Showing 69001 words to 72000 words out of 191310 words

Chapter 24 - ABU CIKIN DUHU BY MAKAWA By abooks.com.ng.txt

son lantana yazo ya nemeta da aure ko za,a dace ta haifa mai diya maza a gidan.
Bayan auren yanzu kuma ya fita a tsakanin su suka koma kamar annabi da kafiri tun bayan dataga ta haifi namiji din duk da dan ba lafiyayye bane yazo.
Innan mu tana bakin murhu tana hura wuta ta fito ta zauna a kofan dakin ta tana fadi a fakace.
Yau kuma su oo me aka samu da farar safiyan nan ake wanan duke a gaban murhu ko anyo aikene daga bariki za a sha dadi haka ?
Inna dai yi tayi kamar bata jita ba taci gaba da fadin muna nan dai idan tayi wari maji ai .
Gashi dama ko a gida a shedesu da dan hannu balle anje birni anga banza aita wawurowa ana kawowa gida.
Hakan bai mata ba ta sake fadin wasu dai sunji takaici ya ko auren fari babu har ta shiga duniya yawon banza .
Har azo anawa mutane feleke a gari a saka a canza duk da kayan zina to ai haka ba mamaki tunda tsohuwa ma ta tsufa bata san ta tsufa ba ka jaraba kullun ana makale da naji ana abu daya diya tayi da kaitai a birni uwa tayi nan da tsoho.
Allah sarki dadin abun dai da tsohon sunna tsohuwar ke makale ba mazan wasu take ci ba a titi kamar macijiyar da bata ramin kanta.
Sai dai anyi rami tayi shige ko tabi darnin makwabta ana dannan ta ana sukawa akanta saman titi da tsufanta diyata dana makwabta suna kallo.
Innalillahi aikuwa dama inna takan tara mata na kwanaki kafin ta gaji ta bata amsa koshi sai idan taji ta tabo zancen diyan tane zata samu mai zafi daya ta fada mata taja bakinta tayi shiru ta barta tana haushi.
Wani lokacin har makwabta sai sun shigo rabon ta akan tayi hakkuri ta daina idan kuma sun gaji sai tayi tayi sai ta gaji zata kyale don kanta.
Wani lokaci kuma har uwarta takan tako gidan tazo taya ta fadan suyi harsu kare babu mai tankasu.
Yau din ma da taga haka jin amsan da inna ta bata ta yafa gyalenta ta fita zuwa fadawa uwarta abinda ke faruwa harda karya da gaskiya ta kwasa ta fadamata.
Sai gasu tare sun dawo ita haushi uwarta haushi Allah ya taimaka inna ta gama girka dan taliyan hausa da take dafawa yara su karya dashi din Abba yace kuntu billahi baida ko kwandala a hannun shi da zasu karya.
Amma yana fita ya shiga dakin lantana data haushi da masifan ai ta ganshi ya shiga ban daki daga yau sai ka koma ka mannewa tsohuwar matar ka tunda duk kokarin da nake maka baka gani kai.
Halin maza sai su nan Abba ya dan fara kame kame yana rarashinta har yakai ya dauko dan kudin daya kwana dashi hannun shi ya mika mata su gaba daya don kawai ya samu ya shawo kanta kada ta gujeshi kamar yadda ta fada din.
Shine bayan fitan shi inna ta fito tana hura wuta ta ja inna da wanan masifan har yakai inna ta mayat mata da martanin da yai mata zafi shine uwarta ta shigo da masifa.
Tana fadin sai tayi karan innan mu don kazafi wai inna tayi mata a cewan ta jin fitinan yayi yawa yasa Asabe fitowa don da farko batayi niyar fitowa ba.
Ji datayi tace zata kai karan inna ga hukuma yasa ta fito tana fadin ke mai tuwo baki tunanen me yarki itama ta fada mata .
Har ta bata wanan amsa itama don haka kawai ba zata fada mata ba ai don kawai an mayar da haulatu mai hakuri a gidan tana kawar da kai ga abinda yarki jeyi mata ko yaushe.
To tsohuwar banza kin fito ki shigar matane ko me yanzy haulatun ce mutum a wurun ki tunda yarta na can birni tana bin maza tana zuwa maku nan da abin duniya yanzu sun koma abin son ki kuma ?
Jin haka da innan mu tayi ta bude labulen kofan ta tana fadin saukin abindai kafin ta fara aikatau wasu sun tafi butnin sunyi har saudiya yin dandin kasa mai tsarki basu dawo da komai ba kasan nan sai tsaraban shegu.
Idan kuma suna da uba yau a fito muna da uban su mu gani don haka kafin yata taje birni bin maza tsohuwar banza ta fara zuwa ta dawo muna garin nan da tsaraban annoba.
Yau zaki san kin tabani garin nan yau zan nuna maki ko wacece ni a garin nan inna tace idan kin tashi kisa a rufeni dan makullin ya bace iyaka ke nan.
Lokacin har yara da mata da muke makwabtaka dasu sun cika gidan suna kallo da saurare.
In dai barikin ne ai iyawace don karshe sai an koro yar taki da ciki kowa ya gani a garin nan lantana ta fada cikin jin kunya da nauyin yaran dake ihu bayan fitar uwarta don halin su ya ishe mutanen unguwa dama.
Har wurin aikin Abban mu lantana da uwarta suka sameshi suna fadin sai sunyi karan innar mu don tayi masu kazafi da cin mutuncin da ba a taba masu shiba yau.
Abba ya shiga ba mahaifiyar lantana hakkuri yana fadin ta barshi da inna dama halin innan mu yakai mashi ko ina a gidan.
Haka dai Abba ya samu ya lalaba su suka bar gidan bai dade ba shima a waje sai gashi ya shigo yana kwalawa inna dake bandaki kira .
Bata amsa ba saida ta fito ta bayan shi take fadin gata ai tana sauraren shi.
Ke don baki da mutunci yanzu har kika iya bude baki kika zagi uwar lantana a gaban ta karya suka fada wayasan inda yar taki take a birni dama.
Allah sarki hakane dama ai na sani kaima yaran ba damuwan ka sukayi ba ai tunda tun lokacin daka mikata wurin yar uwarka har yau baka taba bin bayanta kaga inda take zaune ba don an hanaka zuwa gani don a samu abun fada min.
To bari kaji malam idan ku dakai da uwar matan naka bakuyi karana ba yau ni zanyi naka a garin nan duk inda kakai min ya sai ka fito min da ita don wanan abin ya isheni.
Ni ga Allah na dogara nasan irin tarbiyan dana ba diyana don bata gaji shashanci ba a gurina balle taje tayi shashanci a birni.
Yanasu yau ke da bakin kike fadin zakiyi karana kan yar cikina a mata ya baci inna tace kwarai kuwa bello ta fadi sunan Abba ba sakaye kamar yadda take kiranshi da malam.
Mamaki ya kara kashe abba jin abindata fada sunan shi gatsau haka babu sakaye data sabayi mai don gabadaya ta birkice masu a gidan.
Wani kalon kalo suka watsawa juna kafin Abba ya kuta yana fita daga gidan inda lanta taji haushi cikin daga murya take fadin tunda har kika zageni dani da iyayyena ke kuwa sai yar taki tayo abin kunya birni an korota ta dawo maki maga ta tsiya.

Nikan unda na shige daki nabar mami na fada a falo ban fito ba sai bayan sallah isha,i koshi din abinci na fito.
A falo gaba dayan su suke in ka debe mazan da basu rigada sun shigo gidan bako a lokacin don ko hjy a falon tayi sallah bata shigo dakin tayi ba nasan saboda tafiyan ne yasa ta zauna a nan bata dawo dakin tayi sallah ba.
Banda hara ba abindaya shiga tsakanina dasu Rufaida duk da na gashesu a cikin jam,i saidai su basu amsa min ba.
Sai hjy ce ke fadin yarnan yanzu nake zancen ki a raina ina batun aje a dubo min ke a daki ko lafiya kika shige har wanan lokacin ?
Ina zancen dai ai ya wuce tunda kinji uwar ku ta tsawata kan hakan suma kina ganin su da shegen son jiki suke ta yaya zaki dauki kayan kasan ki har kiba wata wanki can.
Haba haba hjy a daina wanan zancen tunda mami tayi mana fada a kanshi dazu ba wanda zai kara bata irin wanan aikin acikkn mu ai tunda mami ta hana abata Aisha ke fadi.
To uwata hanani in fadi tunda kun shuka rashin gaskiya wa yarinya baku son a fada kuma kai kuma dai kazamai ne wallahi.
Ta fada rai a bace tana mai kawar da kanta ga kallon su sukai tsuru tsuru don mami na falon itama ta kafesu da idanu.
Rufaida na shirin mikewa tabar falon don takai kololuwar cika tana batsewa wai akan yar aiki mami tana wullakantasu don kawai taga gidanta ne yanzu dan uwan mahaifin su ya rasu yasa ake masu hakan.
Batakai ga tashi ba taji sallaman jalal yana washe baki ya shigo da ledoji niki niki a hannayen shi yakai gaban mami ya aje lodojin yana zama a kujera tare da fadin.
Wassh Allah yau na gaji da yawa mami tace da kai me ke nan fa mami tunda aka fito daga sallah yaya jack , , , ,
Bai karasa fadi ba saboda hararan da mami ta watsa mai yasan me take hararan shi dashi yace a wani yanayi i am sorry mami na mantane kin hana mu kirasa hakan ni kuma bakina ya saba da hakan tun a can.
Rufamin baki ku kun fada inagana waje jalal ka fita min a ido duk kuka bari wanan sunan ya shigo kasan nan raku saiya baci sosai.
Yana dariya yace yanzu dai mami ba wanan ba kinga ledan nan wai duk na tsohuwar nan ne yaya ya ban kudi a hado mata wai kada taci abinci da dare sai wanan din shi ya dauka nan irin can ne da tsofi sukecin wanan dadin yana magana yana zamowa daga saman kujeran yana kokarin budan ledan.
Wanan ya hana rufaida dake cika tana batsewa tashi don tun shigowan shi falon ya dume da kamahin suya irin na yan gayu ba suya na gida ba wanda yasha kayan hadin sanadarin zamani.
Hannun shi mami ta buge ya jaye yana fadin wassh Allah mami zan bude ku gani ne ai ko ya fada yana dariya.
Mikawa hjy abinta babu maici a cikin ku wurin sai idan ta gama ta baku ragowa idan zaku ci.
Haba mami ta bamu ragowan ta kuma bayan ta gama zuba mai miyau da goro zamuci salma ta fada tana kallon mami din.
Hjy da sai yanzu ta fahinci me ake nufi lokacin da mami ke kallon jalal tana fadin ya mikamata take fadin au me muka samu ne wai.
Bakiji bane hjy wai Jafar ne yasa a sayo maki wanan shine syke son su saka maki rani a ciki don suna yan kwadai.
Ja,irin miskili ya gama babautan nasa yana neman shiri danine kuma yanzu dazun fa ya gama fadin me na biyo ku yi nan nazo in sakawa mutane nauyina sai gashi shiya fara daukan nauyin kuma ?
Haka kika fada ko bari ya dawo saina fada mai wai badan Allah ya saya maki ba neman shiri dake yake ya sayo maki.
Kaji ja,ira zaki hadani fada da wanan mai kama da yan ruwa yazo ya hanani shanruwa a gidan nan ke nan.
Ya jalal yaga sun tsaya surutu mami bata sab sanda ya jawo ledan ba yana fadin bari nidai na bude don inyai sanyi bana iya cinsa kuma.
Yana bude ledan farko wani kanshi ne duk ya game wurin leda daya ya tura a gaban yan mata yana fadin ku ku dau wanan wanan kuma hjy wanan nasu ne idan sun shigo.
Ya mike ya isa gaban tsohuwar tare da ledojin a hannun shi yana fadin hjy mu muci wanan ko tace kaidawa ke nan miko min nan dagani sai yar nan da take dawainiya dani zancisa.
Kaji hjy kuma ya wuce ki bata fifike ne a ciki kilama bata taba cin suya irin wanan ba ai Nazira ta fada a daidai lokacin da suke shigowa gidan shida Jamal.
Yau kan ya wanke kanshi a wurin tsohuwar da murna da lale marhabin ta tare shi tana fadin kaga mijin arziki wanda yasan zafin iyalin shi.
Mami na masu dariya yazo gaban mami ya dan dukar da kanshi wanda kamar hakan al,adan yayan mami ne don har ya mamud haka yake mata da girman sa in zai fita ko ya shigo zai duka mami ta ahafa kansu tana saka masu albarka tare da fatan alheri a garesu.
Don tun ina mamakin hakan har nagaji don na saba da ganin hakan wurin yayan gidan maza ko Aisha da take mace kamar zata koma cikin uwar wani lokaci idan abin ya motsa mata ko yanzu tana zaune tunda tai magana da farko bata kara magana ba a wurin kowan su nakan waya suna abu daya charting ko dawa soke yi oho ?
My friend an dawo ke nan mami ta fada tana shafa kanshi tare da fadin ubangiji yayi maku albarka ya kare mun ku a duk inda kuka saka kafanku.
Tashi yayi ya nufi wurin hjy ya zauna a kasan carpet tare da riko hannun da ta dauki cinyar kaza tana ci yakai a bakin shi ya gutsura kadan kafin ya kai mata itama a bakinta .
Ni dai ina gefe zaune a kasa daga gefen hjyn ina kallon ikon Allah tare da mamin wai yan gidan mami suke kwadayin nama haka ?
Wanda nama sai an mayar da saura kitchen don sunci ya ishesu wanan wani irin nama ne hakan don idan kaga mami ta sayo nama a waje to kilishi ne zata shigo dashi mai yawa kowa yaci har a ture saura su mama kande su dauka..
Dan albarka hjy ta fada tana hadiyan naman dayasa mata a bakinta ta gutsura kowa falon na busy suna cin naman suke gaidashi dashi.
Dabi,an shine kyaluwa dan haka yi yayi kamar baiji su ba hjy ta juyo tana fadin taso mana yar nan ki diba kinyi zaune kina kallon kowa nacin abin arziki.
Saiya dan juyo ya kalleni guri da nake zaune din ya kawar da kanshi kamar ba kowa a wurin .
Na mike nazo gaban hjy din yana zaune har lokacin yayi rigingine a wurin kafanta idon shi a carpet nakai hannu zan diba Nazira tace
Ke dakata don Allah menene haka zaki saka mata wanan hannun naki mai dauda a cikin abu haka kai tsaye ba tare da kin wanke hannu ba.
Cak na tsaya daga daukan naman da nasoyi din ina kokarin mikewa a inda nake gurfane don barin wurin.
Ke diba ki wuce ya fada batare daya dago kai ya kalli kowa a wurun ba ya fadi hakan sai jamal yake fadin haba Nazira ku daina irin hakan don Allah dai.
Bazasu bari ba don da zasu bari ko ance suyi wani abu kan yarinyar nan ai basuyi ba kuma yadda nayi masu yau.
Me ake mata idan ba iya yinta ba taga yan aiki a wurin nan ne ko taga su kande na zama a cikin mune haka su ?
Nazira zan saba maki a gidan nan fiye da tsamanin ki to bari kiji zeey da kike gani daya kuke da ita a gidan nan yadda na daukeku dasu Aisha haka itama nake daukanta don ba wai aikin kudi aka kawota yiba yadda kuke tsammani.
Rokota nayi gurin iyayyen ta suka taimaka min suka ban ita a cikin mutunci sau nawa wai kuke son in fada maku hakane wai ?
Look akan yarinyar nan zan sabawa yarinya a cikin gidan nan ko wacece me yarinyar nan ta tsare makune wai haka kuke sakata a gaba ko yaushe ya fada a hasale cikin daga muryan shi dasai ranshi ya baci akejin shi irin hakan.
May be don sunga ta fisu kyaune da tsari suke kyashin ta jalal sarkin barkwanci ya fada kai tsaye yana masu dariyan kyaita.
Kai amma jalal din din don Allah kada tasa taji dadi har taji dadin raina mutane a gidan nan ta dauka wani kyaune da ita.
Garin dauko naman saboda rawan da jikina keyi na dauko gefen fifiken kazan dayasha carbej da albasa dasu maggi curry da sauran hadi namike tsohuwar na fadin baki dauki abin kwarai ba nace wanan yayi min yanzu naci abinci na bar falon ga baki daya har lokacin jamal da jalal suna cacakan ya matan a kaina.
Jalal ke fadin wanan kina ganita idan tayi clean gidan nan ma baya daukanta ke zeey fa idan ta waye ba karamar classic lady bace wurin nan.
Dakin na shiga na aje naman don naji ya fita min a rai don disganin da nazira tayi wurin daukan naman a gaban kowa.
Nima fa mutum ce kamar kowa da suke min haka don kawai ina yar kauye kuma diyar tallaka tallakama mai faci.

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login