Showing 6001 words to 9000 words out of 191310 words
Chapter 3 - ABU CIKIN DUHU BY MAKAWA By abooks.com.ng.txt
gado hakan take tambayan Asabe wani abin ne inna ?
A hasale asabe ke fadin tambaya nakeyi wa kika aika yakai min abincin don yanzu na aje dankali na fito bangani ba .
Haka yasa nasan duk wanda yakai min abinci shine ya daukan min shi dama an dade ana min sata a daki ina hakkuri banda dama in aje yan kwabbaina sai in nema in rasa.
Da sauri na furta Allah ya tsareni da daukan abin wani nina kai abinci kuma ko kallon dakin ki banyi ba na fito.
Ke rufa min baki kwadayayya satan naku har yakai haka ban sani ba dole in kira mai gyara ya saka min kuba a kofana don watarana kada kuyi min wanda yafi wanan.
Wani irin bakin cikine ya rufe ni a lokaci daya ina jin idona kamar zai rufemin a wurin don satan dankalin da Asabe ta laka min.
Da ba don nasan itace ta haifi mahaifin mu da naja mata Allah ya isa a gurin duk da hakkurin inna saida tayi magana wanan karon.
Haba umma a gabana yarinyar nan ta shiga takai maki abinci ta fito kuma ban ganta da komai ba a hannun ta.
Ai dada goyon bayan ta zakiyi ta fara mugun abu tun a gida idan yayi karfi sai ta zauna maki a gida ai don babu mai kwasan barauniya yakai gidan shi.
Abbane yayi sallama ya shigo ganin mu cirko cirko a tsaye bai hannashi fadin yanzu dankaline har yai yawa haka a gidan aka barwa Akuyan umma tana ci haka?
Gaba dayan mu kallon Asabe mukayi don jin abinda baba ya fada nan kuma ta fara kame kame tana fadin .
Hannu na dora akai na fasa wani uban ihu ina fadin Asabe mai nayi maki kika dafa min sata a gaban kowa.
Ashe akuyan kice ta daukar maki dankalin ki kazo kina fadin nice na satar maki harda kudi nake shiga dakin ki in sata.
Abba ya daka min tsawa tare da fadin ke ke meye haka kike fada da sauri kanwata Fatima dake bi mun take fadin Abba yanzu fa Asabe ta gama fadin wai Abuce ta sace mata dankalin ta a daki daga kawai takai mata abincin ta da innarmu taba takai mata.
A wani irin yanayi na bacin rai da mamaki lokaci guda Abba ya juyo yana fadin sata kuma umma ?
Ina yaran ne jinin kine umma koda itace ta daukar maki ai ba zaki kira hakan da sunan sata ba.
Ta daka mashi tsawa tana fadin yi min shiru wanda baisan abinda yakeyi ba.
Yau aka fara sata min abu a gidan nan bana magana don gudun irin haka in magana ku karyatani a gaban diyan ka da matan ka.
Waya sani ko itace ma ta dauko din ganin za,a ganeta ta jefawa Akuyan nawa.
Allah ya sauwaka Abba yace ya nufi hanyar dakin su bai shiga ba ya duka ya dauki buta zuwa ban daki.
Asabe ma ta juya zuwa sashenta tana fada inda take shiga ba nan take fita ba wai Abba da innar mun suna lalatamu da gurbatacen tarbiyan da suke bamu.
Inna kan daki ta shige tana kuka hankan yasa dole na tsayar da nawa hawayen don komai ya wuce a ran inna.
Tun faruwan wanan abin na ja baya da lamarin Asabe ba ruwa na da tsabganta iya
kana da ita gaisuwa ban yarda in shiga ko lungunta.
Muna kallo idan jikokin ta na birni sukazo yadda take ji dasu take nuna kamar su kadaine ta haifi uwarsu sam mu bamu isa mu rabe ta ba.
Shi yasa ake fadin kakanni sun fison jika na wurin diya mace don ni na tabbatar da wanan maganan gun kakantamu.
Sannu sannu har lokacin Auren data nema wa Abban mu ya karaso buki ya tashi sosai Asabe ita tayi uwa tai makarbiya don Abba yace shi baida zarahin kara aure a yanzu.
Ta saka aka tayar damu daga dakin da muke kwana munaji muna gani aka gyarashi tsab wace kullun take kukan bata da kudi sai gata ta fitar da kudi don kawai taga ta kuntatawa innar mu rai .
Sai fadi take Allah dai ya kawo amaryan Abba tazo ta haifa masu magaji a gidan ko suma zasu shiga fagen zurian dake tun kaho da diya maza a gari.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
3️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
LITTAFIN KUDINE DARI UKU NE KACAL DON SAMUN SHI ZAKIYI TEXT A WANAN LAMBAN DON LAYIN BAYA KASAN A YANZU KO KI TURO KATI WAYA KO KI TURA BANK DA WANAN LAYIN 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK NAGODE DA KULAWAN KU GAREMU, , , ,
Ta dade zaune tana son mikewa zuwa daki don ta dauko takardan da take son turawa saidai jikin daya fara manyanta tana jin kiuya da nauyin tashi daga falon ta zuwa daki a lokacin.
Wani wawan tsuki taja a ranta take raya ya kamata dai ta samu wanda zai dinga taimaka mata wanan dawainiyar yayi yawa a yanzu gareta.
Wayan ta dake gefen tane ya dauki kira ta dauko tana kara jan tsuki sai dai ganin bakon lamba dake kiranta ne kuma ga layin special nomba ne ya bata mamaki.
Taso share kiran don bata san mai layin wayan dake kiran nata ba a lokacin wayan yana gap da tsukewane ta samu ta daga.
Muryan namijine yake mata sallama ta amsa da mamaki don har lokacin bata gane mai kiran nata ba dai.
Bayan sun gama gaisawa ne mai magana ke fadin hjy nasan ba zaki sheda mai kiranki ba a yanzu don an dade bamu hadu ba tun muna US rabon damu gaisa.
Sai mamaki hjy keyi a ranta tana fadin waye wanan kuma wanda ban gane ba dan tunane tayi kafin tace isma,il soba ko ?
Dan dariya ya sake tare da fadin abin mamaki gaskiya kinyi kokarin sheda muryana is about 20 years yanzu da bamu hadu ba.
Ai ba zan manta da muryan ka ba a duk inda naji shi ta fada tana daure fuska kamar wanda take wayan yana kusa a lokacin.
Yace hjy sai naji kina kasan har kusan shekara daya da rabi abin ya ban mamaki matuka har ki shigo kasan nan muna jaha daya ban san da hakan ba.
Yanzu ka sani ai wakila don bai zama dole irin ku su sanda dawowan nawa bane nan ta bashi amsa.
Watau halin na nan a yadda nasan shi hjy baki barin ko ta kwana har yanzu ashe ?
Jin tayi shiru ba amsa yace hjy dama naso muyi wani magana dake ne wanda ya shafi rayuwan ki sai dai naga kamar baki maraba da wayana a yanzu.
Kai isma,il kafi kowa sanin halina don haka babu abinda ya shafi rayuwan ka dani a yanzu dama nasan don ka bata min rai ka nemi layina don haka ina maka warning da kada ka sake kirana.
Dan murmushi taji ya sauke dama yasan za a rina idan hjy iyami ce don bata daukan maganin raini ko kadan.
Shidin yasanta ta dalilin yin karatu a tare ne duk da ya girme mata sosai ga haihuwa amma haka suke shan fama da ita don akwaita da kwazo da basira a lokacin da sukai karatun tana goyon danta na uku ne .
Kawar da zancen yayi ta hanyar tambayan ta yaran don sunayen su bai bace mai ba har wanan lokacin.
Wanan tambayan yaran daya jefo mata yasa ta dan sasauta mashi tare da amsa mai da suna lafiya .
Ance in kana son kama uwa rike yaranta yanzu zaka zama masoyi a gurin ta hakan ko ya faru da hjy har ta manta da fadan ta dashi take fada mai rayuwan yaran ta a yanzu.
Karshe dai yace sai sun zo don bashi kadai ne zaizo ba akwai magana mai muhinmanci da zasu so suzo yi da ita.
Nan ma saida hjy tayi korafi akai kafin ta kashe wayan tana kara jadda mai cewa idan yasan shirmene zai kawo shi kadama su zo din .
Shi dai dariya yayi yana fadin sai idan sunzo din zataji sukai sallama ya kashe wayan.
Kai hjy ta girgiza tana fadin mutane akwai tsegumi har suna daukan zancen abinda bai shafesu ba suna dangantawa da lamarin su.
Mikewa tayi don dauko takardan datake so daki har lokacin tana maijin zafi a ranta na ba gaira ba dalili wata kila kuma har yanzu haushin wayan da abokin karatun ta yayi matane oho ?
Kiuyan fitowa dakin tayi zuwa falon ta har akai kiran sallah ta samu ta mike don zuwa sallah.
Yanzu idan akwai abinda hjy ta tsana shine rashin son motsa jikin ta don hutu yariga da ya gama ratsa ko ina nata ga yaran da take zaune dasu baka more ne gaba dayan su son jikin su yama so yafi na hjyn yanzu don gatan da ake nuna masu.
Sai dai duk da hakan tana dan kokartawa tana sakasu wani abin can ba,a rasa ba sai dai zata sha mita da jini duk tana hakkuri da wanan.
Wani lokaci kuma zata zage tayi masu fada sosai akan rashin son motsa jikin da basa yi dan abu kadan zasuce sun gaji.
KAUYEN ANCAU
An kawo amaryan Abba wata bakace gajera bata da tsayi saidai akwai mazauna irin na mata gareta.
Ni dai banga abinda nagani gareta ba sai halin kiyayya kawai da Asabe ta dagwarawa mahaifiyar mu in bashi ba babu ta inda ta kama kafan innan mu.
Zaman su ba yabo ba fallasa don inna bata shiga tsabganta ko yaushe tana kofanta ita kuma amarya tana lungun Asabe.
Idan muna gida mune abokan hiran innar mu sai kuwa ranan da akace itace da girki ranan zan fara labe labe don ban yarda da tsarin Asabe ba .
Na cewa mu dinga kwana dakin ta haka yasa na share dan karamin dakin da ake tara tarkace a gidan mu dakin ba wani girma ke gareshi ba asalima madafane Abba yayiwa innan mu don da dama tana wahalan girki a ruwan sama.
Abba yayi fada har ya gaji don ko naje lungun Asabe da sunan kwana bana shiga dakin ta saidai in tsaya daga waje.
Idan na faki idon Abba ya shige zan dawo wanan dan dakin in kwanta dama mu uku ne masu dan wayau da muke zuwa kwana dakin Asaben.
Zakaji tunda asuba Asabe na fada wai an jawo mata kwanan wahala a daki yara sunzo sun hanata shakat daki suna damun ta da tusan dare ko tace wai an mata fitsari a daki.
Ranan da tace fitsari kanwata dake bi mun tace itama daga ranan a inda nake kwana zata dinga kwana don sherin Asabe ya isheta.
Sai lokacin Abba yasan ban kwana dakin dole yakawo ido yasa mun hakana muka mayar da dan dakin wurin zaman mu koda da rana ne a nan zamu zauna muyi tsabgogin mu.
Wanan baiwa Asabe ba don ganin yadda mukan saka innan mu a cikin nishadi wani lokacin har mu zauna ana hira da dariya .
Sai kuma hakan ya fara basu haushi suka kulla wani sherin a kaina wanda ya girgiza mu ga baki daya yan dakin mu.
Ranan monday da safe muna ta shirin makaranta tunda naga Asabe ta fito daga lungunta zuciyana ke bani akwai wani abu da zai faru a gidan don daga dakin da muke ina jin muryan ta a tsakar gida tare da Lantana Amaryan Abba suna dan zance kasa kasa.
Don ranan inna muce da girki a dan dakin mu muka kwana inna tunda ta fito ta dama kokon safe da zamu karya dashi kafin mu fita ta koma daki don ta shirya kananun da basu iya shirya kansu sai an taimaka masu.
Na fito da sauri kada in makara kofan innar mu na isa ina fadin inna ni zan tafi kada in makara.
Na juyo inda su Asabe suke da zuman in sallame su lokacin Abba daga daki yake fadin kin karyane Abu ?
Na karya na bashi amsa daga waje don ban shiga dakin ba tunda na girma innan mu ta koya muna hakan idan Abba yana ckin dakin namu.
Zoki karbi murtala ki rike ko fanke kya saya a hanya Abba ya fada daga dakin.
Tsiyan banza dama nasan kai ke koya masu kashin kudi don baka gudun Abin kunya kai kan wa yan nan yaya matan naka.
Karatun bokon dole duk yan uwanka wa kaga ya dage kan sai diya mace tayi boko haka ?
Badani za, ayi wanan abin kunyan ba kuke nan ko yaushe ku dorawa ubanku wahala don kawai baisan ciwon kanshi ba.
Gani kunan haihuwan yuyuyu da aka tara mai agida ace har mace bakwai ko daya ba kawar ba a cikin ku.
Daku da uwarku kunki ku barshi ya ji da abinda zai ciyar daku da wanda zai tara yai maku aure nan gaba.
Amma kullun in sata in maita sai ya lalube aljihun shi ya baku dan abinda ya kwana dashi ko kuma in bakuje makarantar ba uwar ku ta lalabe shi a daki.
To hakan ba zai yuyu ba don baku da uwar ku kadai na haifarwa shi ba don haka daga yau na kashe wanan bokon naki.
Aure zan maki shekara goma sha hudu ai kin isa aure har kina batun wuce munzali.
Gwanda ki tafi dakin mijin ki yaji da sauran yan uwan ki da suka rage kafin suma a fitar dasu sai gidan ya koma hondaku .
Bansan lokacin da Abba ya fito daga dakin inna ba don tunda ta fara magana na zuba mata ido ina kallon ta cikin al,ajabi da mamakinta.
Muryan Abba naji yana fadin haba dai umma aure fa yanzu ga Abu haba wani irin aure kuma kamar yadda taken nan.
Hae guda nawa Abu take da za ace za,ai mata aure a yanzu akaita gidan miji ?
Wani tsawa ta dakawa Abba tana fadin yi min shiru shanyaye kawai wanda baisan ciwon kanshi ba.
Dame su hansai da Adawiya suka fita ga shekaru da akai masu aure kuma suna zaune kalau a dakin mazan su har yanzu.
Abba yace Allah ya huci zuciyar ki umma ni gani nayi har guda nawa Abun take ne da za a ce aure yanzu.
To ai gaskiya umma ta fada inji lantana amaryan Abba ta fada aure ga ya mace shine wajibi.
Ba wani karatun boko ba can da yanzu shike kara lalata yara yanzu haka idan ance ma yarinyar mnan tasan komai game da aure kada kayi musu.
Ke lantana ahir dinki ga bata min diya da wanan kalamin naki sai Asabe tace kaji sauna yo ai gaskiya ta fada ko karya nakeyi Asabe ta tsatsareni da idanuwan ta na tsufa.
Bansan lokacin da kuka yazo min ba na juya zuwa cikin dakin da na fito don jin sherin da ake kokarin lakaka min da farar safiya haka a gidan mu.
Sauran magana ban jisu ba saboda kukan da nakeyi makarantar da ban tafi ba ke nan ranan don maganan Asabe tankar umurni ne ga Abba gama kowa a gidan.
A karshe dai na fito yin alwala nake jin lantana na fadin toke umma tunda kowa yasan kyauta na dan maciciji ne babu masunsuni gareta.
Ai baki kyale haka a zuba mata ido ba dadai kin nemi wani a cikin kauyen nan ki hadata dashi zaifi sai aji da sauran .
Don muddin tana gaban ku haka ba wanda zai kula sauran duk sai ai masu daukan daya kinsan halin garin nan sarai.
Duk wanan zance da sukeyi inna tana jin su bata ko nuna tasan ana zancen ba ta kawo ido ta sakawa kowa don nuna ka waici ga wasu mata na karkara.
Har kwana hudu sati na batun shigewa ban shiga school ba na gaji da zama daki mu don ko tsakar gidan mu na daina fita idan ba wani abu zanyi wajen ba.
Daki innar mu na shiga na saneta tana nade kayan data wanke na yara gaida ita nayi ta juyo tana amsawa fara nade kayan nayi sai inna tabar min nadin ta juya tana fadi.
Saliha tazo tambayan kitso nace ta tafi ta dawo don nasan halin ki sarai dan ajiyan zuciya na sauke ina fadin.
Ni inna banwa kowa kitso a barni inji da abinda yake damuna sai naga inna tayi murmushi tana kaiwa zaune gefen gadon famekan ta.
Tace ai dama haka ake son a ganki cikin kuntatawa da damuwa sai bukatan lantana da umma ya biya idan sunga kina wanan takura dama abinda ake so ke nan damu.
Shiru nayi ina nazarin maganan inna da bata kara dora wani lafazi ba bayan wanan data fada hawaye ne yadan biyo fuskana na share da sauri.
Don nasan ran innan mu ba zaiyi dadi ba itama don ban taba jin ta furta komai cikin zancen hanani zuwa makarantar ba sai yau da tayi