunci ke nan da ace matarshi mai kaunar yan uwanshine da ita zaiyi amfani har ya gano abinda yake so a wurina din.
Ko yanzun ma bai baci mai ba don zaiyi amfani da daman shi na namiji ya tursasata zuwa gidan don kawai su sada zumunci a garemu ta hakan har dan shakuwa zai shiga tsakanin mu ai.
Da dare suna zaune cikin ikon Allah itace ta dauko zancen jafar din da kanta take cewa dashi yanzu dai kanin ka shi ya fita zancen kowa a garin nan tunda yazo sau daya nasa shi a idona yana ganin bai neman komai a wurin kowa yanzu.
Shi jafar din ya dago yana tambayan ta da mamaki tare da fadin ina mamakin wanan halin naki Nuriya ?
Jafar naga ko yau muna tare dashi a gidan nan shekaran jiyama mun dade dashi