Showing 165001 words to 168000 words out of 191310 words
Chapter 56 - ABU CIKIN DUHU BY MAKAWA By abooks.com.ng.txt
take matsa min da nayi wanan shigar tun ina kunyan hakan har nazo na daina ina fita hakan kamar yadda ta umurceni dayi din.
Ruwane ya gwauce kamar da bakin kwarya muna zaune muna hiran mu bamu daga a falon ba don sanin lokacin sallah baiyi ba a lokacin.
Duk da ruwane mai karfi da akeyi hakan bai hananu mu jin dirin motoci da horn a gaban gidan ba lokaci guda saidai hakan bai wani damun ba don ji muke kamar hadirin ne haka.
Don haka hankalin mu kwance muke hiran mu batare da kawo komai a ran mu ba lokacin sai ji mukayi kawai an turo kofan falon da muke zaton a rufe yake.
Don bamu barin kofan kasafai a bude hakana a namu zaton yana rufe a lokacin ashe a bude yake jin aturo kofan yasa hankalin mu ya koma a kofan lokaci guda.
Shine ya shigo falon ba tare daya dago kai yasan damu a falon ba yana dan kakabe ruwan daya dan taba mai jiki daga waje wajen shigowa gidan.
Gaba dayab mu a cikin mamaki muke kallon kofan don jin anturo da mamaki karara a fuskokin mu sai ganin shi mukayi tsaye yana kakaban ruwa a jikin shi.
Kafin ya dago kai ya sauke idon shi garemu idanuwan shi masu haske kamar kwan lantarki ya kura min ido da maki a fuskan nasa.
Tsaban rudewa da fargaba yasani mikewa lokaci guda don rabona da ganinsa yanzu kusan shekara daya ke nan ake batun rufewa tun bayan daya dauko mu a kauye tare dasu maizube da halimatu ya tafi sai wanan karon dana gansa.
Idanu ya kara watso min sun kara fari da girma gasu dal dasu tankar hasken lantarki saboda tsaban jindadin da yake samu.
Ga wani girma da kwarjini daya kara baiyana mai alaman jin dadi ya zaunu mai a yanzu fiye da lokacin daya barmu a baya.
Masangalin kujera na dafa a cikin kyarman murya nake fadin sannu da zuwa yaya .
Sai lokacin ya dan yi kamar wanda yai shock a cikin basarwa da dakewa ya amsa da uhmmm yana karasowa cikin falon.
A daidai lokacin ne kuma aka sake turo kofan saiga wanan yaron nasa ya shigo dauke da jakkar kayan shi yar karama.
Shima tsayawa yayi yana kare muna kallo cike da fara,a anty fadila take masu sannu da zuwa da signal ta nuna min in karbi kayan a hannun yaron nasa da yake rike dashi a bayan shi.
Na karasa cikin takon da bansan inayin shi ba zuwa inda suke tsaye din na dan gwauta ya jafar din zuwa amsan yar jakkar kayan.
Sai cewa yayi cikkn wani murya mai shrge dana mata barshi kawai zan karasa dashi ciki ya fada yana kokarin wuce inda nake tsaye.
Da sauri anty fadila ta amsa da fadin is her duty give it to her ya dago yana kallon ta a cikin mamaki kamar ba zai bayar ba sai kuma ya mika min jakkar.
Kamar kullum wanan yaudararen idon nasa ya watso min wanda na riga dana saba ganin wanan kallon nasa tun ina a gidan mami zaune idan sun shigo tare da yayan.
Zama sukayi a falon yana gaiswa da maizube da halima datake murnan ganin yaya din sai faman washe baki da takeyi don ganin sa.
Bankai kayan dakin ba don a rufe yake tun lokacin kitchen na nufa a can na samu anty fadila tana hada masu abin sha tana ganina tace good oya dauki maza kikai masu wanan.
Na dauko har lokaci yana zaune suna hira da maizube sama sama na dire masu ruwan da drinks a gaba shi kamar yadda ta koyar dani din inyi idan ya shigo.
Wanan yaushe ta koma haka yaron nasa ya fada a daidai lokacin da nake mikewa daga dukawan danayi ina aje ruwan cikin kashe murya.
A takaice na amsa masa da kwanaki wanda ni kaina bansan zanba da amsar hakana ba alokacin fito min tayi a bazata.
Kaishi kawai ya girgiza cikin wayayencewa gami da basar da disgashin da nayiba take.
Na juya zan bar wurin naji ya din na fadin dawo ki zuba muna yanauin maganan sa kamar a kasalace yake a lokacin.
Na dawo badon naso ba na fara zuba masu a hankali abin mamaki sai bayan na zubane wanan yaron ya mike ba tare daya dauki nasa yasha ba yana fadin.
Zai fita yaga sauran wa yanda suke tare dasu a waje ba tare da ya jafar din ya bashi amsa ba yaba zaune ya dafe kanshi da hannun shi daya har ta fice falon bai masa magana ba.
Dauka nayi nikan na mika mai a cikin ladabi da girmamawa sai naji yana fadin thank you bayan ya karba daga hannuna.
Banyi mamakin jin kalman daga bakin shi ba don godiya ga bature ba wani abu bane wanan na saba da godiyan su tun a gidan mami.
Saidai naji dadin hakan a raina don godiya wata kalmace mai nuna yabawa ga mutum ga wanda akaiwa hidima.
Yana gama sha ya mike tsaye ya nufi hanyar dakin da yake shine nasa din a gidan wanda har lokacin dakin yake rufe.
Ina ganin ya shige na sauke wani irin ajiyan zuciya lokaci guda kamar wace ta tsira daga wani abun tsoro.
Maizube ne ta fara mikewa tana fadin wanan yaron yai muna bazata shigowa haka babu sanarwa a garemu Allah yasa dai abincin da akayi zai gamshe shi.
Anty fadila tana kitchen din zata bada umurnin abinda za a girka masu yanzu na fada ina kokatin zama.
Ke kuma ina zaki zauna nan miji yana gari ai tashi zakiyi kije inda yake ko da wani taimako da zaki masa yanzu.
Wani iri naji a raina idan naje mezan masani don dai kawai in basar da zancen ta sai kawai na mike kamar zan nufi dakin sai bayan ta shige dakinta na dawo na shige nawa ba tare da nayi abinda tace min din ba.
Ban dade da shiga daki ba wayana ya dauki kara da mamaki na isa inda wayan yake na dauka anty fadilace ke fadin kina inane ?
Daki na bata amsa a takaice tace ki sameni a kitchen kai tsaye ta kashe wayan haka yasa na mike tsaye nafito zuwa kitchen din.
Nan na samu sunata aiki a kitchen din tare da banufar dake dafa muna abuncin a gidan tana min bayani muna aikin har muka karasa daidai lokacin da aka shiga sallah magariba don dama yanayin hadarin ne yasa garin duhu kamar magariba yayi a lokacin.
Bayan mun gama jera komai nakaiwa su maizube nasu a dakita na koma dakina don gabatar da sallah na.
Wanka na farayi kafin nayo alwala nafito na tayar da sallah din ban daga daga gurun ba sai danayi duka sallalolina gaba daya nayi kafin in tashi in gyara jikina.
A cikin wani dogon riga har kasa mai laushi sai kaina dana gyara tare da daura dan kwalin rigan ta hanyar sako bellen daurin gefena duka biyu wanda yin hakan yabada wani ma,ana a gareni.
Fitowa nayi falon ban samu kowa a falon ba sai kayan abincin da aka jera masu saman table masu kyau na zamani da daukan ido wanan duk aikin anty fadilace.
Ina shirin komawa bayan na karewa falo kallo da irin kamshin dake tashi a cikin sa saboda gyara na musaman daya samu dan shiga dakin danayi don yin sallah.
Anty fadilace ta fito take fadin yyauwa dama yanzu nake shirin shiga surin ki na kiraki ki samu mijin ki a daki ki fada mai abinci na dinning ki kula da wanan matukar yana gari a tare dake wanan yana a cikkn aikkn ki daga yau.
Dan jin nayi ina tunane a raina na yadda zan iya tunkaran shi da wanan zancen kamar ta shiga zuciyana taga abinda nake tunane a lokacin.
Take fadin kwaliyan ki yayi kyau matuka yanzune kika nuna min kina amfani da shawaran da nake baki kullun.
Don haka sauran aiki yana gareki kije ki sameshi a dakin shi tunkan ya fito hakan zai kara kawo kusanci a gareku ko yaushe.
Idan kuma ya fito ki tabbatar da kin zauna sai idan ya gama ci kina zaune a gurin wanan ma wani isimine na mata da mata da yawa suke sakaci dashi tana gama fadi ta juya don barin wurin
A hankali na ja kafana zuwa dakin bakina yana cike da addua na tun kari dakin nasa yayin da gabana sai faduwa yake min din tsoro da fargaba abinda yin hakan zai iya jawo min idan na kai kaina gareshi din.
A kofa na tsaya na da runtse idanuwana tare da tattaro karfi da kuzari azuciyana na kai hannu ina kwankwasa kofan.
Kusan sau uku ina kwankwasa kofan kafin naji ana kokari bude kofan daga ciki hakan ya dan sani ja baya a hankali tare da tsoron hakan a raina.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
5️⃣1️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
YAR UWA DON GIRMAN ALLAH YAR UWA KADA KI KARANTA IDAN BAKI BIYA BA, DARI UKU NE KUDINSA DON NEMAN KARIN BAYANI KI KIRA WANAN LAYIN 08036959257, , , , ,
Shiru babu wanda ya bude kofan hakan yasa na tura kofan a hankali na shiga dakin csn na hango shi zaune saman sallay yana azzakar da counter a hannun shi.
Jin alama an shigo mai dakin yasa shi dago kai a hankali daga inda yake zaune ya hada gwiwan shi biyu wuri daya ya hade da hannayen shi saman kafan da counter din shi yana danawa a hankali.
Idon shi ya sauke a kaina kafin nayi karfin halin karasawa wurin shi a hankali ina fadin bansan kana ibada bane dama nazo fadama abinci na saman dining an shirya ma.
Kai ya gyada min a kasalance ba tare da yai min magana ba ganin haka yasa na juya da sauri don barin dakin don gabana dake fadawa ban ko tsaya yiwa dakin kallon tsab ba don ganin irin alatun dake cikin dakin nasa.
Duk da ganin namu dakin da muke ciki ya kai iyakar haduwa wurin tsaruwa sai naga wanan din nasa kamar shagone na shiga.
Ke jimana naji muryan shi a bayana yana fada a hankali naje na tsaya ba tare dana jiyo na fuskance shi ba don yadda yai maganan.
Da ban nan mami tazo gidan nan naji tambayan yazo min a bazata don haka na basa amsan tambayan da fadin ya mamud daine yakanzo dubamu sai ko ya jamal da yazo sau biyu .
Tsaki yaja yana mikewa tare da fadin ba wanan na tambaye ki ba ai nasan da mamud yana zuwa dubaku ai.
Gabana yayi dam sai nayi shiru don yadda ya katseni a cikin fada lokaci guda abin ya ban mamaki matuka.
Don haka tun bai fadi komai ba kuma naja kafana na bar dakin don gudun wani fadan kuma.
A tsakiyan falo na hango Tajjuddeen tsaye kamar yana nazarin wani abu saidai yana ganina ya nufo inda nake da sauri yana fadin.
Me kika shiga yi dakin ogo a yanzu wa ya baki daman shiga masa daki a wanan lokacin?
Idanu na zaro a tsorace don don jin irin tambayan daya jefo min a bazata wanda imani da tsoro tambayan ya mamayeni lokaci daya.
A cikin karfin hali na bude baki nace waya aikoka tambayana wanan dalilin yanzu.
Wani irin kallon tsana ya watso min kafin yace dani babu saidai hakan kada ya baki daman kusanta kanki gareshi kuma.
Kaina na dukar kasa nayi dan shiru kafin in dago a fusace ince dashi matsayin ka da kimar ka baikai ka yi man wanan tambayan ba a yanzu .
Kafin in bude baki in bashi amsa ya nunani da yatsa a fusace shima yana fadin ke ni zaki rainawa hankali ashe baki da kunya da nake ganin ki haka ?
Gaskiya jackson ya illanta maki rayuwa daya tsaya ya mayar dake mace haka mara moriya gashi kina neman kai kanki ida matsayin ki bai kai ba.
Idanun sa sun kada sunyi jawur zuwa tsatsan bacin rai dani haka nima domin maganganun shi sun daga min hankali sun tsoratani lokaci guda.
Na runtse idanuna ina jin kuna da radadi a zuciyana kafin in bude udanun nawa na sauke su a kanshi cikin tsana ina fadin .
Dakata wai malam ka daina yaba min kalamai kamar wani ya aikoka gareni kai a wani matsayi kake da zaka tsareni da wanan maganan akan mijina.
Ciki da alaman mamaki ranshi bace ya ware idanuwan shi a kaina yana fadin what ke kanki daya kuwa yarinyar nan kinsan ko wa nake a wurin jackson ?
Nima a fusace nace gomane gareni kai waye da har zaka tsareni da wanan dokan akan ya jafar din.
Daki kuma ko gobe zan shigesa ne don dakin mijinane bana wani ba kai wani matsayi kake dashi a wurin shi daya har ya baka daman yi min wanan tambayan ?
And kuma ka sani duk duniyan nan banga mahalukin da a yanzu ya isa min wanan banzan tambayan da kai min ba a yanzu kokai ka fadane a cikkn maye kila.
Kamar yadda kace rayuwata ta samu illa idan har hakane ina ganin ai wanan damuwatace bana wani ba ko ?
Daga hakan na juya na barshi a wurun tsaye baki bude yana bina da kallon mamaki don jin abindana fada.
Nayi kokarin mayar da mood din fuskana a hakan bai dameni ba saboda kar ya gane maganan shi yayi min ciwo sosai a raina.
Harna nufi hanyar dakina sai na canza shawara na nufi dakin anty fadila a lokacin saidai bata a cikkn dakin yasa na jiyo don na koma dakina cike da bacin rai atare dani.
Da kyar na samu na karasa daki na shige a take naji wani irin zazzabi yana neman ya rufeni lokaci guda.
Gado na fada na dafe kaina gabana yana faduwa nake fadin wanan sace irin bakar ranane haka gareni da har wani dan aiki zai fada min irin wanan magana kai tsaye.
Komawa nayi na zube rigingine ina lumshe idona yayin da buguwan zuciyana yake karuwa gareni lokaci daya.
Na dade kwance a hakana kafin tunane yazo min ina tambayan kaina shi din wai wani irin matsayi yake dashi a gurin ya jafar din da zai min wanan kalamin haka ?
Cikin wani hanzari na mike zaune bandaki na fada na dauro alwala nazo na hau sallaya na fara sallah ko wace ruku,u da sujjada sai na gayawa mahaliccina Allah damuwata kafin na danji sanyi a zuviyana.
Ban kara fitowa falon ba kamar yadda anty fadila ta umurci inyi don wanan maganan da mukayi da tajjudeen din ranan ga abi kuma ya tsaya min a raina sosai don ko barci bai barni nayi ba sai faman tunane da nakeyi a daki ni kadai.
Washe gari ma ban leko waje ba har wuraren sha biyun rana ina dakina a cikin damuwa da fargaba da zancen wanan mutumin a raina .
Gashi lokaci daya duk nabi na susuce ga baki daya idan mutum ya kalleni zai fahinci ina cikin damuwa a tare dani.
Suko a zaton su maizube ina wurin yaya jafar dinne a can na kwana a wurin sa don hakane ma tunda ta shige dakinta bayan zuwan shi bata sake fitowa ba har wanan lokacin.
Anty fadilace da tajini shiru ta leko dakin sai ta sameni a kwance cikin wanan yanayin na damuwa a tare dani din.
Tunda ta shigo dakin take watsa min kallo a razane kamar tana nazarin yanayina yayin da niko ganin ta dakin nawa yasa na dan kakaro fara,an dole a tare dani.
Saida ta kai zaune a kusa dani take fadin meke faruwane dake haka kin rame haka a cikin kwana daya ?
Kina da wata damuwa ne a tare dake da ya mayar dake haka lokaci guda duk kin zabge ko wani abin ke damun ki haka ko kuma ganin mijin kine ya sakaki fargaba ?
A ladabce nace da ita a, a anty lafiyata kalau illa dai kewan innata da kannena da nakeyi duk kwana kin nan.
Murmushi tayi taba fadin baki tashi kewan su ba saida mijin ki ya dawo kika saka damuwa haka a zuciyar ki lokaci guda.
Kaina na sada kasa ina dan murmushin yake kafin naji tace kinga fada min damuwan ki zainab don nima akwai abinda yake damuna dan zuwan mijjnki garin nan .
Don ba wani ya fada min ba Allah ya nufa inji komai a kunnuwa na yau din nan da safe na fito don duba masu girki dazu.
Da sauri na dago kai ina kallon ta don jin karin bayani daga abinda take hashe din lokaci guda kuma sai kunyar hakan ya