Showing 162001 words to 165000 words out of 191310 words
Chapter 55 - ABU CIKIN DUHU BY MAKAWA By abooks.com.ng.txt
yakai ina ganin abin kamar a zahiri a idona don irin kallon da yake min a lokacin.
Jafar da tun safe hankalin shi na ga ya sake kiran Fadila yaji ya jikin nawa saidai kuma aiki yai masa yawa yau din sai dare ya samu kansa yana hutawa a gidan sa.
Wayan shi dake gefene ya dauki kara ya dan dago yana kallin wayan da mamaki don gani mamice ke kiran shi a lokacin.
Duk da yasan a can Nigeria yanzu akwai sauran lokaci dare bai wani yi ba a can ya dauki wayan kafin kiran ya katse mai.
Da sallama a bakin shi ya daga wayan tare da mika mata gaisuwa a cikin girmamawa kagin ta furta dalilin kiran nata garshi.
Ba tare data amsa mashi ba take fadin Jafar wai me kake son mayar da kanka a cikin kune ?
Duban wayan dake hannun shi yayi cike da mamaki kalamin mami din yana fadin mami nayi wani laifi ne yanzu kuma ?
Au baka ma san da kayi min ba daidai ba ke nan ashe har yanzu kana nan da zancen yarinyar nan zainab har wata can wai kanwarta tana kokarin cusa kanta gun yaran nan a school din su.
To kayi gagawan yiwa zainab da duk wani nata iyaka da zuri,ata a garin nan tunkan ranku gaba daya ya gama baci gareni.
Jafar din ya kasa gane me mami take fada don haka ya natsu da kyau yana gyara zaman shi do n kara fahinrar inda zancen nata ya dosa dashi.
Idan kana son kanka da lafiya na fada ma ka sallami yarinyar nan zainab tun kan raina ya gama baci dakai a gidan nan.
What mami ya fada dan jin abinda ta fada a kan zainab din wace ke matsayin mata a gareshi duk da yasan auren bawai wani abu ya daukeshi ba shima.
Yace mami amma kinsan akwai aure ai a tsakanin mu dan haka babu zancen saki a tare damu mami kinsan da hakan.
Jafar ni kake fadawa akwai aure a tsakanin ku in yarda tunda nasan baka fito ta inda ya kamata ace zan yarda da hakan ba.
Kamar yadda na aurar da dan uwanka a inda nake so haka kaima nake da burin maka aure na gata kowa ya san da zancen.
Bazan taba amincewa da wanan aure naka ba na fadama gata da daraja kamar ko wani da zan ma a kasan nan ban yarda da auren da zaka sa mutane su kalle da ban san komai ba.
To wallahi kaji na fadama koda wasa na kara jin zancen wanan yarinyar ya fito a bakin ka gabana saina bata maka rai fiye da yadda bakai tsamani ba.
Dan haka na gargade ka da ka ja mata kunne akan yayan gida dan karsu kara nuna sun sansu ko a ina ne kuwa.
Jafar din dake jin zancen mami din kamar al,amara dan ya shiryawa hakan ko wani lokaci yace.
Mami za a kiyayye ba zasu kara shiga harkan diyan ki ba ko jikokin ki insha Allahu zan tsawara masu kan hakan.
Har ta gama fadan ta sai hakkuri yake bata ranshi idan yai dubu ya gama baci da hakan don shi sam baiga abin fadan mami ba a nan.
Aikin da baiyi ba ke nan dan gaba daya ranshi ya gama baci da zancen mami din a hankali idanun shi suka soma sauya launi.
Ya dinga jin zuciyar tana masa radadi da zogi ya mike zaune game da dafe kanshi tare da sake wani irin huci mai zafi lokaci guda.
Ba shakka har idan ya yarda da abinda mami din su keso a gare shi komai zai iya faruwa dashi a karshe.
Don haka ya zama wajibi garshi ya jawa zainab kunne kan duk wani abinda ya shafi mami dawani nata .
Saidai kuma ta yaya zaiga laifi zainab di bayan tana gida kwance bata da lafiya a inama ta fita har taga wani da mami ke wanan maganan haka wai.
Shi a rayuwan shi ya rasa gane dalilin wanan kiyayyan da mami takewa wanan yarinyar da bata san komai ba a game dashi.
Idan ma taimako ne ai ita zainab din ta taimaka amma son zuciya ya rufewa mami din ido ta kasa gane hakan ta ko ina saboda wani dalili nata can na daban.
Ba shakka son zuciyar mami din yayi yawa ga wanan magana data kasa hakkura da jerabawan ubangiji a gare shi .
Don haka ya zama dole ya nunawa duniya yarinyar nan tana zaman matar shine da kowa ya kamata ya sanda hakan yanzu .
Ba zai damu da wani ra,ayi ko son kai da mami ke shirin nunawa ba a nan don sam yarinyar bata da laifi asalima ai laifin nasa ne gaba daya bana yar mutane da ya jefa a tsaka mai wuya ba.
Duk da yasan da ita kanta zainan din idan hankalinta yazo ta mallaki hankalin kanta akwai kalubali mai yawa a gaban shi.
Wanda yasan kafin lokacin zai iya magace komai a tare dashi da duniya ba zata zargeshi ba kan hakan.
Wanan wani damane ya samu da zaiyi amfani dashi don kawai ya fitar da kanshi daga wani tarko da mami ke shirin dana mai wanda zai dawo ya damesu gaba daya.
Da kyat ya tashi ya iya kulle kofan shi do baya bukatan kowa ya dameshi a wanan lokacin yana da bukatan ya kebe kanshi shi kadai ko zai samu natsuwa a wana lokacin.
Zazzabi mai zafine ya rufe shi a wanan lokaci tare da dumbin damuwa a zuciyar shi tabbas da mami tasan koshi waye ba zata tsaya tana fada akan shi ba.
Da mami ita kanta ba zata yarda ya auri yarta da ta dauko amana ya gani a gaban ta har yaga dacewan ta da wanan dama nasa ba ya kulla alakan aure da ita.
Wani iri yake jin kanshi a lokaci daya ga azaben ciwon kai dake damun sa ga matsanacin kasala gaba daya ya rufe shi a lokaci guda sai yake jin duk zaman garin ma ya fita mai a rai tankar ana hura masa wuta a jikin shi.
Wani irin nadama da dana sanin biyewa abokai na kurciya ya kamashi a lokaci daya a haka har gari ya waye mai duk da bugun kofan da yake ji ana masa baisa ya bude kofan nasa ba a lokacin.
Kwana biyu ya dauka a gida bai fita ba don yanayin jikin nasa da yake ji wanda ba komai ya haddasa masa hakan ba sai tsananin samuwa da halin da yake ciki.
Ya mamud ne da ya sha kiran shi a waya ana fada masa yana barci har yakai ga fahintar dan uwan nasa baida lafiya ya samu mami da zancen.
Da farko mami bata tayar da hankalin ta ba saida sukai waya da babban yaron shi yake fada mata yadda jikin ogan nasu ya tsananta a lokacin hankalinta ya tashi.
Da kyar ta samu aka sadasu a waya dashi take fadi a cikin tsigar lalashi jafar baka da lafiya baka kira gida ka fadi.
Yanayin yadda yake magana ya kara sa mami a cikin damuwa ta kara kwantar da murya gareshi tana fadin meke damun ka hakane friend ?
Mami kirji na da zuciyana kamar zasu fashe nake jin su ina jin zuciyana kamar an daure min shi gaba daya na rasa abinda yake damuna.
Mami tace kayi hakkuri ka daure kuje asibiti dukkan al,amari ubangiji yasan dashi ka daina saka aiki ko wani damuwa a zuciyar ka hakan nan.
A haka mami ta samu ta rarashi dan lelelen nata har dai yaji zuciyar shi yadan sausauta mashi daga irin kuncin da yake jin kansa a ciki lokaci guda.
A bangaren mu kuwa bamu san wainar da ake toyawa ba iyaka dai anty fadila ta kasa samun shi a waya.
Tun hakan yana damun ta har takai ga furta min cewa kwana biyu fa bata samun oga a waya idan ta kirasa.
A cikkn rashin ko in kula nake fadin anty isan ya damu ai shi da kansa zai kiramu yaji lafiyan mu wata kila aikine yai masa yawa.
Kai ta gyada min alaman a,a zainab raina yana ban ba lafiya dai sai dai duk abinda ake ciki zan barshi zuwa gobe ko jibi idan bai kiraba zan nemi abokin sa na nan muji ko lafiya yake a can.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
5️⃣0️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
YAR UWA IDAN KIN GANI KARKI KARANTA IDAN BAKI BIYANI HAKKINA BA NA FITAR MAKI DA HAKKI NA FADA LITTAFIN KUDINE DON ALLAH, , , ,
Kina jina malam ya fada na amsa a sanyayye da ina ji malam kada kisa damuwa ko kadan a wanan mafalkin naki don har gobe haske na gaban duhu.
Matuka kina rike da ayar Allah a tare dake babu wani shedani ko wani mahulunkin da zaiyi galaba a kanki face sai in hakan mukaddarine daga Allah dama yana a cikin kaddaran ki.
A iya binciken da nayi na gano wanan mutum wani shedanine dake tare da mijin ki a kullun wanda ya sha alwashin ganin bayan duk wata macen da zata rabi mijin naki.
Ba akanki kawai yake shedan shi ba duk wata mace hatta uwar data haifeshi da zai iya sai yayi sanadin raba alakan shi da ita.
Saidai a garemu wanan abin matukar zaki rike adduan dana baki kafin kuzo wanda shi din makamine dama ga mumuni ga bayin da suke mika al,amarin su gurin ubangijin su koda yaushe.
Malam shidin ba mutum bane kamar yadda nake yawan ganin sa a mafalki ko na tambaya a cikin sanyin murya da damuwa.
Murmushi naji malam din yayi tare da fadin a buncike na dai shi din mutum ne kamar kowa saidai shedanin gaske ne na kwarai.
Hasbunallahu wani imal wakil na fada a sanyaye tare da sauke ajiyan zuciya don tsoro da fargaban da ya ziyarci zuciyana a lokaci daya naji malam din yace.
Saidai abinda nake so dake Abu shine ki kwantar da hankalin ki da sannu zaki fahinci waye shi wanan mutum din cikin masu alaka da mijin naki.
Shi mutum masheranci ba kasafai kake saurin gane shidin makashin ka bane sai idan ka kwantar da hankalinka a sannu zaka fahinci duk wani mai binka da sheri a doron kasa ko ta wurin maganan sa ko yanayin kallom sa gareka da dai sauran su.
Mun dauki lokaci tare da malam yana kawo min ayan Allah da hadisai har saids hankalina ya kwanta naji duk tsoron dake raina a lokacin yana gushe min a lokaci guda.
Bayan sallama da malam din na koma gaban gado na zauna da wayan a hannuna na fara tunane wanan wani sabon kaddarane kuma ke shirin tunkaroni a yanzu.
Ina zaune ashe hawaye na zubo min ban sani ba sai jin muryan anty fadila nayi a kaina tana fadin me kuma ya faru haka zainab ke kadai a daki zaune kina hawaye haka ?
Kaina dago ina sauke sanyayyen ajiyan zuciya ina kare mata kallo tana tsaye da wani leda a hannunta fari ta karaso shigowa cikkn dakin tana maimaita tambayan ta a gareni lokaci guda.
Meya farune kuma don nasan ba zaki zauna haka kawai kina zubar da hawaye haka ba ke kadai a daki zainab ?
Ki saki ranki dani wallahi na fada maki ni mai taimakon kine ko da yaushe zainab don ciwon ya mace na mace ne yar uwanta ko kuma zancen fadan da mijinki yayi min ne ya sakaki wanan kuka yanzu ?
Kaina girgiza ina kokarin kakaro murmushin dole a fuskana kada ta dauka wani abu nake boye mata haka don ban da niyar fada mata wanan sirin nawa.
Nace anty ba komai bane kawai tunanen makoma na a gidan nan nakeyi sai hawaye yake zubo min ban sani ba ina kokarin share hawayen dake fuskana din.
Dafani tayi tana fadin kinga irin mazan ku dama tsada sukeyi koga matayen auren su idan kinga mutum da kyau ga ilimi ga dukiya uwa uba wayewa lamarin shi gaskiya sai a hankali dama.
Nasha fada maki ba sanya zakiyi ba saifa kin dage zainab a wanan zaman naku kada ki damu da duk wani hali da yake nuna maki a yanzu .
A sannu a hankali komai zai daidaita a tsakanin ku ke barin fada maki gaskiya daga yan mata har manyan matan barikin garin nan.
Duk idon su akan irin mazajen nan suke ko yaushe burin duk wata mace a yanzu shine ta samu gidan hutu irin wanan ta yadda zata shiga tsara ta nunawa duniya ita watace a gari abin kwatance.
Ke bari ma dai in maki na mahaukaci ai yanzu idan kayi sa,a ka damki namiji kada kayi sakaci dakoma wayeshi kama abinki ki damke ta yadda matan waje zasu gane ayya yana gaba da tsakuwa wurin taunawa.
Don haka kama jiki kafin yazo ki nuna mai ke yanzu ba da bane a gurin ki kinsan kanki kinsan ajin ki ta yadda zaiji shayin yi maki wani iskancin su na maza can.
Dago kai nayi da sauri ina kallon ta don jin abinda ta fada ni ta yaya zanwa mutum kamar ya jafar wani sallo ko kissa can har yasan ni din mace ce ta fada a duniya.
Tace kina mamaki ko zainab zakice nace maki lokacin da zaki kama shi a hannun ki kina juyawa yadda kike son abinki da kowa zaiji a ransa dama ace shine a matsayin ki a lokacin .
Jin abinda ta fada yasani sauke wani irin ajiyan zuciya mai dan karfi don jin zancen ta nakeyi kamar almara a kunnuwa na.
Har yaushe hakan zai faru da take ta fada a gareni ni din da ban ko gama sanin matsayina ba a zuciyar shi har take min hasashen hakan yanzu.
Kina da kyau da zaki sace duk wani zuciyan da namiji zainab irin kiran ki maza da yawa suke so a rayuwan su saidai in hakan bai samu garesu ba dai.
Kin koga yadda kika koma a cikkn kan kanin lokaci zainab yanzu wasu kayan ne na sayo maki irin wanda ya kamata mace na sakawa a cikin gidanta don jan hankalin mijin ta ba yanzu zaki amfani da wanan kayan ba sai lokacin da mijin ki ya dira a kasan nan.
Dan murmushin yake na sake mata a fuskana kawai ta fara daga kayan har kala biyar babu wanda zan iya fita ko falon gidan dasu a ganina balle wai gaban shi ya Jafar din da take nufi.
Godiya nayi mata a fili a zuciyana kuma fadi nake Allah ya sauwaka min sakace wata karuwa can riguna haka duk a bude kamar rigan turawa marasa tarbiya.
Zai maki kyau sosai ta fada tana kara dagasu tare da fadin ina gani su naga sun dace dake sosai yasa na sayosu tunda akwai kudi a hannuna.
Nagode na kara fada a cikkn kulawa da nuna girmamawa a gareta kuma na kula da hakan yayi mata dadi sosai ta mike tana fadin don Allah ki saki ranki na fada maki saifa kin jajirce sosai ba a sanya a harkan aure.
Kwana biyun nan nikan na mayar da hankalina a wurin addua ne sosai da kai kukana gun ubangijina Allah kuma sai nake jin natsuwa da kwanciyan hankali yana kara shigana ko wani lokaci.
Hakama maizube na kula da tana tayani da addua don itama tana bata lokaci sosai wurin fadawa Allah al,amarin mu.
Falon gidan muke zaune bayan sallah la,asar wanan ya zama muna kamar dabia a gudan a wanan lokacin mukan hadu nan mu dinga fira da juna ana dariya.
Wanda hakan kan min dadin a rayuwana har in manta da wani abu a tare dani gashi a sannu ina matawa da tsoron mami a cikin zuciyana.
Saidai tunanen hjy da kewan ta har yanzu yana nan daram zaune a raina don tsohuwar ba abun mantawa bane a rayuwana don jinta nake kamar itace Asabe kakata a guna.
Yun hadarin yamma ya zama kamar al,ada a garin abuja din haka yanzu ko an hada bai faye damuwan mu ba kamar farko.
Da wandone baki irin na mata mai dane jiki a jkina iyakarshi idon kafana hakan yasa santala santalan kafana fitowa fili gasu fari sol dasu don tsaban samun dadin da nake ji yanzu tare da rashin wani aiki da banayi a yanzu yasa kafan ya kara min haske sosai.
Sai dan riga irin na mata dake dan bude daga kafadunshi zuwa iya gwiwana mai launin kalar kampala jikin rigan wanda ya dauki kalar jikina da kyau.
Sai hula dana saka a kaina mai ribon ta baya ya gashina dana daure yasa yadan dago ya kara min kyau.
Wanan duk aikin anty fadilace wace