Showing 3001 words to 6000 words out of 191310 words
Chapter 2 - ABU CIKIN DUHU BY MAKAWA By abooks.com.ng.txt
rashin sanin muhinmancina a gidan nan.
Daga inda Abba yake tsaye yana jin Asabe takai ayah yace kiyi hakkuri umma .
Kin sa halin da nake ciki yanzu aikin ne nawa babu kasuwa ko ina ya rufe yau kwana uku sai ita saudatune ke dan dabara a cikin aljihun ta muna samu muna dan tabawa.
Asabe tace da mamaki karara a fuskan ta take fadin haka ka koma ban sani ba dan nan ?
Kai bakaji kunyar fadin wai ashe mace ke ciyar damu duk kwanakin nan a gidan nan ba.
Mafarin abin gari ana yadamu da fadin talaucin mu yakai haka har mace ce take ciyar damu a gidan nan kai ka kasa.
Kaga amfanin haihuwan da namijin da nake fadama ke nan da yanzu yarinyar nan namiji ne aida ta fara taimaka maka ta wani gurin.
Inna ta fito dakin ta nufi wurin madafin danbun tsakin masaran data hadane ta shiga rabawa yayin da tsakar gidan namu yayi shiru kowa ya zuba idanu yana kallon inna.
Na Asabe ta fara zubawa ta mike ta nufo ta tana fadin umma akai dakine ko a kawo maki nan aje anan in gani Asabe ta fada a hasale.
Saida Inna ta kai kasa don girmamawa ta aje kwano a gaban ta inda take zaune saman kujera dan tsugunno.
Bude kwanon samiran tayi tare da juya dan danbun dake cikin kwanon a yatsune tana tabe baki kafinta dago kai tana fadin.
Saudatu wanan abincin fa kamar za,aba dan goye shi ta juya wurin Abba tana fadin ka duba dai ka gani da idanuwan ka yanzu dan abinda aka zubamin.
Don kawai kace itace ke ciyar damu a gidan yanzu ai dole wullakanci ya shigo a bani abinda akaga dama don kawai rainin da kaja muna don kasawan ka yanzu da gidan.
Umma ba hakana bane kiyi hakkuri tsakin ne baida yawa iyakarshi ke nan dan gyara don yaran nan dake.
Nasan nida malam ba samu zamuyi bama a karshe tace duk da haka a kara min don wanan dai ba isane zaiyi ba ehhe.
Kallin Asabe nayi lokacin da naji ta fadi hakan ina mamaki hali rashin tausayi irin nata duk da jin zancen inna din da tayi.
Dakuwa ta jefo min da hannun tana hagu tana fadin daina kallo na yan nema mai kama da yanyawa.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
2️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
LITTAFIN KUDINE DARI UKU NE KACAL TA BANK KO KATIN WAYA DON TURAWA A BANK ZAKI IYA TURAWA A WANAN 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK ALLAH YA BADA IKON BIYA A CIKIN DAUKI AMIN
Ki daure ki guji shiga hakkin wani abinda ka raina shike zama babba gareka don Allah yar uwa mu guji daukan hakkin a kan mu ki daure ki biya ki karanta don Allah.
Hjy ce zaune a falon ta hannun ta rike da waya kaya take oder da za, a turo masu dan yanzu ba sai ka fita zuwa waje ba idan kasa hutar da kanka waya ya wadatar da komai ga kowa.
Sallaman da akayi daga kofane ya dawo da ita cikin hankalinta ta dago kai tana kallon kofan shigowa falon nasu.
Da fara,a a fuskanta tana aje wayan daga gefen kujera take fadin kune tafe sannun ku da zuwa a cikin fara,a kamaf yadda ta saba tarbon duk wani dan uwa da zaizo gidan musanman daga bangareta kona mijin ta .
Yanzu ma yan uwan mijin tane su biyu sula shigo gidan barin abinda takeyi tayi ta tari bakin nata.
Yau kan mun taki sa,a kina waje don zuwan mu biyu ana fada muna kina ciki bazamu ganki ba.
A daidai lokacin ta sauke glass din dake idon ta tana fadin abako fada min zuwan ku ba gidan nan ko sau daya.
Dayan tace yau dai aimun taka sa,a mun samu kina wajen dan dariya hjy iyami ta sakeyi tana fadin mun dade bamu haduba.
Safiya ya bayan rabo wace ta kira da safiya tace wallahi haka al,amari yakan kasance ai rayuwa ke nan idan na tuna baya sai nakanji kamar abubuwan da su dawo sabo.
Dariya sosai hjy iyami ta sake tare da fadin kin tuna zamanin kurciya ke nan dai ga wanan zancen naki.
Safiya ta lumshe ido tana bin lafiyan kujera sanyin AC yana ratsa jikin ta a hankali tare da fadin bari matar yaya ai kowa tuna bara baiji dadin bana bane.
Jin hakan hjy ta fahinci mai take nufi yasa tayi saurin kawar da zancen tana fadin bari a kawo muna abinci muci nima yanzu na dawo gidan .
Yau na fita ziyarane har gidan su Ado da salihu nake don tun zuwa na garin ban leka kowa ba bako dadi mutum yana kulaka kai baka mayar da kara akace.
Tana fadin hakan ta mayar da hankali kan wayanta dake gefe dauka tayi ta kira mai aiki tare da umartan a kawo masu abinci tana da baki a falo.
Kai matar yaya wai wasu baki har yanzu dai wanan halin naki yana nan ashe ance idan kasan mutum ko shekara nawa ne kada ka tambayi halin sa.
Murmushi hjy tayi tana fadin meye duniya sa,ade wanan duniyan har nawa yake ga bawan sa.
Idan badon muzo mun gani da idanun mu bazamu taba yarda da kina nan a yadda kike ba a yanzu.
Wai sa,ade ina da wa yanda sukafi min kune a rayuwa duk mace mai hankali da tasan ya kamata ai baki nata ba ko yaya yake kuwa.
Don samun duniya sai idon ka ya rufe ka mata da goben ka ko makomar yayan ka yau fa in mune gobe bamu bane.
Wani lokacin koda kana raye sai kaga anayi ba tare da kai haka abubuwan suke zuwa ai kinga gara mutum ya gyara tun duniya bata kisa ba.
Mai aikin data kirane ta shigo dakin dauke da katon ture da manyan kuloli abinci saman shi dining ta nufa da zuman jerawa yadda ta saba.
Sai hjy iyami take fadin ki kawo muna nan yau a kasa zamu zauna muci dan dariya suka kwasa tare da fadin za a tuna da baya ke nan dai.
Lokacin da yaya yake aiki lagos muna gida tare dake ake zuba abinci a cikin katon ture mu taru munaci ana hiran arziki.
Ai wanan abin duk shigowan sadiya ya kawar muna dashi tana fadin wai muna taruwa ana gulmanta bazan manta da zuwan wanan yar uwan hjyn mu datazo daga kauye take fadin kema ai saiki fito ayi gulman dake.
Budan bakin sadiya sai cewa tayi ni ba zan shiga cikin su rainani ba ko ita wanan don diyan tallakawane ita bata san kanta ba.
Dan murmushi hjy iyami ta sake don tuna wanan labarin da safiya ke fadi yanzu sa,ade tace yau ina arzikin nata dana gidan su datake tun kaho dashi din.
Duniya ke nan alokacin tana dauka tafi kowa da komai bata san me gobe zai iya haifa ba a gare ta.
Hjy ce ke fadin bissimilah ku muci abinci ko juyowa sukayi a lokaci guda suna kallo abincin da mai aiki ta hada masu gwanin ban sha,awa kai kace wani dinner aka hada hakan .
Haka kamshin shi abin sone ga mutum balle ya kai ga baki yaji dandanon shi.
Daidai hjy na zama a kasan take fadin ance yanzu koyarwa kikeyi safiya ke kuma sa,ade nursece asibiti ?
Ashe kina da labarin mu ke nan har yanzu tana daukan cokali take fadin haba aiba zan taba mantawa da kuba a rayuwana .
Adaidai lokacin data fara bude kulan tana mika masu plate a gaban su da spoon da fork ga kofuna da lemoka don sha aka tabardar masu.
Nan kowa ya shiga dirkawa cikin sa abinci suna danci suna taba hira yayin da sanyin AC ya fara ratsa jikin su.
Sai da anty safiya ta hadiye naman da take tauna a bakin ta na kaza take fadin a gaskiya mun gode daz bamu lokacin ki da nuna rashin kyama ko babbanci a garemu yadda ake nuna muna har yanzu a gidan mu.
An mayar damu bare a cikin dangi duk kokarin da baba yayi yaga ya hada kan zurian shi kafin ya bar duniyan nan .
Zan iya cewa daga ke sai mijin kine baku nuna muna wani bambanci a tsakanin sabanin sauran dake yawan nuna mu barene a cikin su ko yaushe wani abu idan ya taso na family din mu.
Din kawai mu uwarmu kadai ta haifa a cikin su lokacin da yaya ke raye yana iya kokarin shi damu amma tun bayan rasuwan yaya din abubuwa suka kara lalace muna ga baki daya.
Wani abin saidai mu tsunci labarin faruwan shi a gare bamuci arzikin da za,a fada muna ba mu.
A hsnkali ta lumshe idanuwan ta tana maijin zafin yadda ake yawan nuna masu a cikin yan uwan su din.
Tace ku dauka har yanzu ma yayan ku yana a raye ne safiya don ya barni ya bar zurian shi komai ke damun ku kofa a bude yake dakuzo da bukatan ku nan mudin dai abin baifi karfina ba agidan nan.
Sallama yan matan hjy ne da suka dawo daga school saida su ukune kawai don farida yar wurin hjy ba a kaduna take karatun taba tun dawowan su suka sama bata gurbin karatu Abuja can take zaune tana karatun ta.
Sai hutu take dawowa gidan haka yasa idan ba hutu akeyi ba zaka gansu su uku ne kawai a gidan.
Kansu a sama suka gaidasu kamar basu sheda ko suwaye su din ba garesu don kawai raina masu arziki da sukeyi.
Safiyace take fadin wai ba Rufaida bace da salma nan dan juyowa salma tana fadin nice daga haka tasa kai tana kokarin shigewa daki.
Rufaida salma kuzo nan hjy ta fada a kausashe saiga su sun dawo da sauri suna fadin gamu mommy ta nuna su safiya da hannu tana fadin baku san wa yan nan bane halan ?
Mun sansu mama gwaggo safiyace da gwaggo sa,a salma ta fada a dan yatsune kafin hjy tace duk da kun san su saidai kamar baku san yaya suke da mahaifan ku bako ?
Nan kan shiru sukayi suna kokarin dukar da kawunan su kasa don sun fahinci mai hjy take nufi da fadan hakan.
Karna kara ganin kunyiwa wani babba wanan gaisuwan koda basu din bane wai salma sai yaushe zaku gyara halin kune don Allah ta fada a dan hasale .
We sorry mommy gajiyace dama ya hana mu tsaya dan Allah ku ban guri marasa ta ido kawai ta fada a dan hasale.
Bayan shigewar su dakunan sune anty safiya ta sauke ajiyan zuciya tana fadin kindai gani yanzu ke nan ai.
Wanan ba akidar kwarai bane ka nunawa yaro ga yadda kake da dan uwanka har abin yazo ya shafi naku yayan nan gaba.
Mikewa sa,ade tayi tana fadin antyce ma dai ta damu da wa yan nan mutane, nina dade da zubar da duk wani wanda ya nuna baison wata alaka zumunci dani ai.
Zancen ta baiwa hjy dadi ba ta fahinci akwai bacin rai a cikin halaiyan da yan uwa ke nuna masu kasancewar su su biyun yan uba ga yan uwan haihuwan nasu.
Sallama sukaiwa hjy tare da mata godiya da nuna jin dadin su irin taron data nuna masu din bata nuna masu halin da yan uwa suke nuna masu a cikin su.
Ita kanta bata samu mahaifiyar su a gidan raye ba saidai ga yadda take jin labari zamane akayi bana dadi ba a cikin gidan lokacin da mahaifan su suke a raye wanda itama ta dan ga wani abu a rayuwan datayi dasu gidan kafin Allah ya azurta mata mijin ta harsu bar gidan zuwa lagos karshe ma suka bar kasan ga baki daya.
Lokacin ita kanta sarakuwanta tana yawan nuna mata tayi hankali da yaran don su din ba jinin taz bane diyane kawai na maigidan ta da aka haifa mai auren baya daya kara na karamar yarinya daya auro.
Ga yadda take ji sarakuwar ta itace mata ta farko a guri mijin su saida sukai kusan shekara hamsim a tare ya auro mahaifiyar su safiya din.
A cewar hjy ita ba a hadawa diyan ta yan uba don haka ta hana mijin nata kara wani aure daga baya .
Surukin nasu yana sana,a a kauye har ya shigo birni ya fara sayar da kayan mata irin su dan kune da sarka da jakkuna.
Daga baya kuma daya bun kasa ne ya fara sayar da gwala gwale wanan ne ya kawo mai tarin arziki mai yawa har ya tamfasawa iyalan shi katon gida da suke zaune a ciki.
Bawai bokaye kawai ko asiri taga sarakuwar nata nbi ba saidai iri matan nan ne masu ji da izza da isa da gadara wanda take ganin yanzu diyan nata da jikoki suna koyi da wanan halin.
Saidai daga bayane kariyan arziki ya afkawa mijin nasu bayan siyasan shehu shagari da mazajen arewa da dama suka samu wanan koma bayan a sanadiyar canji da gwaunatin soja mai a lokacin ta kawowa mutane yayi sanidiyar karewa wasu bayin Allah da dama a cikin su har da surukin nata ya samu wanan iftila,in tare dashi.
ANCAU KADUNA STATE
Kamar yadda Asabe ta sha alwashi akan Abban mu dole sai ya kara aure hakan ne ya faru don Asabe taje nema mashi auren yar wata mata da ta dade tana zawarci batai aure ba a kauyen mu.
Tun innan mu bata san wanan zancen ba har yakai ta sani saboda bakin Asabe dake sake suratai barkatai na rashin ilimi da jahilci tare da kiyayya ga inna damu diyan ta.
Da yake Allah yayi inna mu mace ce mai hakkuri da kawar da ido ga komai koda tasan kaine ke cuta mata din.
Sai ma bata nuna tasan Asabe nayi ba a gidan don bata nuna damuwata ga abinda Asabe ke yawan fadi ba ko yaushe.
Mu kan mu bamu tsira ba gurin Asabe don tana nuna muna tsana karara kamar ba jinta muke ba mudin .
Daga zagi sai dungura dan abu kadan yanzu zata sauke muna bala,i a kanu komai mukayi bamuyi daidai ba.
Ainihi Asabece mahaifiyar data haifi mahaifin mu ta hayayyafa da dama basa tsayawa da sun dan tasa an yayesu sai zazabi ya kama su su mutu.
Sai ya kasance ga mahaifin mu ta samu ya fara tsayawa sai mace da muke kira da gwaggon birni don a birni take yanzu da mijin ta daya samu wani ubangida a can ya daukesu bayan aure ya mayar dasu a birnin.
Sai ya kasance mahaifin mu yanzu kawai a gaban ta sai yan jikoki da take dashi ta tsatson shi wanda kiyayyan fitowan mu diya mata a duniya yasa bata kaunar mu har cikin ranta.
Ni dana dan kawo wayau a cikin mu nasan halin da muke gidan na zaman Asabe da innar mu don su sauran yan uwana gorin inna bai taba tayar masu da hankali ba sai ma kawai ja baya da sukayi da al,amarin ta.
Don yawan fada da zagi da take muna a gidan duk da Abba ya dan kewayewa Asabe gefen ta ma,ana ya dan raba tsakanin mu da ita sai dai hakan bai hana Asabe fitowa zaman sa ido ga inna damu.
Wajen karfe dayan rana kasancewar yau asabar muna gida bamu zuwa boko mun dawo islamiya tun sha daya muna gida.
Ina daki ln mu na yara don shigata ke nan na gama wanke tufafin mu da suka dan taru nayi wanka ina shafa mai.
Naji muryan innar mu tana kwala min kira da yar mairo na amsa da Na,am inna daga dakin tare da saka hijjab a jikina na fito da sauri.
Ina fadin gani inna tace yi maza ki dauku abincin nan ki kaiwa umma kada yayi sanyi nace tau inna tare da dukawa na dauki kwanon samiran abincin Asabe.
Munace mata Asabe ne don dukka gari haka ake kiranta dashi in ka debe Abban mu da innar mu koshi Abba sai zuwan inna ne gidan ya canza mata suna dama da Asaben yake kiranta.
Na isa kofan Asabe ina ta sallama bata karba min ba haka yass na kunna kai dakin na aje mata abincin a gefen kofan ta kadan ko waige banyi ba na fito daga dakin.
Dawowa nayi na karasa shirina kafin mu zauna cin abinci tare da yan uwana don a tare mu hudu ake hada muna abinci don yana kawo dankon zumuci inji manya sukace.
Muna gab da gamawa sai ga Asabe tun kan ta karaso wurin mu take kwalawa inna kira cikin tashin hankali.
Gaba dayan mu hankalin mu ya koma gare ta muna duban hanyar kofanta tana zuwa take tambaya wa yakai min abinci a dakina ?
Cikin sanyi murya irin na innar mu da kusan kowan mu ya