Showing 150001 words to 153000 words out of 191310 words

Chapter 51 - ABU CIKIN DUHU BY MAKAWA By abooks.com.ng.txt

A ina yaji wanan zancen na fada a fili ba tare da nasan zan furtan hakan ba yace wacce abin ya dama ta fada min tunda ke ba zaki kira ki fada min ba asan abinda za a kan wana case din.
Koda na dago kaina gaba daya dakin idanunsu a kaina yake lokacin suna sauraren meke faruwa duk da bajin maganan sukeyi ba a lokacin.
Har ya gama maganan shi na kashe wayan ina kallo da mamaki sa,adatuce ta fara fadin me yaji yayan mu ?
Zancen fadan inna da lantana na dazun yake min fada ban sanardashi ba sai ji yayi ke nan yasa wani ya samai ido a kaina a garin nan kome ?
Da hannu sa,adatu ta nuna min tsakiyan kan halima take zaune a kusa da ita tana lasan miya a kwanon data karasa cin abinci a lokacin.
Itace dazun ta dauki wayan ki da aka kiraki ta fada mai komai yaji inna takai mata magara daga inda take zaune tana fadin waya aike ki mai shegen bakin tsiya da yawan magana.
Inna tambayana yayi ina yayar mu nace tana waje wurin da lantana ke fada dake shine na fada mai komai daya faru inna ta karasa a cikin sanyin murya.
Yanzu me kikayi ke nan yarnan zaki jawa mutane zancen gori da zunden mu a cikin garin da gidan nan kaf yanzu idan wanan zancen yazo kunnen jama,a ai sai a saka mu a baki.
Da kyat na hade wani yawu mai daci da dumi daya taru min a baki tun barin wayan na kasa magana in furta komai sai binsu da kallo da nakeyi dakin duk lokacin da wani yai magana a cikin su.
Bayan dogon nazarin danayi na yan mintina da har ya hana inji karshe fadan inna da halima ashe har dukan ta tayi a wurin ban farga ba.
Ba komai na tuna ba sai abinda ya fada da bakin shi ki huta kowa naki ya huta ta karkashin ki ayi alfahari dake a cikin yan uwan ki wata rana idan kin daure zama dani yadda nake.
Indai hakane na zan gwada in tabbatar da hakan daya fada min din idan har gaskiya yake har cikin ranshi abinda ya fada din a lokacin.
To ya zama dole kodan farin cikin mahaifiyata da yan uwana in amince da tasa bukatan mutukar hakan ba zai sabawa addinina ba ko ya taba min mutuncina .
Duk da nasan yin hakan wani gangancine nake kokarin aikatawa a rayuwana a matsayina na ba yar kowaba a duniyan nan nasa na tarawa kaina babban ganganci a rayuwana.
Haka kawai na dauki waya da sauri na rubuta idan hakan zai zama farin cikin mahaifiyata da yan uwana a shirye nake da inyima biyayya idan hakan bai kauce wa addinin mu ba.
Ina gamawa na sake karantawa batare da nazarin komai ba na tura mai sakon kai tsaye ina mai runtse idanuwana a hankali.
Muryan inna ne ke fadin wani abin yace ta fada mai ne ko me yafaru ya furta hakan.
Ba komai bane inna na bata amsa don hankalinta ya dan kwanta ina kokarin kawar da damuwan dake fuskana a lokacin.
Ba zan so mu jefa ki a cikin wani halin rayuwa harda zaki takura ba saboda wanda daga baya za a dawo abin yazo ya damu mutane kuma.
A,a inna don Allah ki cire damuwa a ranki kan wanan zancen don shi haka rayuwan shi yake da taimakon na kasa dashi ko yaushe.
Allah ya kyauta inna ta fada tare da kaiwa halimatu wani sabon rankwashe akai ta sakr sake wani ihu mai karfi tana fadin inna bansan hakan zai maku zafi bane ai.
A daidai lokacin dana tura mai da sakon yana kokarin fita falon mami don ya dubata a daidai tsakiyan falon sakon yashigo mai a wayan shi.
Wani irin shu,umin murmushi ya sauke a fuskan shi wanda baisan lokacinda ya sakeshi a fili ba don saurin kamawa da tarkon shi danayi a lokaci guda.
Caraf idon shi suka sarke dana mami dake zaune ta hakince tana ba mai aikinta umurni a lokacin.
Ya karaso zuwa saman kujera ya zauna a kusa da ita ba tare data samu mai magana ba don ta lula acikin tunane halin da dan nata ya shiga ba tare da saninta ba.
Idan ko har akan wanan yar matsiyatan abu kamar wasa ga zance naso ya juye ya zama mata babban magana a rayuwa yanzu kuma.
Har yau kan ita mami a daure yake don ta rasa gano me yagano a jikin wanan yar har ya mace haka a cikin sonta .
Yarinyar da ba a bakin komai aka dauke ta ba don yar aikine ba wata mai galihu can ba ko asali har yake neman jefa kanshi ga halaka haka ?
Saidai maganan babban danta mamud ya kara jefata a cikin zargin dan nata a yanzu don tsoron ta Allah kada abinda dan uwan nasa ya fada ya kasance gaskiyane hakan .
Ita dai a iya sanin ta da dan nata tun yana karami komai zayi a duniya zaiyi shine a cikin hikima da fasaha irin na masu hazaka da kwakwalwa.
Sai gashi yanzu ta kasa gaskanta zarginta na canza halayen dan nata ga baki daya ga yadda suka san abinsu da farko.
Fuskan shi a wayan shi yana duba tun bayan zaman shi wurin hankalin shi ya koma kan wayan mami tana magana da mai aikin da bazaice ga fuskanta ba tunda yakai zaune a wurin.
Juyowa mami tayi tana masa duba irin na tuhuma lokaci guda don yadda ta ganshi din yazo ya zauna mata ba wani jin darr din ta ko kadan akan laifin da take ganin ya aikata dole yaji nauyin hakan a lokacin.
Jikin shine ya bashi a lokacin da ana kallon shi yasa ya dago kai dan jin hakan da yaji a jikishi.
Caraf idanuwan shi suka hade dana mami din lokaci guda sai yaji ya dan tsargu da hakan shima don irin kallon da uwar tasu take mai a lokacin don haka ya dukar da kanshi babu shirin haka saboda nauyin ta dayaji.
Jafar may ye matsalakane yane yanzu mami ta fada tana mayar da hankalinta gareshi baki daya don ji amsan da zai bata a lokacin.
Amma sai ta lura kuma har ya mayar da hankalin shi ga wayan ba tare da yasan tanayi ba a wurin da kai nake magana ta fada da da karfi tare da nuna bacin rai a fuskan ta.
Firgigit yayi tare da sake dagowa yana kallonta yana fadi mami ban jiki bane na dauka da wanan kike ai har yanzu ya dan fada a tsarge.
Jafar wai yake damun rayuwan kane a yanzu koka sake shan wani abinne kuma saboda wanan banzan yarinyar daka kwallafa rayuwan ka gareta don jaraba.
Nafa gaji da wanan kwanaye kwanayen da kakein a gidan nan aure dai ne nace bada yawun bakina ba sai kasan yadda zakayi da yar mutane tun yanzu.
Shiru yayi na dan lokaci kafin ya dago kanshi da yake a sunkuye ya dubeta tare da sake wani guntun murmushi a fuskan shi yana fadin.
Mami kina ganin akwai wata wace har zata iya sauya min rayuwana a yadda nake har yaushe na hadu da wanan yarinyar taki da zata sakani wani abinda ba halina ba yanzu.
Ran mami ya baci ainun da abinda ya fada a ranta tace mamud yayi gaskiya al,amarin yaron nan yayi girma ban sanda hakan ba kenan.
Jafar yanzu duk yarda da amana dana baku ashe akwai wani rayuwa da zaka fada wanda ban san dashi ba a tare da kai har ka boye min kanayi. .






ZAINAB IDRIS MAKAWA










🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅




4️⃣5️⃣


ZAINAB IDRIS MAKAWA




FATAN ALHERI GAREKU HAR ABADA YAN UWA MUSULMAI ALLAH YASA MU GAMA DA DUNIYA LAFIYA ALLAHUMA AMIN, , , , , ,




LITTAFIN NAN NA KUDI NA YAR UWA IDAN BAKI BIYA BA KADA KI SHIGA HAKKIN WANI DON ALLAH , , ,




Zan iyacewa gaba dayan mu dakin mun shafa da zancen zuwa wani bako da yafada a jiyan do bamu dauki abinda muhinmanci ba a rayuwan mu.
Sai gashi kawai an kwadawa Abban mu sallama da sassafe ya fita zuwa waje ya dan jima sai gashi ya shigo yana kwalla min kira kamar a kidimance shima yake a lokacin.
Da sauri na dago daga saman raggan katifan da nake kwance na sa,adatu data barmi in kwanta don ina bakuwa a cikin mu.
Abba ina kwana nake kokarin fadi yayi da Abba ya dakatar dani da fadin yar sani wasu mutanene suka zo min da wani zancen yanzu a waje wai maigidan ki ya turosu daga birni zasu duba fili a nan kusa ko wani wuri za aiwasu aiyiuka ko ?
Da sauri na dago kai na dan saci kallon Abba din dake tsaye ya kura min ido don jin karin bayani daga bakina a lokacin.
Kai na girgiza tare da fadin Abba ban san da wanan zancen ba gaskiya na fada dan azauna lafiya kada Abba yayi zargin wani abu innan mu ta hada a lokacin.
Ko wani zargi yazo ya shiga wanda hakan zai iya jawowa innan mu wani matsala a rayuwan ta tunda ba zanso hakan ya faru ba.
Baki da labarin hakan Abba ya fada a cikin mamaki tare da kara kallon yanayin da nake tsaye kafin yace ikon Allah .
Ya juya ya tafi ya barni a wurin runsunne kafin in tsinkayi muryan lantana daga sashinta tana kwalawa Abban mu kira da dan karfi kamar tana bashi umurni.
Abba dake a rude a lokacin bai samu amsa kiran nata ba sai fita da yayi zuwa waje ya nufi gidan dan uwansa a nan cikin unguwan namu.
Hakan baiwa Lantana ba naga ta yafa zani ta bi bayan Abban sai dai ganin bakin datayi a wajen gidan namu wanda wata kila ta firgitane da ganin fuskokin su a lokacin.
Sai gata ta juyo da sauri ta dawo cikin gidan dama da daura gaba kawai ta dan yafa wani ragga a kanta tana rike da danta a hannu jalo jalo, ta fita daga gidan .
Ba kunya ta nufi sashen Asabe don gulma innan mu sai aikinta takeyi ba tare data mayar da hankali ga abinda ke faruwa a gidan ba lokacin.
Bamu san meta fadawa Asabe ba mundai ji Asabe na fadin subbahanallahi da safen nan haka baki a cikj bakin kaya idan dai ba wani yai masa cune ba aka turo akama min shi.
Umma lafiya inna ta fada a daidai lokacin da Asaben ta fito a rude daga wajenta lantana na binta a baya.
Ina fa lafiya yanzun nake jin mugun labari a bakin yar nan wai wasu baki da bakin kaya sunzo sun tasa dan nan a gaba zasu tafi dashi.
Anya kuwa umma haka zancen nan yake yanzu fa ya fita nan naga ya kira yar sani yana tambayan ta wani magana kafin ya fita.
Koma dai menene barin leka wajen in gananwa idona abinda ke faruwa dashi din haka tunda safen nan.
Bayan fitan Asaben itama sai gata taja ta tsaya don irin mutanen da suke wajen gasu Abban mu a gefe daya tare da wasu yan unguwa suna magana a tsanake.
Haka asaben ta fita tana ratsa mutane a dan gigice tana tambayan abinda ke faruwa ba wanda ya koma ta kanta karshe ma suka kwasa suka shiga mota zuwa gidan maigari.
Nan suka bar asabe tare da wasu yan tsirarun mutane a wurin yan gulman da basu gane komai ba ala dole ko sai sun gano hakan suji kwam.
Sai kusan sha dayan rana mudai tun muna saka rai da dawowa Abba har muka koma daki don mu karya masu wanka kuma suka shiga yin wanka don ka,idar innan mu ce tasa ruwan wanka kowa yayi wanka kafin rana ya dago.
A wanan lokacin ne Abban mu ya dawo gidan ko yanzu shigowan ujula yayi yana kokarin fita daga gidan Asabe ta dakatar dashi.
Abban ya dawo tare da dan mata bayani a takaice tare da fada mata cewa umma ba komai bane sai alheri haihuwace ke kokarin nuna dadin ta a gidan nan yau.
Do yaron nan mijin Abu ne ya turo a sai fili a kusa damu nan za, ai masa wani aiki a wurin wanda bansan me za,a gina maiba amma dai aiko maiye dai karuwa mune ai.
Hakane inji asabe ta fada tana gyada kai alaman gamsuwa da maganan shi tana fadi ikon Allah .
Akan ya mace ne wanan baiwan ya sauka a gidan nan haka duniya kabar mutum a inda ka gansa don baka san baiwan da Allah yai mar ba.
Ranan dai mutanen basu bar wurin ba saida suka tabbatar da an fara aiki yadda suke so sukayiwa kowa sallama suka bar garin da yamma lis.
Injiniyan sa zaiyi aiki da ma,aikatan shi aka bari bayan sun samu masauki inda zasu zauna ko washe gari haka suka tashi da aiki wanda hakan ya jawowa mutanen unguwar mu ciniki a wurin su da safen .
A kwana biyu da fara aikin kwantsan saiga shi a garin yazo dagashi sai wani abokinshi saikuma security dinshi da yazo dasu inda kallo ya dawo garesu.
Zatinshi, izzashi da wayewa da kamala uwa uba ilimi da isa ya kara hakashi idon duk wanda ya ganshi a lokacin .
Duk wanda aka fadawa wai shine mijina bai yarda don sam ansan shi din ya wuce ajin aurena saidai idan an masa dole a kaina sai ya aureni da wata manufa dai.
Zancen zuwan shi yabi gari lokaci daya duk wanda yasan da hakan saida ya tofa albarkacin bakin shi kan zancen auren kowa da irin abinda yake fada kinsan kauye da samun magana.
A ranan bayan ya gama ganawa da iyayyena tare da zaga aikin ginan da akeyi babu kama hannun yaro don kudi na shan kashi sosai ga aiki ga kayan aiki sai shigo dashi ake tun ranan da aka fara aikin.
Ganin zuwa matar malam illiya yasani shan jinin jikina sosai don abinda malam din ya fada min ranan da naje gidan shi din.
Ba wani bata lokaci muka hada tafiya inda halima ta nace saita bini nan dai aka kwasa sai karshe aka yarda mu tafi tare idan matar malam zata dawo su dawo tare.
Ba takura ga zaman mu don motar mu daya ni matar malam da kanwata motar daya sai scurity din dake gaban motar a zaune tare damu.
Munbar kauye da zance a bayan mu tafiyan dan lokaci ya kaimu kaduna na dauka ba zamu tafi gidan mami ba kamar zuwan mu.
Sai gashi mun sauka a gidan inda muka samu Nazifa da anty salma kawai a gidan Rufaida bata nan sunce bata faye zama gidan ba yanzu sosai.
Sunyi matukar mamakin ganin mu a lokacin saidai sa yake a tare muke dashi daga mu harshi babu fuskan yun wani zance a lokacin .
Na dauka zama kwana kaduna sai baya munyi sallah munci abincine anty salma ta shigo tana fadin wai ya J yace mu fito zamu tafi.
Ba a cikin wani sakewa muke ba dukkan mu har anty salman da take min kallon mamaki a fakaice ta kasa ko dan sakewa damu Nazifa kan tun ganin farko da mukai mata a falon ban sake sakata a idona ba har wanan lokacin.
Rufaida dasu Ruby sun zo gidan gulma sun samu mun wuce don ko mami dake Abuja har labarin zuwan mu gidan ya isar mata a lokacin.
Sai ashar ta kundumawa dan nata damu tare da fadin a fada mai maza mu bar mata gida kafin ranshi ya kaiga baci.
Ba wanda zai iya fada mai sakon har muka bar gidan don dama da abinsa zaiyi a kadunan yasa muka tsaya a nan.
Karfe takwas na dare muna a cikin wani rantsetsen gida da ban san ko a ina wanan gidan yake ba haka mudai namu idone kawai.
Alhamdullahi komai a kwai a gidan babu ne kawai babu ga gidan da girma duk da darene bai hana mu gane hakan ba.
Irin su cultizen su club ko Iliminaties, dai da sauran su ai zubur mami ta dago tana fadin what, what, mami ta kara fada tana gyara zama jalal yace yes of course mami don yanzu ai kinsan duniya saida wanan kuma muddin sunan har zaiyi fice ka kaiga wani matsayi nan gaba.
Kirji ta dafa tare da fadin innalilllahi wa inna,alaihim rajin sai ra hada da mikewa tsaye a daidai lokacin kuma shi ya mamud ya shigo falon tare sa jamal.
Jalal ke fadin mami nifa bawai nace hakan bane naga kin daga hankalin ki sosai kwatance kawai nayi maki ai da hakan ya fadi a cikin damuwa.
Mami kan ta shiga wani hali a lokacin don bata masan me take fadi a

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login