Showing 141001 words to 144000 words out of 191310 words
Chapter 48 - ABU CIKIN DUHU BY MAKAWA By abooks.com.ng.txt
gidan wa ke nan wallahi wai ashe tana gidan hjy Tantano duk wanan neman da ake mata.
Wani ajiyan zuciya mami ta sauke kafin tace da wanan yarinyar suke ke nan ko ?
Wace yarjnyar Ramatu ta tambaya kafin tace au nagane ba tare suke ba gaskiya ita kadaice da kayan ta yanzu aka sauketa gida masu shi basu ko zauna ba wai suna saurine.
Guntun murmushi mami ta sake a fuskan ta tare da ajiyan zuciya tace Ramatu yanzun na yarda da ake fadin jika yafi da dadi wallahi wanan abinda hjy tayi min akan yaran nan.
Anywhere zan kira in an jima ki ban hjy din muyi magana tunda yanzu nasan mutanene a tare da ita ina fatan dai baki bari kowa yasan da wanan zancen ai.
Haba dai antyn mu tayaya zan dabawa cikina yuka da kaina kan wanan magana ai wanan ba abin bari na waje yaji bane ace hjy tayi fushi dake tabar maki gida har baki san inda take ba tsawon kwanaki haka.
Bari kedai Ramatu ko wa yan nan dake tare dani ai ban bari sun fahinci yaya kan zancen yake ba sam kinga min yar iskan yarinya zata ja a bagani a bangon jaridan kasan nan don tsiya.
Dariya mama Ramatu ta kwashe dashi tana fadin ai sai dai kada a kara amma wanan yarinyar ta rigada ta cuci mu saidai kawai a dauki mataki don gaba kuma.
Mataki kan kamar na dauka Ramatu don gaba dayab su saina nuna masu kuren su har shi jafar din ina binshi a sannu ne yanzu in samu akaiga auren nan shi da yar gurin saudat.
Har yanzu zancen yana nan ke nan da kawai ki barshi ai daga baya zao gane irin gatan da kike so kimai idan yaga matsiyatan daya jawo a jikin shi suna batun rufeshi da bani bani.
Barni da mara hankali mami ta fada tana maijin zafi a zuciyar ta kan abinda yar uwanta ta fada yanzu.
Bayan ta kashe wayan idanunta ya dade a runtse tana tunane kafin ta mike zubur kamar ta tuna da wani abu a lokacin.
Ficewata da dan sauri zuwa part din dan nata jafar har tana hada kafa a wurin sauri lokaci guda .
Tayi sa,a tana murda kofan taji shi a bude bata tsaya jiran wani abu ba ta afka ciki part din kai tsaye da sallama.
Yana zaune saman kujera sai farar takarda dake nade a hannun shi ya duka yana zukan farin garin dake saman dayan farar takardan dake aje saman table.
Wani irin ja tayi baya kamar zata fadi lokaci guda kuma tabi bangon dakin tana dafa a habkali don yai mata makari daga inda take tsaye.
Saida ta dafa bango ta samu numfashita ya dan daidaita ta samu fadin Jafar sai kuma idon ta ya sauka akan wasu tarin kwayoyin dake watse a gefen shi.
Da wani irin rawan jiki mami ta ke nunashi da yatsan hannunta tana fadin Jafar yaushe ka fara wanan halin ban sani ba ?
Yadda take maganan kamar wacce ke gudun wani yaji abinda take fadi din a lokacin a hankali ya dago kai ya kalli mahaifiyar nasa yana fadin .
Mami kiyi hakkuri bansan zaki shigo a yanzu ba har na kai ga shan abinda zai kwantar minda hankali.
Idan naci gaba da zama haka ban samu abinda zai taimakawa kwakwalwata ba zan samu matsala sosai shiyasa na sha wanan a yanzu don ya dauke mi ragamar hankalina na dan lokaci zuwa yanzu.
Don ba zan iya jure ji da gajin yadda kike kokarin hanani abinda nakeso a rayuwana ba mami sai kuma ya mika mata hannu alaman dai ya fara fita hayaci shi a lokaci.
Kamar wawiya haka mami ta koma lokaci guda do haka tabi hannun nasa daya miko mata zuwa gare shi.
Don bata son ko cikin diyan ta wani ya riskeshi a wanan halin da ita ta riski dan nata a ciki.
A hannu kuera ta zauna ta tsura mai idanu yayin da nasa idanuwan suke kamar a lumshe duk da tasa ba barci yayi ba a lokacin.
Kanshi ta dauka zuwa cinyanta ta fara shafa a hankali take hawaye wani na bin wani suka fara sintiri a idanun ta lokaci guda.
Babu abinda ya fado mata a rai sai irin wasoncin daahaifi su yabar mata kafin bari shi duniya akan ta kula mai da tarbiyan diyan shi kamar yadda sharia ya sharadawa musulmai.
Mami hawaye wasu nabin wasu ta kasa controling din su tuni kanta gaba daya har jikin ta ya dauki canji lokaci guda ta rasa wani duniya take ciki a lokacin.
Wai yau jafar dinta ne haka dumu dumu ta kama shi yana wana dabia da tafi kyamata ga diyanta.
Ta rasa meke mata dadi a ranta gashi tana son fita ta koma dakinta ko zata samu ta fasa hawayen ta su samu zuba kasa ko zataji sanyin abinda takeji a ranta.
Gashi kuma tana tsoron fita a lokacin kada wani ya shigo part din bayanta ya same shi a wana halin ko kuma ganta a cikin wanan yanayin da take yanzu a tambaye ta dalili.
Asalima idan son samune daga ita sai shi idan ya farfado ta samu ta gargade shin sosai kan hakan don ya tsira da mutuncin shi a idon jama, a.
Jin mami ta zurfafa ga tunanen da takeyi ne yasa shi dan dago kai ya kalle ta a hankali ya ke fadin go back to your room mami.
Idan na tashi za shigo muyi magana dake anjima murya cikin rada mami ta sake fadin zan koma amma sai ka ban duk wanan abinda kake sha yanzu na fita dasu dakin nan hankalina zai kwanta.
Murmushi yayi yana dan mikewa daga zaune tare da fadin kiyi hakkuri mami nasan na bata maki saidai nima din ba hakan naso ba dani.
Nasani jafar yarinyar nan ta cuceni ta gama min da rayuwa jafar a sanadin ta yau jafar har shaye shaye ka koma yi haka.
Cikin wani iri kuzari ya dago yana kallonta fuska daure kafi yace mami idan ma cutane ai yarinyar aka cuta tunda ita zata zauna da mashayi irina yanzu.
Wani irin sauti gaba mami ya bada lokaci don ji abinda yake fada a cikin maye jiki babu karfi ta mike tare da aza kanshi saman filo tana fadin .
Ka kwanta da wanan shirmen da kakewa mutane a yanzu yanzun ba lokacin maganan komai bane.
Murya kasa kasa irin na wanda baya cikin hankalin shi a lokacin kamar mai shiri barci yace iam telling you mami itace muka zalinta, , , ,
ZAINAB IDRIS MAKAWA
🦅 ABU CIKIN DUHU SIRI NE 🦅
4️⃣2️⃣
ZAINAIBA IDRIS MAKAWA
ASSALAMU ALAIKUM YAN UWA DA FATAN KOWA NA LAFIYA UBANGJI YA BAMU HASKE GA AL,AMURAN MU AMI YA ALLAHU, , ,
YAR UWA LITTAFIN KUDINE KI TUNA HAKAN DON ALLAH KADA MU RIKE JUNA DANI DAKE DARI UKU NE KACAL SISTER TA BANK KO KATIN WAYA NAGODE, , ,
Kai duniya muji tsoron Allah wai mutane yanzu basa tunane ba a duniya za a tabbata ba zamu koma ga mahailicin mu Allah .
Amma saboda son kai sai kaga idon mutum ya rufe akan duniya ya manta da za a koma wurin ubangijin talikai ya dinga yin abinda ya ga dama.
Mami batai tunanen laifin daga gurin ta bane sai kokarin dora laifin abinda idon ta yagani akan dan nata yau takeyi a kaina.
Tana tunanen da badon ni ba da danta bai shiga wanan halin ba data sameshi a ciki don kawai wanan matsalan har yakai ga wai ya fara shaye shaye haka saboda idon ta ya gama rufewa a lokacin.
Ta dade kwance ita kadai a dakin kafin tayi karfin halin mikewa tsaye don zuwa gahatar da sallah la,asar da yayi tun dazun tun safe ta kasa kai komai a cikin ta har zuwa lokacin.
A Inda ta idar da sallah take zaune har lokacin tana cikin zulumi da tunane halin data riski dan nata a cikin .
Wayan dake gefen tane yake ta ringing ta kasa tashi ta dauka sai bin waya takeyi da idanuwa kawai a saman gadon.
Mami wayan kine fa ke ringing Aisha ta fada daga kofa tana shigowa daki lokacin idon ta akan mahaifiyar tasu dake zaune wurin da take sallah.
Dago kai tayi ta kalli yar nata a ciki wani irin yanayi na ban tausayi a gare ta da wanda ya ganta a lokacin dole ya fahinci bata a cikin hayacin ta.
Mami lafiya Aisha ta fada tare da kaiwa zaune a bakin gado tana kokarin daukowa uwar wayan dake kara saman gado.
Ajiyan zuciya ta sauke kafin tace duba min yayan ku idan ya dawo daga wurin aiki har ta mike tace ya mamud ke nufi mami kin yanzu bai dawo ba ai sai after six zai shigo.
Hannu biyu ta dauka ta dora a fuskan ta a cikin yanayin nuna takura a rayuwanta a lokacin sai kuma ta fashe da kuka mai tsuma zuciya da tashi hankali.
Take hankalu Aisha ya daga sai wanan lokacin ta fara nadaman rashin grany dinsu a tare dasu yanzu ina tasan zata dosa da wanan matsalan na uwar su da bata san abinda ke damun ta ba.
Mami Aisha ta fada a sanyayye mami lafiya meke faruwa ne wai dake barin duba idan ya j na gida na kira maki shi.
Karki soma ta fada a cikin wani murya mai nuna cikkaken umurni a gareta da sauri don tsoro ta koma ta zauna a inda ta tashi da farko.
Ido ta kurawa mahaifiyar tasu kamar tana nazarin ta kafin tayi karfin halin fadin mami koma meke damun ki kiyi hakkuri don Allah ki daina zubar da wanan hawayen haka.
Aisha will you believe da irin halin dana riski dan uwan ku yau a ciki koda yake barshi kawai bai dace ma in fada maki ba a yanzu.
Mami wani abin yayi kuma after all he has gone through na yin aure bai fada maki ba ko ya dauko zeey din ne zuwa gidan na kuma ?
Wani kallon takaici ta jefawa yar nata tare da mata gargadin ke yarinyace Aisha ta kawar da kanta ga kallon ta do takaici data kara bata na ambatan sunana a wurin.
Aisha ta dade a zaune tana kallon yanayin mahaifiyar tasu dake a cikin tashin hankalin data kasa gane dalilin hakan a yanzu.
Mikewa Aisha tayi daniyar barindakin dob ba zata juri ganin uwar a cikin wanan hali ba na bacin rai.
Sunanta mami ta ambata ba tare data dago kai a yadda take ba taci gaba da fadi kada ki fadawa kowa halinda kika sameni a yanzu.
Naji mami Aishan ta fada har ta soma tafiya taja ta tsaya tare da fadin but mami da sauri ta fara tafiya bayan hannu da uwar ta kara daga mata kuma.
Koda Abba ya dawo gida da dan ledan shi dayayo cefane din a dafawa hjy ya samu hjyn ta fito zasu tafi don azzarlazalan da ya jamal ke mata tafito kada su makara.
Af hjy wai tafiya zakiyi ne yanzu ga abin tabawa har na sayo a gyara maki kada kizo garin baki taba komai ba.
Cikk yar fara a da nuna jin dadin yadda ake kulata a gidan namu hjy tace ai yata ta gama ban komai yaushe rabona da nasha fura da nono haka mai dadi.
Ga kawata ta nuna Asabe bayan innar mu tana fadin ta kawo mi ganye shima na taba ko hakama aina gode.
Ta nunani tana fadin saidai ga matar jikana nan don Allah ina son a bata duk wani kulawan daya dace da ita don yanzu ita din ba abin wasa bane a guri kowa.
Kanne dakr gefe tsaye duk suka kalloni a lokaci daya don jin abinda hjy din ta fada akaina suna murmushi.
Nauyi da kunyane ya kamani lokaci guda muna gaba nan muka barta da Abba da innar mu da Asabe suna maganan abinda bansan kome suke fada ba a lokacin.
Muna tsaye a bakin mota tare dasu ya jamal duk da dai gaisuwa kawai mukayi dashi ya juya abinshi bai kara bi ta kan mu ba kuma.
Wanan fa mai kama da balarabe yayar mu amma dai bai iya hausa ba ko don naji hausan nasa kamar da turanci ya amsa mana.
Yayan mune ba bata amsa dashi batare da kara furta komai ba hankalina yana gun abinda suke tataunawa a kai.
Abba ya san fito ya bar hjy da innan mu sai can ta fito ta amemu a wurin motar hannu ta mika min na nufi wurinta don na gane abinda take nufi da hakan.
Dan rugumeni tayi kakar mai rada take fadin in kula da kaina zamuyi waya idan ta isa gida tana son in zama mai biyayya a duk yadda na riski kaina a ciki da mijina.
Nauyi da kunya ne suka dan rufeni saiga idanuwana suna dan ciciko da hawaye a lokacin guda kamar kada in rabu da tsohuwar muna kalo haka ta barmu a gurun suka tafi bayan alherin databi kowa dake wurin dashi na kudi.
Mun juya da zuman shiga gida muka tsinkayi muryan Abba da lantana har da innan mu da sauri muka karasa zuwa ciki don ganewa idon mu abinda ke guda.
Lantanace ta cikuwaikuye abban mu dake tare ta a dole sai ta karbi ladan da Abba yabawa inna mu a gyara min abinda ya sayo a yiwa hjy dan abin motsa baki.
Tunda na tunkaro wurin nayi arba dasu a halinda suke ciki na runtse idanuwana a hankali do abinda idona ya gane min .
Kai kai kai amma yar nan baki da albarka yanzun nan da bakin ma a gidan sai kinyi wanan saida halin da kika saba ashe.
Da badon mutane na sun tafi ba haka zaki barmu da abin fade a gidan nan saboda baki fitina irin naki.
Inna don Allah ki mika mata ko manene a daina wana fitina indai a kaina ne ake wanan abin na fada cikin dan marairaicewa inna mu din.
Ba ita kadaice mai bakin ci ba yau ina sin i gani idan na karfi ne tazo takwata tunda an fada mata mu bamu da hakki akan shi komai sai itace za a sayawa taci muna kallo.
Af don kin fadawa yarki tsoron karba zanyi ko me ni kunya ma kika ban ace wai yarka ta dawo yawon bariki haka tana haska gari har zaki tsaya fada kan wana dan ledan hannun ki.
Ina kwalayen da kaya dadin da aka saba zo maki dashi wanan karon ta kwabe ba a kawo din bane ko meye don naga kamar su dawo muka da gaiyan tsiyan ku gidane sun gaji da kwallon mangoro sun yar sun huta da kuda .
Inna mu dai bata sake ledan ba tayi daki dashi muka bita ga baki daya mu yan dakin namu saboda Abban mu dake wuri ya hana ai magana a lokacin.
Muna shiga daki akan kwalayen da aka jera a daki wanda lantana kewa gatse sa,adatu ta nufa tana tambayana ko kwalayen meye ina mata bayani .
Banso akaiwa lantana ba a lokacin kada ta dauka don gatsen da tayine yasa aka kawo mata din kuma in ba akaidi ba inna tace sai tace ai daga bayane aka sayo aka kawo muna.
Kwalayen madara ne na tea sai milor da sauran tarkacen kayan tea da katon din lemoka na sha masu tsada wani abinma sai baya mun bude muka ga meke cikin don har da kaji da ke dankare da kankara ga buhun shimkafa har uku ajiye.
Kamar ba gobe har ina mamakin hali iri na innan mu kamar ba yanzu lantana ta gama mata cim mutunci ba don haka aka diban mata komai aka kai mata Asabe hakan aka kai mata komai da mukazo dashi.
Mamakon injin tace a dawowa inna da kayan sai naji tana fadin wallahi karba zanyi ko yanzu don ba a barin mugu da makami ai.
Ba a san zafin nema ba tunda ba jikin mutum aka kurza ba wanda yaje shi aka sani kuma sunan shi ya lalace ai.
Kowan mu a dakin yaji me take fadi saidai da idanu kawai innan mu ta kallesu kowa ya shiga natsuwa a cikin dakin da alama dai warining inna ta bayar gaba daya a dakin .
Allah sarki wallahi yahanasu ko yau na fadi na mutu a gidan nan kin biyani don bani da kaico gurin haihuwan ki don yar ki zata iya rungumar ku a yanzu ta zame muna gata.
Gorin da aka zugani nasha maki na rashin haihuwan dana mijin yau ga diya macen ta jawo muna arzikin da za,a fade mu a gari muma.
Aiko Asabe bata rufe baki ba saiga lantana na fadin kai Allah