Showing 60001 words to 63000 words out of 191310 words

Chapter 21 - ABU CIKIN DUHU BY MAKAWA By abooks.com.ng.txt

ladabi.
Sai naji ina kwadayin hada iri da ita don irice mai amfani ita din ba abin yarwa bane haka.
Hjy nima yarinyar ta kwanta min a rai sosai ina kulla da ita tankar yar cikina don bata da kyashi ga sanin ya kamata kamar wata babba can.
Tarbiyane idan kinga haka ta samu tun daga gida uwarta ta tarbiyartar da abinda yadda akeson ko wani da ya kasance sai ki kara himma wurin riko Allah ya taya ki rikasu.
Don tafi min wa yan nan marasa moriyan sau dubu a wurina sai hjyn tasu tace tafisu kan gaskiya yaron da ba sai kace ya tashi yayi ba yake abu ai yana da dadin zama.
Hjy kin san wancan zuwan da nayi da yaran nan iskancin da sukai min saida muka koma gida nake ji nayi masu tas wallahi.
Kiyi hakkuri dasu tunda su suka kawo kansu gare ki inma sunyi maki don kansu kowa ma zai girbi tsiyar shi ai.
Ke dai ki rike wanan bisa ga amana da yarda idan dai bata kauce bane don mutum mugun icce ne sai yaga ya ginu yace kaine makiyin sa daga baya Allah ya kare mami ta amsa da amin.
Sai dare mazan suka sake shigowa ina daki naji hayaniyan su ban daga daga inda nake zaune ba naji muryan mami ta fito daga uwar daka tana fadin.
Garin yai maku dadi ke nan ko kun shige cikin gari tun dazun ina shi aboki yake ne banganshi tare daku ba.
Wanan friend naki saike mami yana masallaci mun barshi wai yanzu yake son sallam guards din shi su koma kaduna su kwana.
Da daren nan tau haka dai yace don wai baiga inda zakaisu ba nan suwa ke nan tsohuwar ta tambaya.
Security din da mijin ki ke tafiya dashi don tsaro yaya jamal ya bata amsa a takaice take fadin.
Ikon Allah tafiyan ma sai anyi shi da masu tsaro ko may sai yaya mamud yace kin san su can hakan ai wani abu ne tundaga can aka hadu shi dasu aikin su sukeyi su.
Duniya inda ranka kasha kallo yanzu shi wanan dan figegen aron ne harda wasu masu tsaron shi.
Hjy mu a nanne ba a dauki tsaro da mahinmanci ba amma su can idan har kai wani abune dole kana da masu binka a baya ai massanman shi da sukeji da shi a can.
Waini na kasa gane aikin yaton nan sai jalal yace bako zaki gane ba don shi bros telent ne sosai ilimin shi yaja masa hakan.
Yanzu zai iya kera maki wani abu a wurin nan wanda sai kinyi mamaki don har abin yai tafiya da kafansa su ake kira da sciencetics mana masu fasahan kwakwalwa ikon Allah tace.
Tare da fadin gaskiya yaki aure haka har yana batun rufe arbain fa don in ba zan manta ba tun mulkin shagari na farko aka haifeshi ai.
Kai hjy wanan tashin tasgin haka kan friend dina yanzun dai ni abinda nake so kafin ya tura mutanen nan a cikin daren nan ai masu kokarin wurin kwana hjy.
Tshohuwar ta tambaya su nawane akace hudu hudu ta fada da mamaki tana fadin har karte hudu ke yawo dashi wanan abindai da nake gani.
Ikon Allah yafi gaban mamaki yau ace wai dannan ne Allah yaiwa bawa haka Allah ya ciyar daku baki daya suka amsa da amin.
A daidai lokacin da dan bawan ke shigowa yana waya tsohuwar ke fadin gama yanan ya shigo dayani.
Kai yanzu don baka da tausayi zaka tura yaran mutane da daren nan su koma kaduna don rashin imani.
O lord wanan kuma wani zance take hakane da shigowan mutum ya fada yana kaiwa zaune yana aje wayan da yakeyi.
Aboki wai yanzu da daren nan zaka tura security din nan su koma kaduna sai naga dare yayi ai.
No sun fasa ai mami uncle bello ya sama masu wuri zama da zasu zauna suna can sun tafi suga wurin kafin su dawo su dauki abinci.
Ko kaifa nace ko kai fa dan nan amma ka tura bayin Allah a cikin daren nan haka ai abin baiyi ba kamar dai ba mutane a nan.
Enough dan Allah waiwa ya fadawa wanan mai wa,azin ta damu mutane da wa,azin nan nata a gurin nan.
Kai rufamin baki aini yanzu nasan ba cikkaken namiji kake ba don a matsoraci nake kallon ka yanzu tunda sai an rakoka har karkaran mu matsoraci.
Daidai lokacin nake fitowa daga dakin don kira da mami tayi na amsa daga ciki.
Dariya ya bushe dashi bashi kadai ba duk wanda ke falon saida maganan ya bashi dariya yadda suke kwasa dashi din.
Barin gani idan baki tsorona din da gaske ya fada yana mikewa ya harota ta juya tana neman abinda zata kare kanta kafin ya iso gareta .
Tayi sa,a filo na kusa da ita ta dauka wai dashi zata kare kanta din tana kaimai duka yana dariya ya juyo a daidai lokacin na kawo wurin zan wuce sai ji nayi kumus nayi baya tangal tangal zan fadi.
Mami tace zaka karya min da da wanan karfin naka haka kamar na doki shi kuma ya juyo yana fadin oh sorry .
Tsohuwar nan kinga zaki saka in karyawa mami yarta don fitinan ki to yaushe rabo damuyi fitinan haka.
Ai rabu a gana arzikine dan nan wata ran idan kunzo sai kun tunani da wanan wasan da mukeyi yau ina Alh ina mahaifin ku sun kare.
Kowa yai wani iri a dakin don abinda tsohuwar ta fada wallahi hjy gashi yau muna kewan tsohon nan don da zaran zan shigo naga part din shi sai in tuna da lokacin da muke zuwa yana bamu mazzakwala muna sha yaya mamud ke fadi.
Kai mukan bamu sanshi ba gaskiya sai dai a photo jalal ya fada ai old man din nan ya kware mu daya tafi bamu sanshi ba.
Waike zeey kin debi abincin nan kuwa na juyo ina fadin ban diba ba mami yanzu na idar da sallah dama.
Jeki ki dibi abinci da wanan halin naki ga abincin mu can ankai mana daki tun dazu wanan nasu sai na mutane yayan ku yacan sai a samu yaro yakai masu idan sun dawo.
Juyawa nayi zan koma dakin don ban iya sake jiki suna wurin don haka na juya don na koma dakin hjyn su mami.
Banji me yake fada ba yaya jamal yace ke wai kizo ki zuba mai abinci yar mami.
Jin an ambaci sunana yasa na tsaya tare da juyowa na dawo zuwa inda abincin yake aje dan kallon yaya jamal nayi ina fadin wa zan zubawa.
Yaya jackson ya fada hankalin shi naga wayan shi rasa abinda zan zuba mai nayi don kuloli ne gurin zasu kai biyar duk an cikasu da abincin alfarma har da fate da mami tace tana so yaji gyada a cikin sa.
Fara bude masu kulan abincin nayi don ya zabi abinda ranshi ke so sai dai baya kallona hankalin shi naga waya yana rubutu.
Yaya me zan zubama na tambaye shi ina dan gurfane a gaban shi don ba dining table falon tsohuwar kamar can gida kaduna.
Ya dan dago kai yana fadin anything zaki iya zuba min Aisha ta fito daga dakin yaya mamud daya karbi plate din da mami ke shan fate yana dan sha yake fadin Essha kina gidan nan ashe tun zuwan mu ban ganki ba.
Ina kwance ne yaya ta fada tare da ratsowa ta zauna a hannun kujera tsakiyan su shi da yaya Jafar din.
Ke may kike a wurin nan ne haka ta tambayeni ya Jalal yace wai abinci akace ta zuba take tunane na dan kalleta ina fadi a hankali ban san may zan zubabane ai.
Oh shine kike tsaye a gurin ya mamud yace ka duba ai tana da gaskiyar ta kada ta zubama abinda baka so ne.
Wanan dai ina so inga matar shi kafin in mutu yaro da izza da isa kamar wani basarake dashi matar ka tana da hakkurin zama dakai haka.
Hjy naga fa yau sai yar tsama kuke da yaya Jackson tunda muka zo Jalal ya fada don shi yafi yawan dan magana bisaga Jamal dake da zubin yanayi ya jafar din wasu halaiyan su suna da kama sosai.
Aure nake son yayi hakana ya baku wuri kuma ku samu ku zaburo wanan gwauron ya tare maku wuri.
Muka fada maki samarin suka fada tace to ai shike nan tunda baku son a matsa mai yayi aure.
Wanan fa zata iya hada ma abincin nan duka tunda kace anything zata dauka kace tayima mix ne gaba daya Aisha ta fada tana kallona.
Ke zuba min ki daga min nan don Allah ya fada tare dan dagowa yana kallona.
Hasken kwan fitilan falon ya haskani gaba daya launina bada wani kala na daban ga mai kallona a lokacin.
Na duka ina zuba mai kullan gabana wanda sakwara ne a ciki ashe sai na bude kulan miyan shi dake dauke da miyan ganye yaji egushi da manyan nama na zuba daida don nasan shi baya cin abinci da yawa.
Mikewa nayi zan bar wurin ya kara fafin ruwan wanke hannu fa ba tare daya ko kallo inda nake bai yi ba yai magana.
Har suka bar falon ban kara fitowa ba sai bayan danaji fitan su sunawa mami saida safe na dan kara mintina na fito.
Kayan da sukaci abinci nake kwashewa yayin da nazo kan nasa naga spoon a ciki da alama dashi yaci.
A raina nace bakin bature ke nan abincin ma da cibi zaici don sallo ai kakar nan tasuce maganin shi.
Tas nayiwa falon kafin in shiga wurin mami ina tambayanta koda abinda zanyi mata kafin na kwanta.
Zeey a kwashe kayan abincin nan da sukaci nace na kwashe mami ki duba min kayan barci na a cikin kayana ki ban shike nan sai kije ki kwanta.
Har na kwanta a saman dogon kujera anty Aisha ta shigo tana fadin af namanta da charger na dakin tsohuwar nan dan Allah zeey dauko min.
A kofa na tsaya nayi sallama kafin in shiga dakin yanayin dana samesu a ciki nagane wani magana sukeyi mai muhinmanci a tsakanin su su hudu.
Tsohuwar da kuma kannen mami din duk suna zaune sunyi shiru da suka ganeni.
Sai mami ke fadin bakiyi barci ba ashe zesy a, a nace nake fadi charger anty zan dauka ganin suna kallona duk sai na tsargu .
Na dauka na fita da dan saurina daga dakin don ban son in dakatar masu da maganan da sukeyi din .
Washe gari tunda safe dana tashi nayi sallah na fara gyaran falon har zuwa waje ina jin hayaniyar su dakin har na gama wanka na shiga don mami tana cikin dakin da yan uwanta.
Sai kusan karfe goma suka fara shigowa falon ana gaisawa a tsakanin su babu muryan wanda nake jin tsoro don haka na fito na gaidasu da kwana ina jin mama Ramatu na fadin.
Ga abinci nan tun safe aka aje masu shi basu shigo ba ina shi jafar din gana yan aikin shi nan suma .
Bai fito ba jamal ya bata amsa tare da fadin mama kinsan shi baya fitowa da wuri haka ai sai idan ya gama abinda yake yi.




ZAINAB IDRIS MAKAWA










🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅




1️⃣9️⃣




ZAINAB IDRIS MAKAWA


YAN UWA FATAN ALHERI HAR KULLUN A GARE KU UBANGJI YA GAFARTAWA MAGABATAN MU DA DUKKAN MUSULMIN DUNIYA ALLAHUMA AMIN.

YAR UWA BA ZAN GAJI DA TUNATAR MAKU BIYA KAFIN KI KARANTA BA DON KAICEWA SHIGA HAKKI GA MASU IMANI ALLAH YASA MU DACE AMIN DARI UKU NE KACAL KI GUJI RAINA HAKKIN WANI A KANKI DON ALLAH.


Saida gabana ya fadi don jin muryan dodona da ya shigo gidan bani kadai na gane ina tsoron shi ba don har salma, Rufaida da Nazifa.
Idan ya shigo na kanga sun shiga taitayin su a gidan har jamal da jalal suna wanan rawan jikin da kama kai a gaban shi idan yana kusa .
Nima hakan da nagani ya darsa min tsoron shi a lokaci guda duk da ban taba ganin wanda yaiwa cin fuska a gabana ba.
Dagowa nayi a rikece ban ko debi abincin kwarai a platen din ba don in gudu in koma dakin mu.
Na dai samu gaida shi da kwana na jakafata na shige dakin zama nayi don cin arish da kwai dana debo a falon .
Nayi loma biyu ne naji mami na kwala min kira daga falon da sauri na mike na fito falon ina fadin mami gani.
Tana can tana magana da mama Ramatu kanwarta a lokacin kafin ta juyo tana fadin .
Yauwa zeey don Allah yi serving din yayan ku gashi nan ya shigo yanzu ni zan dan fitane yanzu zan dawo.
Tana fadin haka ta mike sai naji yana fadin amma da mota zaku don akwai dan nisa daga nan gidan.
Eh ai shine yasa nace Jalal ya sauke mu kada yaje nisa yana waje yana jiran fitowan mu ai.
Amma mami jalal ne zai jaku ga driver suna waje sai shine zai jaku ban faye yarda da tukin yaran nan ba gaskiya yake fada da turanci.
Sun saba jana a mota ko a kaduna don hakane ai na yarda da tukin motar nasu.
Allah tsare yace yana mayar da kanshi ga wayan dake hannun shi aikin shi ke nan ko magana yake hankalin shi a kan waya ko sytem din shi shiya a raina nasa mashi mayen computer.
Abincin na gama zubawa lokacin falon daga shi sai tsohuwar dake zaune itama kudi take kirgawa daga haban zanin ta nakai mai abincin gaban shi na aje.
Ruwa na koma na dauko na aje mai cikin dan muryana nake fadin yaya ga abincin nan do gudun kada inyi laifi kuma gare shi.
Jin abinda nace yasa shi dan juyawa saman lafiyayyen kujeran falon tsohuwar da zaka iya da kira dakin wata amaryace can don haduwa.
Wayan ya aje daga gefe kafin yakai kallon shi ga abincin ya dago kai yana kallon tsohuwar kuma.
Kai kai kai wanan tsohuwar ko fashi kika farane haka ina kika samo wanan kudin haka masu yawa ?
Yanzun kuma bakiki kariba don baki da tausayi sai kuma kin karbewa mami dan kudin ta maimakon ki kara mata.
Kafin tsohuwar ta dago kai tana fadin ja,iri da hausan ka kamar na mai koyo uwar taka mai tausayina ita take aiko min da kudin ai.
Yau kuwa zance ta daina don ba kashewa kike yi ba boyewa kike yi idan an baki ashe.
Ina wurin fridge ina daukan ruwa insha suke wanan barkwamcin da kakar tasu na dauko ruwan na juya zan wuce daki don da farko tsoron shigowan shi ya hanani daukan ruwan .
Naji yace ke wanan uban abincin da kika zuba ni dawa zanci shi haka ?
Tsayawa nayi wuri daya da goran ruwan a hannu na ya sake fadin sai kizo ki dauka ki cinye shi tas.
Cikin karfin hali nake fadin na debi abinci yanzu yana daki na aje zanci kai wanan yaron da fitina kake wallahi ina laifin yar nan tana iya kokarin ta da kai.
An fada maki kowa irin kine dake loda abinci a cikin sa yana kiba kamar za,a tafi gasan gwaji dashi halan ?
To ba zataci ba idan zakaci kaci da yawan fitina har yaushe zaka zauna kana matsawa yarinya mutane haka.
Yar nan ko karyawa bata samu tayi ba yanzun taga ba yan uwanka abin kalaci suka fita kai kuma kazo da naka tsurkun yanzu.
Idan kayi fushi sai kaje kayi aure kowa ma ya huta mitar ka na tsiya kaji min yaro da jarabar tsiya haka.
Hjy dama naga kin gaji dani ai ki huta min gori yau kaduna zan kwana idan Allah ya yarda idan ka tashi ka wuce jos zaifi ma sauki ai.
Ina tsaye wuri daya ni ban gusa ba ina sauraren da bai karewa da tsohuwar ko da yaushe sai dai idan basu hadu ba idan kuma bata ganshi ba ta kafa mita ke nan ina ya shiga.
Zo ki dauki abincin nan na fasa ci ya fada da dan karfi simi simi na tako zuwa gaban shi ina zuwa nakai kasa tare da fadin.
Don Allah yaya kayi hakkuri na fada ina kaiwa kasa kamar zanyi kuka a gaban shi bace min dagani a nan na firgita sosai tare da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login