Showing 105001 words to 108000 words out of 191310 words
Chapter 36 - ABU CIKIN DUHU BY MAKAWA By abooks.com.ng.txt
ya duba mai aiki sukai kicibis da Nazifa ta fito falin sannu da zuwa ya J ta fada cikin nuna kulawa ba taee daya amsa ba yace ke dauko tsintsiya ki share part din nan.
Wa ni ya jafar ta fada tana wani turo baki gaba bake ba wancan zaki bace min kiyi abinda nace tunkan ranki ya baci wurin nan.
Ta juya tana gunguni zuwa kitchen yana tsaye har ta fito abinka da wanda bai saba aiki ba ji rakeyi kamar ta kurma hannu akai tayi ihu a lokacin.
Wajen gidan ya koma ya tsaya harta karasa can ya dawo ya samu wai ta gama kamar bata taba komai ba a dakin dakin na nan yadda yake.
Fita yayi da sauri yana kiran sunan ta da dan karfi ta fito ya balla mata harara yace common shara ma ba zaki iya ba.
Yayani fa bana shara wanan ma ai nayi kokarin yin sa yanzu kawai ba a sa yan aiki irin su , , ,
Ji kake fauuu ya wanke mata fuskan ta da mari da sauri ta kurma wani uban ihu daya fito da sauran daga daki.
Ta durkushe a wurin tare da dafe kuncinta da dukka hanayen ta biyu ta durkushe a wurin.
Saiga salma da Rufaida sun fito daga dakin da sauri suna ganin shi suka rikice sai sannu da zuwa suke mashi.
Kai ku fito ku gyara ko ina na gidan nan yanzu kafin indawo ko kuma ku samu naku hukuncin zaku zauna kubar gida haka a kazance kamar babu mutane a gidan.
Ya J mai sharan ne bata zo ba wai danta baida lafiya ku ba mata bane aikin me kukeyi a gidan ku ?
Ya j ba aikin mu bane shara fa yace oho relly ku din ba mata bane oya ban son in dawo gidan nan in sameshi a haka ya juya fita ya barsu nan tsaye nazifa na dafe da kumatunta tana hawaye.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
3️⃣1️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
ASSALAMU ALAIKUM WARAHAMATULLAH YAR UWA BARKAN MU DA WARHAKA DA FATAN ALHERI GAREMU BAKI DAYA ALLAHUMA AMIN.
LITTAFIN NAN NAN NA KUDINE DON ALLAH KADA KI KARANTA IDAN BAKI BIYA BA YAR UWA DON KAUCEWA SHIGA HAKKIN WANI.
DON TURA KUDINSA 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN WAYA 08036959257 UBANGIJI ALLAH YA HORE ABIN SAYA ALLAHUMA AMIN, , , , , ,
Daga inda nake kwance nake tajin dan kida na tashi a dakin sai dai dayake ba waya gareni ba yasa ban damu da in dago don ganin inda wayan ke kuka don a zatona ko wanine zai shigo dakin wurin hjy.
Don yanzu dakin bai rasa masu shigowa lokaci lokaci mussanman jikokin hjyn diyan mami ko wasu baki.
Haka yasa ko yaushe nake cikin gyaran dakin don kada a samu dakin yadda bai dace ba.
Wayan ne ya kara kira daga inda nake kwance rub da ciki don wanan dabi,a nane idan ina karatu in kwanta hakan duk da ance hakan baida kyau a musulunce.
Makan da hjy takai min a baya yasani dagowa a firgice tare da juyowa lokaci guda ina mamakin hakan take fadin sabon shiga wayan taki ce ke kida haka yana damun mu.
Kallon hjy nayi tace jeki ki dauka kada ya katse hjy kila ba kira bane wata kila alam ne wa nake dashi da zai kirani ni ?
Waya saya maki wayan idan bashi zai kira wanan lokacin ba ta fada a dan shagwabe da ban ma san nayi ba don ance ido wa ka raina yace wanda nake gani kullun idan ba hjyn ba wa zan tsaya yiwa wani shagwaba haka a gidan sai dai idan su mama kande da lami dan dama dama.
Jeki mana tun dazin waya na kara baki daga ba ta dan fada a cikin yanayin bani umurni don ba wasa a idon ta ko kadan a lokacin.
Dauka nayi sai kuma na tsaya ina kallon wayan don ban san yadda zan danata ba in amsa kiran.
Can dai na tuna da yadda anty Aisha ke daukan nata na daga tare da kara wayan a kunne na shiru babu sallama babu hello.
Yasa na sauke wayan ina kallon screen din wayan da sai lokacin ma na fara ganin yanayin ta na mayar da sauri na sake karawa a kunne na.
Jin har lokacin ba magana yasa na mayar da wayan kasa inda take canji na kara jona ta na juyo zan koma inda nake kwancene wayan ya kara daukan kara.
Na kara dauka na danna dauka a cikin siririyar murya nayi sallama badon naso ba sai naji sauke ajiyan zuciyar shi a hankali tare da fadin.
Barka da dare kuna lafiya saida na lumshe idona don jin muryan shi tar a kunne na da kuma abinda ya fada.
Da kyar na iya budan baki na amsa da lafiya kawai ban kara furta komai ba shima a nasa bangaren shiru yayi bai kara magana ba sai can yake fadin .
Wayar tayi maki ke nan ko ya fada don yarasa me zai fada, don jin muryana yasa shi jin kamar numfashin shi zai dauke a lokacin.
Dan murmushi nayi wanda bansan sautin shi zai fita waje ba har ya iya jina a cikin wayan.
Ashe kina murmushi da alama dai kina son waya a rayuwan ki tunda yau har waya ya sakaki yi min murmushi duk da bangani a fili ba nasan hakan yai maki dadi sosai.
Yaya sai anjima na fada don jin abinda yake fadi wanda kunnena ba zai jure daukan sautin muryan shi don yanayin dana soma ji a tare dani lokacin.
Ke ina wasa dakene zan kira kice zaki kashe min waya kina jina ya karasa magana dashi.
Kayi hakkuri yaya na fada a dan maraice kin kyautawa kanki da kika zamo mai saurin bada hakkuri don ni mutum ne da bai son raini ko a cikin abokaina.
Gabana ne ya fadi don jin abindaya fada tare da tambayan kaina yanzu wani raini nayi mai daga fadin sai anjima kawai.
Hjy fa tana ina naji yana fada donni har na shiga tunane a raina na manta da waya a hannu na lokacin.
Gata kusa dani na fada yace a bata wayan da sauri na mikawa hjy wayan ta karba naji sun fara gaisawa dashi.
Ka isa lafiya ya ka samesu nan yace hjy banje gidan kowa ba ina gida kwance tundana dawo.
Tace badai kana lafiya ba ko kadai kula da kanka ka dinga cin abinci don nasan halin ka jafari baka son cin abinci akan lokaci.
Allah sarki hjy zan kula kinsan ba komai nake ci ba hakana nagode da kulawan ki garemu kema ki kula da kanki ki dinga kashe kudin ki ba sai mami ta saya maki ba .
Idan na kashe zaka ban wasune ta fada a cikin zolaya kada ki damu hjy idan kudine baki da matsala su ko yanzu idan kina so zan turo maki.
A,a Allah dai ya karawa arziki albarka ta fada hjy wanan adduan muke bukata a wurin ku ko yaushe.
Addua kan muna yi ko yaushe ana kanyin tane Allah ya tsare ya kare ya kawo sauki a rayuwa.
Ya saki ajiyan zuciya tare da fadin shiyasa muma muke addua Allah ya barmuna ke a tare damu hjy don ki kula damu.
Kaida ka kara hakkuri kayiwa uwar ka biyayya a tafi a yadda take so don wuyan sha,ani kega uwar taku rayuwan turai ya bata ku ga baki daya yanzu.
Hjy turai basu da wanan halin ni kaina ina mamakin canzawan mami yanzu tun daeowan ta kasan nan komai nata ya canza a yanzu kamar ba mamin mu ba.
Ku daiyi hakkuri hjy nasan mami zata sauko da kanta idan ta gane gaskiya don mamud ma complain din da yake min ke nan ya rasa gane kan mami yanzu.
Kuci gaba da mata biyayya dukkan ku wataran zata gane gaskiya ta gyara da kanta Allah yace aiwa iyayye biyayya koda basu raye wasu nasu suna nan.
A hankali yace Allah ya bamu ikomn yi hjy nagode sukai sallama ya kashe wayan shi don yasan ba zan kara dauka ba.
Wayan ta miko min na karba take fadin kinga yanzu ai kwaji sauki ki daina wanan guje gujen da kike masa kamar kinga dodo.
Murmushi mai kama da yake na sake kasan fuskana tare da daukan takarduna na hada a jakkan makarantana.
Dan hira muka taba kafin barci ya fara daukana itakan sai dare da na falko fitsari na samu tana ibadan ta a zaune.
Idan na samu tana hakan watarana nakan yo alwalan inyi raka, a biyu in koma in kwanta idan an kira sallah zata tayar dani nayi sallah asuba zaman da banyi da kakana Asabe a gidan mu shi nakeyi da wanan tsohuwar don yadda ta daukeni take kuma sake min fuskanta tankar itace ta haifi mahaifana a cikin ta.
Barci ne ya daukeni ban sani ba bayan na idar da sallah sama sama naji muryan mami a dakin mu suna magana da hjy.
Bayan sun gaisane take fadin hjy kinji shirmen da yaron nan yaje yayi a kaduna wai jafar nason mu gama lafiya dashi kuwa hjy ?
Me kuma yayi kibi a sannu koma meye don yana da hankali ko me zai aiwatar.
Ina hankalin yake nan hjy yanzu aka kirani ake fada min wai yaje ya daki yaran nan har Nazifa da Rufaida sun kwana a gidajen su.
Yanzun kanwar daddy su ta kirani tana fada kan abinda yaiwa yar nata assha ita hjy ta fada tun kan mami ta karasa magana.
Wanan yar bata da tunane don jafari ya duki yar ta har zata kira ki ta fada maki ina wanta ne yana da ikon hukuntata idan tayi mai ba daidai ba.
Hjy meya kawo duka yanzu kamar jafar zai tsaya yana duka mace ina yaran nan yanzu dai sun wuce duka sai tsawatawa.
Ki dai yi bincike abinda ya hadasu fada aji haka kawai tunda ba hauka yayi ba, haka kawai ba zai farmasu da duka ba ai.
Wani abin dai sukai mai har hakan yakai ga faru a tsakanin su don haka ki binkita karki hau danki da mumunan zato har ki yanke hukuncin da bai dace ba a kanshi.
Hjy koma meye ba zaiyi hakkuri dasu wanan kawai wani sallon jan magana ne a guna yanzu kinji ita Binta tana fadin wai akan wanan yarinyar zeey ce ya daki yarta.
Wace yar tana nan ina suka ganta wai meyasa mutane basa son a zauna lafiya ne.
Kawai su dorawa yar nan bakin jini don kawai suna daukanta mara gata shi rashin gata rashin ubane halan ?
Yar nan fa ba shegiya bace don da ubanta don Allah ya nufa zataci daga tsatson su duk wani maganan bantanci sai ya kare akanta yanzu ?
Don kawai suna takana da iskanci irin tasu da basu san darajan dan Adam ba ina koke haka kikai ta fama da korafin su a lokacin saida Allah yai maki tsaye a kansu.
Hjy shine dalilina kan yaron don nasan ko bai samu matsala da kowa ba zai samu da yan uwan uban shi kan abinda yake son yi a yanzu.
Don daga sama,ila har ita binta din duk suna da bukatan ya auri diyan su kinga kuma ba abinda zai yuyu bane gareni.
Shiyasa nafi son ya fita can nesa yaje yai auren shi zaifi mun kwanciyan hankali tunda dai ba ganin su zasuyi ba idan yai auren sai dai idan yazo da tashi matar irin haka.
Duk ina kwance na lafe ina jin duk abinda ke wakana a tsakanin su zancen sukaci gaba dayi inda yanzu zancen ya koma akan hiran auren mami da mijinta .
Mikewa nayi daga inda nake kwance na sauko a hankali tare da kaiwa kasa na gaida mami da kwana ban tsaya dakin ba nafita zuwa dakin mami din na fara gyara mata.
Ga kudi nan a watse ko ina saman gadon kamar lissafin su take ta fita daga dakin da wayoyin ta aje saman gadon.
Ni dai na hadasu wuri daya na daga filo na saka karshin filon na gyara gado ta hanyar cire zanin gadon na shimfida wani don wanan kwanan shi biyu da shimfidawa ke nan.
Har na gama da dakin nata, tana dakin mu da hjy suna hira don haka na nufi kitchen kai tsaye don mu gaisa dasu mama kande da kwana.
Ina kitchen din suka hada abincin hjy na dauko na nufo dakin mu dashi inda na samu mami din tafice daga dakin.
Ina kika shiga ne tun dazun nake zancen ki a araina wankin tufafina da suka dan hadu nake son a kaiwa mai wankin can ya wanke min.
Ina kitchen wurin su mama kande kina aikin ko kindaiji abinda sahibin naki ya fada ki daina aiki a gidan nan gashi uwar taku yanzu nake fada mata abinda yace tace bashi ya dauko mata ke ba ai.
Kinsan iyami hutsuwace idan ba ita taso abu ba balle wanan da kamar jira takeyi ya zanta akai.
Hjy nidai don Allah ai masa magana ya daina kulani kada mami tazo tana ganin laifina a banza .
Yar nan aikin san yadda so yake ke idan kika fara kaunarsa ai duk abinda uwar taku zata fada ba zai taba damun ki ba gidan nan.
Hjy ni na fada da mamaki ni ina zan kai dangaye kamar yaya a kauyen mu ai sai suce yawon barikin na fita da gaske.
Kai yaro man kaza ke yanzu wazai samu tsalelen saurayi kamar jafari nidai hjy don Allah ki masa magana ya daina kulani kada su anty Rufaida su sakani gaba kuma ina zaune kalau.
A kul, akul na sake jin kiyi wanan zancen wata rufaibaida can dagasu har iyayyen nasu suma ba so suke ayi dasu ba.
Nasan wanan ba yanzu ba ina kula dasu a gidan nan duk take taken su ina karantasu a idona kece din dai da suka raina Allah ya makalawa son ki a ranshi.
Dukda suna ganin ki ba a bakin komai ba a gidan nan ba sai gashi Allah yana shirin daukakaki a cikin su shine suke neman hanyar da zasu bataki ga kowa yanzu.
Ni jafarin yayi min daidai daya gargadasu ya kora min yan banzan yaran nan suka bar gidan nan yara babu abinda suka iya sai munufi da iya shege a tsakanin manya.
To ba suna son shi ba su yaso su mana tunda sune yan uwan shi masu kudi nikan ya rabu dani hjy.
Yar nan kina data ido kuwa jafarin ne bakya so ko Allah zakiwa butulci da baiwan da yai maki na samun shi ta fada ranta a bace.
Bakina bude da zumar bata hakkuri don na fahinci jikan nata baya laifi a wurin ta amma sai ta dakatar dani tana cewa.
Ke matsoraciya ce ko mai zurfin ciki ke ko irin kishin nan ma bakya nunawa akan mai son ki sai faman gudun shi kike kamar kinga dodo.
Bance komai ba donni maganan tsohuwar ya fara wuce sanina don ni a ganina ko anty Aisha banjin tana maganan samari balle har aje ga magana na a gidan meyasa wanan bawan Allah keson ya takurawa rauwana hakane yanzu gashi ya saka tsohuwar nan ta hau zancen ta zauna a kai ba wanda ya isa ya furta wani kalami kan zancen shi.
Ganin yadda take magana rai bace bil,hakki yasa muryana rawa nace hjy don Allah kiyi hakkuri ban san ranki zai baci haka ba don na fadi ra,ayina.
Tsaki taja tana kawar dakai daga gefen tare da fadin ana baki kina roko idan uwar taku taji kina fadan haka ta samu inda zata fito masa ke nan ai akan cewa ya rabu mata dake tunda bakyason shi.
Fita nayi daga dakin tare da kayan wankin ta dana kwasa ban yarda na dawo dakin ba na zauna wurin su kande ko abinci ranan ban samu ciba don dan damuwan dana shiga najin wai akaina wani abu na shirin faruwa a family su kuma yanzu.
Ina jin su kande da lami suna hiran su wanda yawanci akan aiki dake masu yawa na yaran mamine wanan yace wanan yakeso a dafa mai wanan kuma yace baya son wanan dole sai sun kara dafawa.
Ga Nuriya matar yaya mamud da nata azzalzalan don ita din girkin daban suke mata dole don tace ba zataci na yawa ba da ake dafawa a gidan duk da haduwan shi ga dadi.
Ban tsika a zancen su ba kuma din sun san ba zan fadawa kowa wanan zancen ba a gidan.
Lamice ta kalloni tana fadin yau kan ke kamar wani abuna damun