Showing 114001 words to 117000 words out of 191310 words
Chapter 39 - ABU CIKIN DUHU BY MAKAWA By abooks.com.ng.txt
ba zan haifi da da cikina in zauna dashi ba tare da yaji magana ta ba duk ko abinda yazama.
Nabi iyami a sannu ne inga iya gudun ta gareni saida har yanzu shedan yayi shimfida a zuciyar ta ita bata bi magana ta ba ta yaya yayan ta take son subi nata don wani manufa nata can na daban.
Idan anyi magana ta farawa mutane kame kame akan zancen ta mata ita ba haka muka dorata ba ina mahaifin yaran nan da halin shi ta aure shi lokacin shima ba matsiyaci ta sameshi ba ba a cin arziki taci ita a rayuwanta.
Hjy ce ke fadan wanan maganan a cikin bacin rai ban yarda na tsuka mata ba sai faman tunanen da nake a cikin raina a lokacin.
Mikewa tayi don yin sallah walha haka ya ban daman gyara kayana kamar yadda ta umurce ni inyi har ta idan a daidai lokacin dana gama komai duk da yar jakar kayan da aka ban bai isheni hada yan tsumakarana ba don yanzu Alhamdullahi ina da yan waddatatun kayan da Aisha dashi jafar din suka waddatar dani dasu.
Falo ta tursasa min da mu fito ko jikin nawa zai kara ake min a kwance nake na dunkule saman kujera a daidai lokacin da mukaji takon tafiyan mutum yana shigowa falon mami din.
Ban dago kaina don ganin kowaye ba a lokacin ina kwance a yadda nake.
Muryanta ne ya sheda min da Nuriya ce matar ya mamud tana gaida hjy dake zaune saman kujera ban dago don gaishe ta ba don kowa na gidan ina kallon shi a makiyina.
Idan ka debe mazan gidan gaba dayan su da suke nuna min iya kulawan su idan sun shigo.
Tsiyata da dan kauye gadara ke me kika taka da bazaki gaida mutane ba dadin abin dai dan halin bera ke ga mutum bai gani ya kauda idon sa saiya dauka.
To ai sai ya gani yake dauka ko wani ko ai ko bai gani ba dauka yakeyi don abin yanzu ba sai dan kauye ba don har wanda baka zata ba sai kaji ya yaudari mutane mutanen ma mijin shi na sunna don kawai ya tara ya kaiwa tsofin sa gida.
Hjy kina nufin dani kike wanan zancen au kema da wani ke zancen ke nan ke kalleni da kyau banyi maki kama da tsofin banza ba da zaki kawo wa diban albarka ba.
Kin taba aje abu a gidan nan ta daukar maki ko wani naki ko dan gidan abinsa ya taba bata toyo dama shi ya kawo ki shiyan nan takalan magana ko me ?
Girman mahaukaci karamin mai wayau sai ya fishi ke abinda kikeyi a gidan nan ai ko kare baya ja .
Mayafi kayan dake jikin ta ta cire ta mayar a kafadan ta taja wani uban tsuki tare da fadin hjy tsohuwa ba mamaki dai kema an gama dake gun malam na kauye yanzu.
Idan bashi ba yanzu dai magana ta nake a wurin nan ba tare da ambatar sunan kowa ba shine har kike kokarin bata min suna haka ?
Bari shi mamud di ya dawo da uwarsa Inji wanda ya fada maki haka a cikin su don ba zan taba lamuntan wanan zancen ya tafi a banza ba gidan nan.
Allah dai ya dawo dasu din lafiya hjy tace tana nuna bajin tsoro a cikin zancen ta ko kadan tafito mata hjy zainabu Abun tana asali.
Wanan abin ya kara saukar min da hawayen bakin ciki masu dumi da kunan zuciya a lokaci guda sai me kuma ?
Ba hjy sai ta juyo gareni a zafafe ta hauni da fada a cikin takaici tana fadin ke yar da wanan bakin kukan naki dayaki ci yaki cinyewa gareki.
Wa yan nan ba mutuncine dasu ba zai ruwan jikin ki ya kare a banza basu san kina yi ba maza ki gyagije ki shiga tsabganki hankali kwance kamar Allah ya aiko ki.
Shi ai sheri ga dan wani takine babba ga wanda yayi shi ni dai nasan harga Allah ba shedun zurba baki daukan masu kwandala a gidan nan ba in har sun yayada wanan zancen haka suyiwa kansu sheri don min sai ya tambaye su.
Hjy nikan na yafe masu kada Allah ya jarabi kowa a cikin su da wanan abinda nake ji a yanzu don akwai zafi da ciwo a zuciya.
Kaji ya mai hankali nima bawai ina nufin hakan ya samesu bane ai ina dai fadin yadda abin yake ne don idan sheri ko hairan ka kuddurata wa dan uwan ka sai kwantankwancin hakan ya sameka kaima.
Kiran sallah azahar ya tayar damu a gurin sallah muka idar a daidai lokacin da lami ta shigo dauke da kayan abincin hjy dakin na gaida ita da aiki.
Take fadin yar hjy ance yau bakiji dadin jikin naki ba Allah ya karo sauki na amsa da amin kawai don yanayina babu dadi cikin sa ko kadan a lokacin.
Fitar lami dakin yayi daidai da shigowan shi da sallama a dakin kamar daga sama muka ganshi ya fado dakin a wanan lokacin.
Jafari ka dawone ashe yau zaka dawo garin hjy dake zaune saman sallaya tana jan tasbaha ta fada a cikin fara, a da kulawa.
Eh mun dawo hjy mun sameku lafiya ya gida ya tsufa da jinya ya fada fuskan shi a kaina na dukar da kaina gabana na faduwa tunda yayi sallama dakin kamar an aiko min da mutuwa nakeji.
Ya jikin naki ya fada a lokacin daya karaso yana zama a kujera kusa da inda nake zaune daga ni sai ni don na nade hijjabin danayi sallah.
Dagani sai dogon rigan dake jikina a lokacin sai duk na tsargu da kaina don ban so ya sameni hakan ba a daki.
Sannu da dawowa ya na fada can ciki ciki ya kara fadin ya jikin kunje asibitin hjy ya fada yana kallon hjy din don son jin abinda zata fada.
Asibiti ai sai yan gata ita ina taga gatan da iyami zata kaita asibiti yanzu tunda kajawa yar bakin jini ga kowa a gidan nan wai ace wanan zancen yakai har ga kunnen matar mamuda a gidan nan.
Zata zo ta nemi karawa mutane zafi akai ina fama da uwarku sai gata dazun gabanin azahar din nan wai tazo yiwa yar fade tayiwa uwarku sata a gabana don yarinyar nan bata data ido a gabana fa jafari don iyami ta mayar da yarinyar nan sabban gida yanzu.
Murmushin takaici kawai ya sake a fuskan shi tare da mikewa tsaye lokaci guda yana fadin zan shiga ciki hjy in watsa ruwa.
Naso hjy ta barshi ys fice a lokacin amma sai gashi tana ta janshi da fira daga tsayen da yake yana amsa mata da eh ko a, a da kuma Allah sarki.
Har ya samu ya fita bansan lokacin dana sauke wani irin gwarou nufashi da har ya fito fili ba a lokacin.
Ki daina tsoron shi kwana nawa ne kun zama daya yar nan ki duba saboda ke ya bar abinda yakeyi ya dawo garin nan yanzu bana ko tantama donke ya dawo a wanan lokaci.
Hjy don ni kuma na fada a cikin yar murya da mutum zai dauka a shagwabe nake magana na tace.
Don ke mana yar nan ya kamata ki fara nuna mashi yadda ake nuna mai yadda yake nuna maki kulawa haka nan.
Munci abincin na kwashe kaya don mayarwa kitchen din a can su kande suka tsareni da tambayan meya hada hjy tsohuwa da matar mamud dazun ?
Ke fadin ina barci ban san meya hadasu ba mama bata da kunya bata data ido sam wanan yar kowa sai kokarin takashi take a gidan nan haka take muna sai bayan mun karasa hada mata abinci tasa a dawo muna dashi wai baiyi ba.
Nidai ban tofa ba na bar kitchen din ina jin daci da kunci a tare dani dakin na dawo na kwanta a gefen hjy don jinta nake kamar kakata data haifeni da kanta.
A dakin shi bayan ya fito daga wanka yayi sallah har la,asar yakai zaune a inda yake bai daga daga kasan ba sai murzan kai da goshin shi da yake yana ji yanayin da yake wani iri.
Baison yayi komai a lokacin don yana jiran dawowan mami ne a lokacin yasan zasu hau sama da ita a yadda ta hasala dashi din a waya.
Don kawai yace ta yi set din yarinyar free shi bai dauka hakan ai lefi bane a gurin shi tunda ya biya abinda mami ke tunanen ta kashe wa yarinyar.
Waya ya karba hakan ne ya dauke mai hankali don suna neman shi kan wani ma,aikata da za a gina suna bukatan shi ya tsara masu wasu na,urori a cikin tsarin ginan wanda saishi ne yasan yadda abin zaiyi daidai yadda suke son shi a ginan don bayanin da yakewa sauran ma,aikatar su basu gamsu dashi ba.
Wanan dalilin yasa shi dole ya koma a bakin aikin shi sai dai zaiso kafin ya koma maganan shi da yarinyar nan ya tsaya kada ya bar baya da kura idan ya tafi.
Anyi magariba duk bai fito ba mami kuma tasan ya dawo yana gidan bata nemeshi yadda ta saba ba idan yai hakan.
Ba wai baison fitowa bane gurinta saidai abinda zai faru a tsakanin sune nai shirya mai ba alokacin.
Mami da ta gama fusata da lanarin da hjy ta bata tsakanin ta da Nuriya yasa ranta baci don abinda tayiwa mahaifiyar nata din don bata kaunar abinda zai taba mutuncin hjyn balle ta bangaren ta.
Sallama yayi kofan mami ya shiga dakin kai tsaye tana zaune a bakin gado a cikin rigar bacin ta sai farin tabarau da zai kare mata haske a idon ta na karatu ta duban wani takarda a hannunnta.
Ba tare data dago ta kalleshi ba ta amsa mai sallama a ciki ciki tana mai cigaba da kallon takardan.
Gefen ta yakai zaune yana fadi a dan shagwabe mami iam tearyed ubana ka dawo ta fada ya riko hannun ta yana fadin kasan nan akwai matsala mami.
Bazan iya abinda suke son nayi masu ba don ba zasu iya fitar da kudi ayi aikin kwarai ba mami nasan ba zaka iya dasu ba dama kada dai suga sun gaiyace ka baka amsa su bane kawai.
Duk maganan da take bata dago ido ta kalleshi ba taci gaba da fadin dana san haka zai faru da zuwan ka garin nan da ban bari ka tafi ba.
Dasun baffan ku ya kara kirana kan zancen ka har yana ikirarin ya baka wata daya ka fitar d mata a cikin yan uwan ka daga Rufaida Nazifa da su Rubby.
What mami me zanyi da yaran nan godforbid mami wanan meye a cikin su banda zalla rashin kunya a tare dasu.
Wa yaja kansa da har ya samu kafan wanan maganan dama ai na dade da sani nufin su kanka ko su jalal niko yarana ba wanda zanwa aure a gida .
Mami ku fitar dani a wanan zancen don wanan shirme na dauke shi gareni na riga dana fada maku matata don haka yanzu ku nake saurare.
Zaka fadi haka jafar tunda ka sayeta a hannuna kake gani kana da kudin da kai zaka ban ni maryam har zaka turowa kudi jafar ?
No mami ba haka nake nufi ba don Allah ina son tayi facing din studies din ta a yanzu ne idan haka ya bata maki rai kiyi hakkuri mami ki nemi wata.
Bazan nema ba ta fada tana juyowa gareshi kaje gaka ga yarinyar nan sai dai kasan inda zaka kaita yanzu kuma baida ma matsala hakan mami ya fada tare da mikewa ya bar dakin.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
🦅ABU CIKIN DUHU SIRI NE🦅
3️⃣4️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
Bayan kwana biyu da dawowan shi garin na girshesu dakin mu na fito daga kitchen na nufo dakin da sauri na in fadawa hjy aiken da tayi min wurin kande a kitchen.
Da sauri na koma baya na kasa shiga dakin a cikin tsoro da fargaba don Nuriya dana samu a dakin tana kuka wiwi a tsakiyan su.
Kitchen na koma cikin fargaba tare da tunanen ko akan akainane ko kan waye sukayi wanan haduwan haka.
Na dade a kitchen din kafin in koma dakin bayan fitan su daga dakin wurin hjy duk dako sun dan dade a dakin suna tataunawa a lokacin.
Hjy tana zaune ita kade a dakin bayan dul sun watse daga dakin tana zaune da kullin abu a farar leda tana kallo.
Na shigo take fadin kina kitchen wurin kande ne nace eh na shigo dakin nasame ku a ciki na koma .
Muna nan da mara kunyar sarakuwar gidan nan yau tajimu a gidan nan don jarumina yai mata tas a dakin nan a gaban kowa ya tashi taka ta saida uwarku taja mashi burki.
Wanan dan maganan da tayi ne ya sani tunane tare da jin tsanar da nake mai a wautana gani shine ya jawo min duk wani tsagwama da akemin yanzun a gidan mami.
Sai naji ya dan ragu a raina don yadda hjy tayi min bayani sai naji tausayin shi ya dan tsirga min a zuciya tunda duk a kaina shima yake samun wanan matsalan da kowa haka a gidan yanzu.
Ban kai ga gama tunane ba sai ga yaran Nuriya din sun shigo da littafi a hannun su sun zo nayi masu assignment din su.
Kwasan su nayi muka koma waje kada mu damu hjy a dakin can lambun gidan muka je muka zauna na fara koya masu sosai nakan ji dadin zama da yaran don sukan sakani a cikin nishadi sosai idan muna tare da su.
Hakan ne ya kasance a wanan lokacin da muke tare da yaran a lambo na shagala sosai ga dariyan yarinyar dake shirin kuka don kawai bata gane me nake tambayan ta ba.
Daga can bangare daya ba tare da sanin mu ba ya jafar ne da zaman daki ya isheshi ya fito don ya sha iska a wajen.
Daga inda muke zaune yake kallon mu don mun masifan burgeshi da dauke mai hankalin don ya kula da abinda ke faruwa a wurin.
Ga yaran duk gaba daya suna zaune ne a saman jikina a hakan nake koyar dasu sai in basu takardan su kwashe akarshe.
Yakai minti biyar a gurin tsaye hankalin shi a garemu yana tunane shi kadai a wurin yana kallon mu ko kyafta idanuwan shi baiyi.
Ganin yarinyar ta tubure da kuka a lokaci guda yasa shi saki zafaffan ajiyan zuciya ya fara takowa zuwa inda muke.
Baiso ya karaso inda muken ba amma sai ya tsunci kanshi da takowa zuwa garemu din gadan gadan zuciyar shi na cike da jin tausayin yar dan uwan shi dayaga tana kuka akan karatu.
Kamar daga sama na tsinkayi muryan ya jafar yana fadin meya sa kuka sakata kuka haka zainab ?
A dan firgice na waigo baya ta inda nake jin muryan shi din yana tsaye ya zura hanayen shi a cikin aljihun wandon shi gami da zubo min idanuwan shi akaina yana son jin amsan da zan bashi.
Ganin yadda na dan dirance da ganin shi a wurin a bazata yasa shi fadin kuyi hakkuri don min naga kamar har yanzu bata gane me kike nufi bane.
Malaman kuma kina ganina kin firgice da ganina yanzu yana fadin hakan ya duka ya dauki yarinyar ya dora a cinyar shi tare da kaiwa zaune a dayan kujeran dake gefen mu, muna fuskantar juna dashi.
Da sauri na janye kaina gefe daya tare da kurawa kasan wurin ido ina jin yadda yake lalashi yarinyar dake jikin nasa.
Ina zaune a cikin tsarguwa sai kace wata gunki a wurin ko kwakwaran motsi ban yarda na karayi ba wurin tunda ya zauna din.
Da kyar ya iya budan bakin shi tare da dago kai yana kallona yace kiyi hakkuri ki kara fahintar da ita yadda zata gane me kike nufi da wanan lissafi din.
Bai tsaya yaji abinda zan fada ba ya jawo kujeran tare da dan matsowa kadan a inda nake zaune.
Na cira kai da sauri na dubeshi babu wasa a fuskan shi don shima ni yake kallo a lokacin.
Tsoro da mamakin shi yadda ya zauna a gurin kuma yake son in koyar da yarinyar tasu ya kamani sai naji ya sake fadin yi mata bayani yadda zata fahinta a yanzu man.
A firgice nace nayi mata tace bata gane bane yaya kiyi mata yanzu zata gane din insha Allahu.
Ba yadda zanyi dashi haka na fara nunawa yarinyar yadda zata gane takuma fahinci abinda nake nufi a cijin lissafin tiryan tiryan nake mata bayanin komai ba tare da na dago kai na dubi inda yake zaune rike